Sashe 7
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kafin ya kammala an kirayi isha'i,sake miqewa yayi ya fice zuwa masallaci,don sam baya wasa da sallar cikin jam'i,koda aka idar nan majalisar dake kusa da gidanshi yadan xauna aka taba hira,bai jima can da yawa yayi sallama dasu,kasancewar yana da masaniyar gobe yana da lacture ta qarfe tara,kuma dama bai fiya zama cikinsu ba ba dabi'arsa bace wannan,hakan yasanya wasu kejin haushinsa tare da yi masa kallon mai girman kai,yakan zauna lokaci zuwa lokaci saboda kauda wannan zargin daga ransu,bugu da qari ya sani dole kuwa ya fita tun bakwai,don kuwa da qafarshi yake takawa har zuwa makarantar,zuwanshi mota a abun hawa abune mai matuqar sa'a,imma wani aikin qarfin ya samu yayi ya samu kudi,ko idan anty usaina ta d'anyi samuwa ta kirashi ta bashi wani abun,ko Allah ya hadashi da d'aya daga cikin 'yan makarantarsu ya rage masa hanya.
Allah ya taimakeshi yau cikinsu ba wanda ya shigo masa gida,saboda haka ya kulle ko ina yayi nafilfilunsa kamar yadda ya saba,ya roqawa iyayensa da 'yan uwanshi gafara sannan ya kwanta bayan ya sake kunna rediyon yana sauraren shirye shiryen da sukeyi.
Sannu a hankali tunaninta ya kutso cikin kaiwa da kawowar da qwaqwalwarsa keyi tun dazu,ya dan saki murmushi yana wassafo kamanninta,yanayinta tsarinta da tafiyarta,da ganinta zatayi hankali,da ganinta akwai nutsuwa tattare da ita,da ganinta ba maison hayaniya bace
"Duk taya akayi kasan hakan?" Ya tambayi kansa da kansa,saiya sakarwa kansa murmushi yana girgixa kai gami da runtse idanunsa,shima baisan ya akayi ya tsinci kansa da fadawa wannan bigiren ba,saiya juya zuwa daya barin yana son maoda hankalinsa kan programe din da ake gudanarwa a gidan redio a sannan.
Tun bayan sallar magariba ummantata keta sintirin aiken qannen nata kan ta fito taci abinci,saidai sam ta qiya,tayi kwanciyarta abinta,ranta ne kawai ke mata suya,a duk sanda irin wannan balahirar ta faru a gidansu idan da safe ne wuni take cikin qunci da damuwa,hakanan idan da yammaci ne koda dare kwana take cikin qunci shima da damuwa,wani lokacin takance inama kurma Allah ya halicceta?,inama makauniya ce ita ta huta da ganin wannan baqon lamari,wanda ya zama tambarin gidansu,ya kuma zama abinda jama'ar unguwa ke goranta musu dashi,don babu wanda baisan irin rayuwar da ake tsakanin uammansu da babansu ba,tayi kuka har sau babu adadi,tabi hanyoyin gyara bila adadin amma babu alamun ma sauyi bare akai ga gyaran gaba daya,tayi tunani iri daban daban masu kyau da marasa kyau amma bata samu hanya mai bullewa ba,tayi yaji tabar gidan batasan adadin sau nawa ba amma sun bita sun dawo da ita kan alqawarin komai ya wuce zasu gyara amma babu alamun sauyawar lamuran,ta tambayesu me yasa suke hakan amma su kansu basu san amsa ba,abu d'aya ta sani shine,dukkaninsu tsakanin ummanta da babanta babu wani mai haquri acikinsu,ummanta bata da haquri ko kad'an kamar yadda mahaifinta yake,bata raga masa ko daya,idan ya mata taga bai mata dai dai ba take zata rama,shi kuma yaga ta rainashi kenan haka zai biye mata suyita yi.
Basu san ciwon da hakan ke mata a qirjinta ba,basu san illar dahakan ke haifarwa ga tarbiyya yara da tunaninsu da ginuwar hankalinsu,iyayenka a wannan bigiren na fada da juna kulli yaumin har sauran jama'a su shaida hakan kai me yayi saura a rayuwarka?.
