← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 65

Sashe 34

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ganinta sukayi, kamar mai bacci mom ce takaraso,, kusan gadon ta zauna bude idonta ikram tayi tana kallon su kuka ikram tasa tana fadin mom, dan Allah kice mafarki nake kutasheni daga wannan , kaddararren bacci mom tace kiyi hakuri ikram anbada cigiyar ta insha Allah zaa sameta haka ta ringa kuka tana surutai, akan anemo mata babyn ta su mom har mamaki sukeyi saboda, yadda ikram tashaku,, da ameera

Haka wannan family suka shiga,, tsananin damuwa,,, kullin ana haska photon ameera a gidan talabijin amma babu wanda yace yaga mai kama da ameera hakan na kara karya musu zuciya

Su umma dasuka samu wannan bakin labarin babu abinda umma keyi sai kuka tana kuma kai ga Allah daya tsare mata ameera duk inda take Allah yasa tafada hannu nagari kullin haka take kwana batayi baccin dare ba tana nafila tana kuka

Haka su mommy kullin cikin addu'ar Allah yabayyana ameera kafin lokacin da ameer zai farka

Fatima bata iya baccin kirki duk tabi ta rame sosai sai kuka kullin take musamman ma idan, ta kalli sashen su ameer saita kara shiga damuwa

Ikram kam baa magana ,, dan shayarwa ma gagarar ta tayi saboda,, rashin kuzari duk inda take zaune photon ameera ne take kallo tana kuka saboda har ga Allah tana son ,, ameera tana kaunar ta kamar jinin ta

Acen kuwa yau ne aka tashi su ameera ,, gida suka tafi tin kafin suje,, gidan yacika da dangi sosai suna isa,, gidan maman anty karima ,, tayo wajansu,,, tana kuka tace jenifer na ashe da gaske joshow yake baki mutu ba muke karya ta shi,, zata rungume ameera da sauri ameera ta boye a bayan mama tace mamana ,, murmishi mama tayi tace maman jenifer kidata mu zauna tukun ,, ayi bayani dakatawar maman anty karima tayi suka karasa suka zauna kowa so yake jenifer tamishi magana

Ita kuwa ameera tana rike da hannun mama ta rike gam kamar zaa rabasu zama sukayi,, kowa yazauna,, sai kallon ameera suke suna hawaye wasu na dariya

Mama tace maman jenifer yanzu jenifer bata gane kowa saboda ta manta duk rayuwar ta na baya saboda buguwar da kanta yayi,, shiyasa ta manta komai yanzu bata san kowa ba sai nida joshow dan haka a hankali zata ganeku

Numfashi maman anty karima taja tace to shikenan maman joshow balbu yabata lfy kowa na wajan haka yake cewa

Joshow ne ya kawo yaran wajan ameera ta daura mata macen akan cinyarta namijin kuma yazauna gefen ta

Joshow yace jenifer wannan baby mu ne kinganta ta girma kinga ga marus nan shima ya girma

Kallon yaran tayi tana dubasu kamar wani abu ya tabasu sai ta kalli mama murmishi mama tayi mata tace this is my daughter and son jenifer rungume baby tayi ta janyo marus shima ta hada dashi,, tana jin sonsu a ranta

Mama tace jenifer daga kai, Ameera tayi tana kallon mama tace kinga wannan itace mamanki ni kinga son dina ta nuna mata joshow ajiye baby tayi gefe ta matsa kunsan maman anty karima ta kwanta ajikin maman anty karima tace mama na sai maman anty karima ,, ta rungume ta tana kuka tace,, daughter ina sonki munshiga,, halin damuwa " da baki tare damu,, kallon ta ameera tayi dan batasan mai kalmar take nufi ba

Yaune, Ameer yacika sati biyu yau kuma zai tashi,, su mom sai safa da marwa sukeyi dan kowa halin da ameer zaishiga suke yi,, suna haka wata nosee tace kuzo ya farka dukkansu suka yi dakin,, turus sukayi ganin......

*to ko wani hali ameer zai kasance idan aka cemishi an rasa ameera yazaiji wannan amsar saiku biyo maman nusy domin jin yadda zai kasance*

Ina godiya da comments din ku da addu'o'i ku agareni Allah yabar mu tare nidaku
[28/10, 00:24] MRS. MU'UTASIM: *🌟MAEER DA AMEERA 🌟*

*RUBUTAWA DA TSARAWA*.

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

💫💫
*JARUMAI WRITERS ASSOCIATION 📚🖊️*

*MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA 💪*

*53—54*

A bakin kofa suka tsaya, ganin ameer yasauko daga kan gadon ya zauna a kasa

Da sauri bilal yakaraso inda yake zaunen dagoshi bilal yayi yace sannu ya jikin yanzu ina ke maka ciwo

Dagowa ameer yayi yana kallon su sai kuma ya kalli su mom yaga suna hawaye dukkansu yace mom manene kuke ina ameera ta take kukaini inda aka kaita

Mom takaraso ta kama hannun shi takaishi bakin gadon tasoma kallon shi cike da tausayi

Ameer yace wai ina tambayar ku ina ameera take inason , ganinta,,

Anass ne yakalli mom yace mom mufada mishi gaskiya rashin fada mishi gaskiya matsala ne

Jinjina kai mom tayi tace son kayi hakuri kasan ko, wani bawa ' da irin tashi kaddarar ku taku haka tazo muku inason ka kara imani da Allah yakara imani da kaddara mai kyau ko,, akasin ' haka ameera ta bata tin lokacin kukayi accident annemeta ba'a ganta,, ba nan ta fada mishi komai

