← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 65

Sashe 51

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fiddo da fatima akayi,, tana kallon su da murmishi aka kaita wani daki daban,, Ameer yafito yace zasu sati daya anan kafin abasu sallama , nan suka amsa da to

Muhammed ne ,, yazo gidansu ameera yabuga nan aka bude mishi , su ameera yagani dukkansu " suna cikin shiri

Umar yake dama kai muke jira muje , nan suka tafi su uku ,a gefen titi suka faka motar , suka nufi majami'ar,, suna ambaton sunan Allah ....

*Nima nasoma ambaton sunan Allah " ina binsu abaya duk maison zuwa tazo muje*
[30/10, 17:54] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA 🌟*

*STORY AND WRITER BY:*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

Follow me my WhatsApp group:https://chat.whatsapp.com/KMuyxRBLx5iI93EEYIGlVX

*Wannan fage na sadaukar gareku addana ,, ummu amsad , and ummu shukhura, kudade kuyi karko kamar dabino 💃🏻💃🏻*

*75—76*

A hankali suke tafiya, saboda duhun wajan , ko takalmin su ahannu suka rike , haka suke tafiya , kamar barayi d'akuna uku suka , gani umar yace , yanzu mubi dakuna dakuna " dan mugano awani dakine

Muhammed yace ok mufara da wannan na kusan mu , nan suka shiga ciki " haskawa sukayi nan sukaga , masu gadin dakunan gidan bautar ne suke bacci hadda, munshari ,

Umar yace kar wanda yayi magana ko motsi dayawa,

Wucesu sukayi nan suka shiga dayan dakin , kowanne dauke da addu'a abakinsa

Suna shiga suka haska ihu ameera zatayi saboda ganin kwarangwal din jikin mutane , da alama dai wani abu aka yi da naman jikinsu da sauri umar ya rufe mata baki , yace , haba mana ihu kuma kizama jaruma mana " karki sake kokarin yin ihu , gyada kanta tayi alamar to ,

Gaba sukayi haka suka ringa bin dakunan amma basuga ,, komai ba haka suka hakura zasu tafi "

Harsun juya ameera ta haska wani bangare , nan taga kamar kofa ce na gidan kasa , da sauri tace yaya umar kuzo kuga

Dawowa sukayi ta nuna musu,

Muhammed yace mu bude mugani

Nan suka fara kiciniyar budewa , amma sun kasa saboda nauyin kofar

Iamar ance umar ya kalli gefensa nan yaga wani dan karfe , da sauri ya mika hannun shi yadauko bakinsa dauke da addu'a

Yace muhammed wannan kamar shine bakullin , inda mu gwada mugani kozai bude,

Muhammed yace inda kawo mugani nan suka saka karfen , aikuwa yabude

Cike da murna ameera tace to mushiga , Muhammed yace umar zai shiga tsaka ke abayanshi " ni abayanki kar aje ki sa mana ihu ,

Turo baki ameera tayi , tace ai dai banida tsoro , yace to naji muje nan suka shiga da hasken , wayarsu suke ganin hanya har suka shiga ciki

Babu komai a ciki feline kawai ko ina suke kallon saboda , wajan akwai hasken wata wuta a cikin wani kasko , shiyasa basu ganin duhu ,

Sun dade basuga komai ba suka kari dubawarsu basuga koda wani alama acikin felin ba,

Wata abu ameera ta hango kamar akwati kamar frij , tace yaya kalli cen

Kallon inda take nuna musu sukayi, da umar da , Muhammed suka karasa , wajan

Muhammed yace wa umar yabude suga meye aciki nan ya soma budewa amma kyerma dayake , yasa yakasa

Amsa muhammed yayi yabude, zaro ido yayi ganin mace aciki , saboda sanyin akwatin ta sandare , da kankara , ahankali yace umar leko kagani

Da sauri yaleka , da sauri yake cewa it...it..ita...itace , karima ce maza mu fiddo ta

Ameera ta matso jin abinda, Umar yake nan ta leka dafe kirji tayi ganin anty karima , fadi take,, anty karima

Muhammed yace , dasu babu lokaci maza mutafi musamu " mufita daga wannan wajan nan , suka fito daga gidan kasar

Ahankali yanzu ma suke tafiya har sukabar majami'ar , nan suka yi wajan motarsu " aka saka karima abaya , umar ya zaune kusanta

Muhammed da ameera agaba nan sukayi gidan su muhammed

Yanzu fatima tana samun sauki sosai , ga baby girl din masha Allah , lafiyayya da ita " Inna kuwa koda yaushe tana rungume ' da baby din ta hana kowa dauka , komai ita kewa babyn ,,

Ameer ne da hajara sukazo hospital din suka shiga cikin dakin, da fatima ke ciki da sallama suka shiga ciki , Inna ce ta amsa musu ,,Fatima na kan gado tana cin wuton dawa da miyar kubewa,, yasha man shanu sai kamshi yakeyi

Hajara tayi wajan inna take kawo babyn mugani inna

Harara ta aikawa hajara tace , to ke taya ma kika iya rike jariri abaki kije ki , targada musu yarinya

Bata fuskar hajara tayi tace kai inna hadda cin fuska a alamar na yau , kuma kike cewa ban iya rike jariri ba kokin manta ni nayi renon, Ibrahim shine, kikemin gori

Inna tace bazan bayar badai " koma meye futsararriya,, kawai kitashi kiban waje kona make ki,