Saida umman taga da gaske take bazataci abincin ba kamar yadda ta saba a duk sanda ta samesu suna cecekuceb da suka saba,saita dire faruqu ta nufi dakin nata,ta yaye labulen tana tsaye daga dokin qofa tace
"Tunda sai abinda kikaga dama zakiyi bismillah,dadin abun cikinki ne ba nawa ba,yunwa kuwa dai dai take dake matsalarki ce wannan,ki tashi ki gayamin ya akayi sauran botikaina sabbi suka fashe haka?" Da qyar ta juya daga kwancen da take ta d'aga kai ta dubeta
"Wasune garin wawaso suka fasa su"
"Botikan duka?" Kai ta gyada mata
"K'nnnn,ai shikenan,Allah ya kyauta" ta fada tana sakin labulen,maida kanta tayi ta kwantar,inama ace haka takewa mahaifinsu a duk sanda wani abu ya hadosu?,ta tabbatar da shine tsautsayi irin haka ya faru da yau Allah ne kadai yasan qarshen fadansu.
Mubina ce ta shigo da kwananon abincin ta dire mata ta juya ta fice,bata dai kallesu ba tana ci gaba da kwanciyar
"Idan baki tashi kin kama abinci kinci ba na shigo sai nayi mugun saba miki" ta jiyo muryar umman daga tsakar gida tana gaya mata,hakanan badon son ranta ba ta sauko ta tanqwashe qafa ta dinga cusa abincin har sai dataji kaman zatayi amai sannan ta maida murfin ta rufe ta sake kwanciya.
Runtse idanunta tayi tana fatar bacci ya dauketa,sai taga wata fuska data sanyata saurin sake bude idanunta,dawo mata yayi tar a kwanyarta,bacin ran da take ciki yasa bata sake tunowa dashi ba sai yanzu,saita gyara kwanciyarta tana kallon bango,ta dinga tuno fuskarsa da yadda tafiyarsu ta kasance daga bakin masallaci har zuwa gida,hakanan taji nauyi da bacin ran zuciyarta ya ragu sosai,ta shagala da tunanin daya d'auketa zuwa bacci mai nauyi.
Qarfe biyu na rana gaba ya tsinci kansa hankalinsa ya tafi bakin masallaci gurin da ba wajen zuwansa bane idan ba shagin balarabe zashi ba ko wani babban uzurin ya kamashi na zuwa wajen,sai ya sake tsintar kansa da sake yin wanka bayan ya gama hutawa duk da kusan dabi'arsa ce a duk sanda ya dawo daga makaranta,amma wannan karon saiya laluba kayanshi har ya zaro zai saka ya maida ya sauya wasu,abinda bai taba yi ba,bai taba damuwa da suturar da zai saka,kawai dai yasan dukka kayan sawarshi a tsaftace suke kullum,hakanan basa rabo da guga,duk da cewa ba wasu masu shegen kyau da tsada bane,Allah dai yayi masa wata baiwa ta duk kayan daya saka jikinsa na dauka,hakan yasa matasan anguwar da dama ya tsone musu ido,wanda yawancinsu dukka sunfishi gata rufin asiri da komai da komai,tsaftarsa tasa baka gane kaashinsa.
"Ki kulamin da botikai na,karki sake bari su fasamim botiki,kai jamilu idan ka aje mata ka dawo ka kaimin shara" cewar ummanta wadda take rufe botikin abincin data gama zubawa almajirin ya qaraso wajen ya dora a kanshi suka fice tanawa umman sallama.
Har sunje soron gidan hakanan taja ta tsaya,saita juya da hanzari ta koma ciki
"A'ah,lafiyarki kuwa?" Umman tata da taga wucewarta ciki ta fada
"Lafiya umma ina zuwa" kai tsaye ta dauko dan kwandon kayan kwalliyarta dake saman akwatin kayanta,ta ciro ruwan madubi mai fadi dake soke a ciki ta kalli fuskarta
"Hoda na miki kyau wallahi shahida,don Allah ki dinga d'an shafawa mana" ta tuna maganar da qawarta ta gaya mata daxu a makarantar boko,saita samu kanta da ciro hodar ta bude ta shafa,data sake kallon fuskarta sai taga ta canza din kuwa,sosai hodar tayi mata kyau ta sake fidda kyau da qyallin fuskarta,murmushi ta saki ta aje mudubin ta juya ta fice da sauri.
Yana zaune daga shagon balarabe yana kallon duk wani motsinta dake bayyanar da hankali da nutsuwarta da kuma ainihin ita wace,duk surutu da hirar da balaraben yake masa baya gane abinda yake fada sam,shi kuma bai fahimta ba bare yaja bakinsa yayi shuru ya barshi.
Haka ta dinga raba abincin kamar yadda ta saba,saidai tanata dube duben kadan kadan da batasan meye dalili ba,harta kammala tsaf ta hada kwanukanta waje daya,haka kawai saitaji ranta ya baci lokacin data gama shirin komawa gida,duqawa tayi don daukar botikan taga an sako hannu an dauka,da hanzari ta dago don ganin waye?,ta tsammaci ma su ahmadi ne ma basu gargadin da aka musu jiya ba yau suka dawo,saidai ga mamakinta saurayin jiya ne,gaba yayi abinsa sai tabi bayansa sukaci gaba da tafiya ba tare da kowa yace da d'an uwansa wani sbu ba.
