← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 65

Sashe 56

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ameer yayi caraf yace mommy kullin ,, tana dauko photonki sai take kuka tana kallon photon ,, tace ke sister dinmu ce

Murmishi tayi tace eh kunga,, gani nadawo nice sister dinku ,, takwara bakiyin magana ta kalli ameera

Turo baki ameera tayi ,,tace anty meyasa ,, Ameer yayi magana ni banyi yake ta magana ,,, murmishi ameera tayi tace , haba yar kanwata ai yanzu tare zamuje yawo dake ,,, fuskanta tasaki tace da gaske anty "" Ameera tace sosai makuwa

Ikram tace baby , cikin jikin ki ,, ko zubewa yayi " ??

Yar dariya ameera tayi tace gasucen mai sunanki ,, da mai sunan daddy na

Da sauri ikram tace , ina take mai sunan nawa " doctor aisha tace gata nan bacci takeyi tana mikawa " Ikram ,,yarinyar , amsa tayi tana Allah sarki yaran albarka ,, Muhammed , ya karaso wansu shima ikram ta hadasu ta rungume , sosai

Su jamila ne suka shigo da gidan da cikin ta da kyer take jan kafa ,, Ameera na ganinsu ta mike tana fadin anty jamila , itama , jamila dariya take hade da kuka tana fadin kanwata kece ashe zan sake ganinki , a rayuwa ta ,, kamata ameera tayi takaita kan kujera taimaka mata , tayi suka zauna " Jamila ta rungume ameera tana fadin Alhamdulillah " ashedai kina raye kanwata munyi kukan rashinki ,, a tare damu , yanzu gashi kindawo garemu Alhamdulillah

Murmishi ameera tayi tace ,, kina gani anty jamila , ga yaranki nan tana nuna mata muhammed da ikram

Sosai jamila tayi murna ganin yaran nan tayita rungume su ikram ko dama bacci takeyi

Hira sukeyi sosai ,, yaudai wannan family kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki sosai hakan ,, ya nuna a fuskokinsu dama zuciyoyinsu ,, bayan sallar azuhar , aka gama girki daddy yakai ,, mazan sashen baki matan kuma suna zauna a falo " aka fara cin abinci bayan angama cin abinci ,, doctor aisha tace zasu tafi gidan sister dinta

Mommy tace ta tsaya su zauna anan amma tace a a zasu dawo gobe in ana son ganin ikram ,zata kawota

Ikram tace naso abani takwara amma tinda ke kika dauka duk dayane

Doctor aisha tace Allah Allah yasaka da alkhairi wllh harna fara fargabar ,, zaku kwacemin ,Ikram yarinya tashiga rena sosai shiyasa tin acen nace abani ita

Murmishi mommy tayi tace , ai bakomai da nakowa ne indai ikram karama ce munbaki ita har abada

Sosai doctor aisha taji dadi harda hawayen ta na jin dadin amvata ikram dama batada mace muhammed ,, shi kadaine danta , shiyasa ta kwallafa rai akan ikram , Sallama suka musu sukatafi ,

Daddy na murna yace bari na kira yaya Ahmed da Abubakar ,, na fada musu dawowar daughter ,,nan ya yadanna kiran abba ,, tana ringing daya yadauka " da sallama ,, amsawa yayi suka gaisa kafin ,yake sheda mishi ameera ta dawo kuma da alhalin inna da baffa

Abba yace kai nuhammed nasan dai bakamin irin wannan wasan,, da gaske ne

Daddy yace wllh yaya da gaske yaba ameera wayar

Jin muryar ameera yayi yace abbana nice gani Allah yadawo dani gida,, Abba kace kaga sister din inna da anty karima mai kama dani

Abba sujjadar godiya ga Allah yayi tana tasbihi ga Allah ,, dake jin komai itama hamdala tayi ,, sosai suka shiga farin ciki , abba yace gasunan gobe insha Allah

Yana kashewa ya fadawa abbu sosai gidan yacika da farin cikin dawowar ameera kowa ya matsu gobe tayi dan yaje yaga ameera ,, Khadija ko baa magana kusan kwana tayi a zaune

Washe gari sun karfe 2: pm na rana sukazo kowa so yake yaga ameera har turayya suke , ita kuwa ameera sai dariya takeyi, bayan sun gama ganinta ta nufi wannan umma da yaya safiyan

Ameera tace umma na abbana , tana kukan ganin su ...

[30/10, 19:20] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA 🌟*

*STORY AND WRITER BY:*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

*81—82*

Ameera tayo inda , umma take da sauri tashige jikin umma tana kuka " Umma dinma hawaye takeyi sosai , tace yar inna kindawo garemu Alhamdulillah

Ameera tace umma nadawo dama kaddarar rayuwar dangina ce akaina ,, shiyasa nabar gareku , Umma ga dangin su inna ce da baffa

Dagoda ita tayi tace , to gaske kinga dangin inna

Murmishi tayi tace , eh umma kuje ku gaisa dasu mama da mama , anty karima , yaya umar , da nazeer da kaka usman , muje kigansu

Ciki suka karaso , nan ta zauna , suka gaisa sosai kafin ameera ta gabatar mata da su karima

Sosai umma ke kallon karima " tace lalle jini daya ba wasa bane wannan kama haka yanzu dai , acikin wannan family ku ukun ,, nan kunfi kama ameer da ameera da karima , ga yaranku ma duk masu kama daku

Dariya karima tayi tace , haka ne umma iri baya karya gaskiya ne wannan nan sukaci gaba da hira