Ameer yace haba inna kibata " mana tagani tasa mata albarka

Inna tace kai kuyi tafiyar ku wajan aikinku " karku damemu dan banza, to ance baza'a bataba

Hajara kamar zatayi kuka tace please yaya kace , tabani naganta , Ameer yace zo nan kyaleta idan anty ikram tazo saiki ganta tashi mutafi , office ,mikewa tayi tana kunbura baki nan suka fita

Tinda su muhammed suka dauko karima, mommy sa yakira tana bacci ,, dauka tayi ganin danta ne yasa ta tashi da sauri

Tace hello , son lfy kake kirana sa asubar nan

Muhammed yace mommy kitashi , zamuzo nida umar da ameera , kice abude mana kofa

Mommy tace to to saikun zo , tana ajiye wayar fita tayi tana " cewa mai gadinsu ,idan anyi Hon ya bude kofa,, ya amsa mata da to nan takoma gida

Doctor aisha mamaki take, to kodai wani abu yafaru da safiyar nan muhammed yake gidan su ameera , bata gama tunanin ba taji shigowarsu

Da sauri tasa hijab ta fita tana tsaye har suka fito

Baya suka bude nan suka fito da karima da mamaki take kallon su

Wajan ta sukayo ameera tace please momma ba lokaci muje ki duba mana ita

Bunsu tayi ciki kamar rakumi da akala , a falo suka shimfide ta ,

Ruwa yasoma diga daga jikin alamar kankarar tasoma narkewa , Muhammed ya kalle ta yace mommy ki dubata mugani tana da rai

Kayan aikin ta ta dauko tashiga auna karima tajima tana aunawa , kafin ta dago tace tana da rai zuciyar ta na mugawa ,,amma tana mugatar " karin numfashi saboda nata yamata kadan , kuma dole sai an ringa gasa mata jikinta da ruwa mai zafi sosai saboda kankarar jikinta, ta fita kozata samu damar motsawa da kanta

Muhammed yace to ,mommy muje hospital din , karmuyi jinkiri , kayanta ta hada , umar yadauki karima nan suka shiga mota sai hospital din mommy

Suna karasawa , doctor aisha tashiga office dinta,, ta saka kayan aiki tukun tafito ,, nosee nabinta abaya

Karin numfashi aka sakawa karima shima da kyer aka samu aka saka mata saboda duk ilahirin jikinta yayi tauri ,

Umar ko yama rasa mai zaiyi shida , ameera ,, kuka ameera tayi rusa kamar ance karima ta rasu ,, Umar na bata baki akan tayi shuru amma kamar kara mata karfin kukan yake,, haka ya hakura yazuba mata ido

Cen kuma saiya kira mama , ringing daya ta dauka , dama tana kokarin kiransa ne saigashi ya kirata dan taleka dakinsa sai, Abubakar tagani na ameera kuma sai muhammed , yana bacci nida mufeeda

Mama tace hello umar wai ina kuka tafine na leka banga ameera ba kaima banganka , ba sai yara suna bacci

Ajiyar zuciya yasauke yace mama ki kira , maman karima dukkanku , kuzo hospital din doctor aisha , idan kukazo zakuji komai

Cike da tashin hankali ,Mama tace na shiga uku hallau wani abunne yasamu ameera din

Umar yace no ba ita bace kudaizo nan ya kashe wayar yana kallon ameera da har yanzu take kuka abinta

Ameera ko kukan farin ciki ne takeyi, saboda tacikawa karima burinta gashi kuma sun fiddo ta daga cikin inda aka boyeta ,, shiyasa take kukan farin ciki saboda ,, takusa komawa wajan mijinta da danginta , duk wani nauyin da zuciyar ta kemata kullin yau tana kukan , yana fita , tana haka su mama sukazo

Doctor Aisha ce tafito kallon muhammed tayi tace son , kaje gida ka wanki ikram saikuzo idan kunyi break , , ya amsa da to nan yatafi baima ,, tsaya sun gaisa da su mama ba , ta tafi

Doctor aisha tace, zaku iya ganin ta kafin asoma shirye shiyen mata aikin nan da sati biyu ,

Ameera na ganin mama da sauri ta fada jikin ta tana kuka ,, Mama tace wai lfy kike kuma shi kuma sai murmishi yake " ku fada mana

Dagowa ameera tayi tace mama mun samo anty karima ,

Kallon mama tayi da sauri tace ke ameera bana son wasa " kinsan me mike cewa kuwa

Cikin kuka ameera tace , eh mama kuzo muje kugani , nan suka nufi dakin da aka kai karima,

Cike da mamaki suke kallon karima da take kamar gawa a kwance , maman ta ta karasa wajan da take tana kallon ta tace tabbas wannan karima ce " wannan kayan dashi ajikinta , akace ta mutu kowa

Umar ne yamusu bayanin komai da dakota da abinda doctor aisha tafada

Mama tace Alhamdulillah Allah mungode maka ,sai ta kalli ameera wanda take share hawaye , tace lalle ameera ke haske ce agaremu,, alkairan ki yana dayawa " agaremu Allah yasaka miki da alkhairi yadda kikayi sanadiyar, fitar damu daga duhu Allah yarabaki da duhun kabari, Allah yamiki albarka

Ameera tace ameen mama , nima ai yarki ce , yanzu dai mubari , muga tashin antyna

Nazeer ma kukan yake share hawayen sa yayi yana murmishi ,, yace kaji masu anty to sannu ko

Harara ameera ta banka mishi tace ,eh anji din tuzuru kawai
Chapter 51 · 0% Book details