Basuyi wani nisa ba ya janye ta koma ita ce a gaba shi yana baya,bata kawo komai a ranta ba ta tsammaci bazai gane gidan nasu ba shi yasa yayi hakan,kamar tafiyar jiya har suka je inda ya dakata a jiya ya aje mata botikin,saidai yau din ta daga ido ta kalleshi,akaci sa'a shima ya kalleta a sannan,wani irin zallar kyau da kwarjini idanunta suka gani,sai taji wani abu tun daga qwaqwalwarta har tafin qafarta,mazewa tayi gami da d'auke kai tana jin izzarta ta diya mace na motsawa,a nashi bangaren ma wani abu mai qarfi yaji yana janshi game da ita tamkar maganadisu da mayen qarfe,sai bakinsa yayi nauyi,bai furta mata komai ba ya juya ya soma takawa don barin wajen,daga manyan idanunta tayi tana bin bayanshi da kallo har sai daya bacewa ganinta,batasan me yasa ba bakuma tasan sanda ta saki murmushi ba ta daukin botikin nata ta fada gida.
Allah ya taimakeshi yau cikinsu ba wanda ya shigo masa gida,saboda haka ya kulle ko ina yayi nafilfilunsa kamar yadda ya saba,ya roqawa iyayensa da 'yan uwanshi gafara sannan ya kwanta bayan ya sake kunna rediyon yana sauraren shirye shiryen da sukeyi.
Sannu a hankali tunaninta ya kutso cikin kaiwa da kawowar da qwaqwalwarsa keyi tun dazu,ya dan saki murmushi yana wassafo kamanninta,yanayinta tsarinta da tafiyarta,da ganinta zatayi hankali,da ganinta akwai nutsuwa tattare da ita,da ganinta ba maison hayaniya bace
"Duk taya akayi kasan hakan?" Ya tambayi kansa da kansa,saiya sakarwa kansa murmushi yana girgixa kai gami da runtse idanunsa,shima baisan ya akayi ya tsinci kansa da fadawa wannan bigiren ba,saiya juya zuwa daya barin yana son maoda hankalinsa kan programe din da ake gudanarwa a gidan redio a sannan.
Tun bayan sallar magariba ummantata keta sintirin aiken qannen nata kan ta fito taci abinci,saidai sam ta qiya,tayi kwanciyarta abinta,ranta ne kawai ke mata suya,a duk sanda irin wannan balahirar ta faru a gidansu idan da safe ne wuni take cikin qunci da damuwa,hakanan idan da yammaci ne koda dare kwana take cikin qunci shima da damuwa,wani lokacin takance inama kurma Allah ya halicceta?,inama makauniya ce ita ta huta da ganin wannan baqon lamari,wanda ya zama tambarin gidansu,ya kuma zama abinda jama'ar unguwa ke goranta musu dashi,don babu wanda baisan irin rayuwar da ake tsakanin uammansu da babansu ba,tayi kuka har sau babu adadi,tabi hanyoyin gyara bila adadin amma babu alamun ma sauyi bare akai ga gyaran gaba daya,tayi tunani iri daban daban masu kyau da marasa kyau amma bata samu hanya mai bullewa ba,tayi yaji tabar gidan batasan adadin sau nawa ba amma sun bita sun dawo da ita kan alqawarin komai ya wuce zasu gyara amma babu alamun sauyawar lamuran,ta tambayesu me yasa suke hakan amma su kansu basu san amsa ba,abu d'aya ta sani shine,dukkaninsu tsakanin ummanta da babanta babu wani mai haquri acikinsu,ummanta bata da haquri ko kad'an kamar yadda mahaifinta yake,bata raga masa ko daya,idan ya mata taga bai mata dai dai ba take zata rama,shi kuma yaga ta rainashi kenan haka zai biye mata suyita yi.
Basu san ciwon da hakan ke mata a qirjinta ba,basu san illar dahakan ke haifarwa ga tarbiyya yara da tunaninsu da ginuwar hankalinsu,iyayenka a wannan bigiren na fada da juna kulli yaumin har sauran jama'a su shaida hakan kai me yayi saura a rayuwarka?.