Nafeesa ce tashigo gidan tana fadin besty na ina kike shin da gaske ne kindawo

Da sauri ameera ta mike tana nufar nafeesa tace oyoyo besty me welcome back , besty gani nice nadawo ,, rungume juna sukayi , sosai nafeesa ke kuka

Tace besty na ina kike duk wannan tsayin lokacin ,, gaskiya naji dadin dawowar ki garemu

Bubuga bayanta ameera take alamar hararrashi ,, tace kiyi hakuri haka ya isa haka , muzauna kinji

Zama sukayi nafeesa tace , besty ina cikin da kika tafi dashi ko , yazube ne lokacin da kikayi accident

Murmishi tayi tace gasu cen ta nuna mata muhammed

Nafeesa taje ta daukoshi ta rungume ,shi kuwa sai kallon ta yake yana shafa fuskar ta yace mommy ,,, murmishi nafeesa tace na'am my son

Su khadija sai yanzu suka karaso , ita da rashida ,, rashin gurine a motar yasa aka barsu agida saida aka kawo su umma ,, tukun aka koma aka daukosu

Da sallama suka shigo cikin falon

Khadija na baza ido taga inda ameera zata fito ji tayi an rungume ta tabaya

Juyowa tayi wa zata gani, Ameera da sauri ta rungume ameera tace waiyo Allah kawata ,, kece ashe da rabon zamu sake ganin juna

Murmishi ameera tayi tace ,, wllh kuwa gani aminiya ta ,,yasu baba ya mutanen kauye

Khadija na dariya tace suna nan lfy wllh yabayan rabuwa aminiya ta

Lfy lau ameera tace nan suka zauna

Muhammed ne yashigo da sallama dauke da ikram karama ,, tayi luf abinta

Murmishi ameera tayi tace , baban momsy na barka da zuwa

Harara ya aika mata yace kefa na lura , kin maidani kakan ki ko ,, ai yanzu ni yayan ikram ne yar mommy , kanwata ce

Dariya ikram tayi tace , tab wayagama yaya to ai shikenan

Muhammed yace,, dama mommy tace na kawo kanwata , akwai wanda zasu ganta

Inna tace muhammadu kai ne agidan , namu ina maman taka , bazata zoba da zauna ita kadai,

Zama muhammed yayi awajan inna yace eh tace hutawa " zatayi zatazo gobe kila

Flow inna ta wurgawa ,, Muhammed tace dan kan uba " makaryaci yo to inba karya ba yaushe tacema goben ma kila ne " a ina tama wannan magana sangangamin " banza kaima ina ganinka ,, yan kirki ashe kaidin dan uwan ameeru ne to kafita idona

Dariya suka yan falon sukayi ,, Muhammed ,, yace kai inna to mainayi " kike min baa haka ,, da nace dake zanyi maleji nayi wuff dake to ,, tinda naga alama fada gareki ,, bazan aureki na hakuri dama budurwa nake nema kinga sainaje na , aureta

Ameer ne yafito gaishesu yayi , san nan ya dawo wajan muhammed ,, suka yi musabaha

Kallon ikram yayi datayi luf abinta ko mutsin kirki batayi , tayi shuru ,,murmishi yayi yace babyn kaka ,, bako magana ma , taho mugaisa

Kallon ikram tayi , saida tagama mishi kallon tass tukun ta sauko kamar zataje wajanshi " sai ta kalli muhammed tace ,, daddy wannan tana nuna ameer

Dariya Muhammed yayi yace shima daddy kinefa kije ,bak'e kafada , tayi alamar bazata jeba muhammed yace haba ,ke kuwa yar mommy kije

Murmishi ameer yayi yace,, harta manta ni ne lalle yarinyar nan ,Mika hannu ,, yayi zai dauketa

Ita kuwa ikram ,, ganin zai taba ta da sauri ta shige jikin muhammed tasa kuka tace daddy wannan ,, ta nuna ameer da hannu

Dariya sukayi mommy tace tab ,,kaji yarinya yar nema wai uban nakinne wannan

Muhammed yace ,,ai mommy ta manta shine , shiyasa ma take kinsa

Ameer ya kalli ,, Inna yace hajiya inna mai duniya ,, yadai naga sai wani cika kike kina batsewa ,

Muhammed yace wai dan nace nadena auren ta ne fa shine take fushi

Hannu ta daura a kanta tasaka kuka ,,tana fadin innalillahi wa inna ilaihin raju'un

Da sauri su maman karima tayo wajan ta , tace yaya maryame lfy

Ameer ya kalli maman anty karima yace babu wani abu rigimar tace ta motsa ba wani abu bane yafaru

Inna tace ,, kai ameeru uwarka kakewa wannan futsarar,, dan iska marar mutumci ,, dama nasan aiba kaunata kakeyi ba babu ruwana dakai dan banza kawai

Dariya sukayi mata ,,Ameer yace Allah yabaki hakuri inna mu ,, keda zamu baki ikon diya idan wife ta haifo wasu

Inna ta washe baki tace a to shikenan yanzu nadena fushi dakai

Yauma haka suaksha hira abbu ne bai zoba yayi tafiya zuwa abuja inna tace bazata basu labarin ba indai har abbu bai zoba dan , kar ayi babu shi ,, hakura sukayi sai abbu yadawo din ,,suji story din inna da baffa

Bayan sallar isha"i ,su Muhammed suka shigo gidan , ikram na ganin muhammed ta nufesa ,, tana kuka fadi take daddy wannan ,,, da sauri yakarasa yace kai yar mommy waye yatabamin ,, ke har yasakaki kuka
Chapter 56 · 0% Book details