A razane ya mike yana cakumo wiyan bilal yace no no bana son jin wannan,, maganar impossible ma tace,, ameera bata wannan wajan Bilal ina ameera ta kuje kunemo min ameera ta

Rikeshi bilal yayi yace am so sorry my friend gaskiya muka fada maka ba karya ba ameera ta bata yanzu haka ko ina munbada cigiyar ta har garuruwan nakeza gayen duk munbada ,, pictures dinta kayi hakuri insha Allah zata fito

Ko karshen maganar baiji ba yasaki bilal yafadi akasa a sume, da sauri bilal yayo kanshi,, shida anass

Fatima ce ta bude sautin kuka tana fadin waiyo Allah yaya nashiga uku dan Allah Allah yaya karka mutu kabar mu kada, kaima " katafi kabarmu " muna sonka yaya idan ka mutu nima binka zanyi please ,, yaya dan Allah katashi kaji tana maganar tana kuka sosai har rawar sanyi jikinta ,, keyi saboda tashin hankali

Anass ne yayo baya yakoma wajan Fatima, hannun ta yakama jin anass ne yasa ta shige jikin sa tana kara kankame shi,, rarrashin ta yake yana shafa kanta da dubara yake busa mata iska a kanne ,, duk dan tayi shuru ko tayi bacci dan yaga bacci a idon dan jiya kasa bacci tayi saboda ance mata yau ameer zai tashi,, bata jimaba yaji tana sauke numfashi a hankali kallon fuskar ta " yaga tayi tace bacci saiya rungume ta yazauna yana tausayawa abokin nashi sosai

Mom tace bilal bani ruwan sanyi mai kyau nan bilal yakawo mata,, addu'o'i sosai mom tayi kafin tashafa mishi a fuska baiyi motsi ba rabin ruwan ta " juye mishi a fuska ajiyar zuciya yasauke yana bude" idonshi,, kallon su yake sai kuma yatashi ya jingina da jikin mom ya daura kanshi a kafadar mom

Mom tace sha wannan ba muso,, ya bude baki tabashi ya shanye tas sai numfashi yake fiddawa mai zafi yana juya kanshi wanda ke masa ciwo kamar Zai tsage

Ameer yace ya Allah ka bayyana min ameera ta ya rabbi kasa tana hannu nagari suka ce mishi ameen

Yace bakusan abinda nakeji ba ameera batada lfy ga cikin jikinta,, wanda yake hanata sukoni bata iya cin abinci sai da lallami nake bata,, kullin kuka takeyi tana cewa,, na amshi cikin itama tahuta haka nake rarrashin ta sbd yarinya ce,, bata " san komai ba ko bacci bata iya yi na kirki sai ajikina shima ina mata addu'a a haka take bacci to yanzu wazai mata haka,, " wazai bata kulawa,,, yadda yadace gashi baa san inda take tana kai karshen maganar yana fashe da kuka mai ban tausayi

Mom tace kayi hakuri son insha Allah zaa sameta kaji son

Suna a haka kabeer yashigo,, yabasu sallama nan suka shiga mota sai gida

Shi kuwa ameer duk ya rasa ina zai saka kanshi yaji dadi saboda tashin hankalin dayake ciki

Zaune take tana game a waya,, da gudu yashigo falon,, yana fadin mommy! Mommy! Mommy ki boyeni kada kibari,, yadake ni

Dagowa ameera tayi tana kallon dan nata,, murmishi tayi tana bude mishi hannu ,, da sauri yashiga jikin ameera yana haki da alama dai yaci gudu

Ameera tace my boy waye zai dakeka kake wannan ,, gudu haka kaji kirjinka kuwa kadena irin wannan kaji boy

Dagowa yayi yace mommy,, dukana zaiyi ameera tace,, wanene nuna mata shi yayi inda yake nunawa take kallon wani yaro ne daidai marus zaiyi sa'anin juna dashi

Kallon shi ameera tayi tace zo da sauri yaron ya karasa yana goge hawayen fuskar shi

Ameera tace meya hadaku kuke fada kudena kunji kufa abokai kaji kada kubari wani yahadaku fada, gyada kai sukayi tace to ku shirya nan marus yatashi daga jikin ameera yazo gun abokin nashi suna rungume juna,, suna dariya murmishi tayi tace to kuje waje wasa nan suka fita

Suna tafiya ameera tana binsu murmishi tana jin son yaron nata har kasan zuciyar ta

Shikuwa joshow sai kallon ameera yake yana jin dadi saboda yadda take kula da yaransu , yace my jenifer ina sonki

Ita kuwa batama san yanayi ba,, game dinta takeso bude kofa taji anyi kallon wajan tayi murmishi tayi ganin yar ta ce ta tashi daga bacci

Yarinyar tana ganin ameera saita gwabe fuska kamar zatayi, kuka tace mommy, yar dariya ameera tayi " ganin yadda takeyi ameera tace ,, na'am beauty kintashi to zo nan

Karasawa yarinyar tayi ganin ameera ta dauki wayar ta soma game dinta ai kawai saita saki kuka , da sauri ta ajiye waya " tana janyota jikin ta tace menene kuma beauty

Kallon ta tayi tace mom, yunwa ameera tace to muje nabaki,, nan sukayi dinning ta zuba mata abincin tana bata abaki she surutu take mata da hausar ta wadda bata isheta ba

Duk abin sukeyi joshow na kallon su soyake yaje ya rungume jenifer amma bayason bata rai dan mama tace kada ya taba ta tinda bata haiyacinta

A kauye kuwa su umma suna nan sunyin jimami ba kamar,, Khadija ma duk ta rame sosai bata iya cin abinci tin lokacin da aka ce musu ameera ta bata
Chapter 34 · 0% Book details