Saida umman taga da gaske take bazataci abincin ba kamar yadda ta saba a duk sanda ta samesu suna cecekuceb da suka saba,saita dire faruqu ta nufi dakin nata,ta yaye labulen tana tsaye daga dokin qofa tace
"Tunda sai abinda kikaga dama zakiyi bismillah,dadin abun cikinki ne ba nawa ba,yunwa kuwa dai dai take dake matsalarki ce wannan,ki tashi ki gayamin ya akayi sauran botikaina sabbi suka fashe haka?" Da qyar ta juya daga kwancen da take ta d'aga kai ta dubeta
"Wasune garin wawaso suka fasa su"
"Botikan duka?" Kai ta gyada mata
"K'nnnn,ai shikenan,Allah ya kyauta" ta fada tana sakin labulen,maida kanta tayi ta kwantar,inama ace haka takewa mahaifinsu a duk sanda wani abu ya hadosu?,ta tabbatar da shine tsautsayi irin haka ya faru da yau Allah ne kadai yasan qarshen fadansu.
Mubina ce ta shigo da kwananon abincin ta dire mata ta juya ta fice,bata dai kallesu ba tana ci gaba da kwanciyar
"Idan baki tashi kin kama abinci kinci ba na shigo sai nayi mugun saba miki" ta jiyo muryar umman daga tsakar gida tana gaya mata,hakanan badon son ranta ba ta sauko ta tanqwashe qafa ta dinga cusa abincin har sai dataji kaman zatayi amai sannan ta maida murfin ta rufe ta sake kwanciya.
Runtse idanunta tayi tana fatar bacci ya dauketa,sai taga wata fuska data sanyata saurin sake bude idanunta,dawo mata yayi tar a kwanyarta,bacin ran da take ciki yasa bata sake tunowa dashi ba sai yanzu,saita gyara kwanciyarta tana kallon bango,ta dinga tuno fuskarsa da yadda tafiyarsu ta kasance daga bakin masallaci har zuwa gida,hakanan taji nauyi da bacin ran zuciyarta ya ragu sosai,ta shagala da tunanin daya d'auketa zuwa bacci mai nauyi.
Qarfe biyu na rana gaba ya tsinci kansa hankalinsa ya tafi bakin masallaci gurin da ba wajen zuwansa bane idan ba shagin balarabe zashi ba ko wani babban uzurin ya kamashi na zuwa wajen,sai ya sake tsintar kansa da sake yin wanka bayan ya gama hutawa duk da kusan dabi'arsa ce a duk sanda ya dawo daga makaranta,amma wannan karon saiya laluba kayanshi har ya zaro zai saka ya maida ya sauya wasu,abinda bai taba yi ba,bai taba damuwa da suturar da zai saka,kawai dai yasan dukka kayan sawarshi a tsaftace suke kullum,hakanan basa rabo da guga,duk da cewa ba wasu masu shegen kyau da tsada bane,Allah dai yayi masa wata baiwa ta duk kayan daya saka jikinsa na dauka,hakan yasa matasan anguwar da dama ya tsone musu ido,wanda yawancinsu dukka sunfishi gata rufin asiri da komai da komai,tsaftarsa tasa baka gane kaashinsa.
"Ki kulamin da botikai na,karki sake bari su fasamim botiki,kai jamilu idan ka aje mata ka dawo ka kaimin shara" cewar ummanta wadda take rufe botikin abincin data gama zubawa almajirin ya qaraso wajen ya dora a kanshi suka fice tanawa umman sallama.
Har sunje soron gidan hakanan taja ta tsaya,saita juya da hanzari ta koma ciki
"A'ah,lafiyarki kuwa?" Umman tata da taga wucewarta ciki ta fada
"Lafiya umma ina zuwa" kai tsaye ta dauko dan kwandon kayan kwalliyarta dake saman akwatin kayanta,ta ciro ruwan madubi mai fadi dake soke a ciki ta kalli fuskarta
"Hoda na miki kyau wallahi shahida,don Allah ki dinga d'an shafawa mana" ta tuna maganar da qawarta ta gaya mata daxu a makarantar boko,saita samu kanta da ciro hodar ta bude ta shafa,data sake kallon fuskarta sai taga ta canza din kuwa,sosai hodar tayi mata kyau ta sake fidda kyau da qyallin fuskarta,murmushi ta saki ta aje mudubin ta juya ta fice da sauri.
Yana zaune daga shagon balarabe yana kallon duk wani motsinta dake bayyanar da hankali da nutsuwarta da kuma ainihin ita wace,duk surutu da hirar da balaraben yake masa baya gane abinda yake fada sam,shi kuma bai fahimta ba bare yaja bakinsa yayi shuru ya barshi.
Haka ta dinga raba abincin kamar yadda ta saba,saidai tanata dube duben kadan kadan da batasan meye dalili ba,harta kammala tsaf ta hada kwanukanta waje daya,haka kawai saitaji ranta ya baci lokacin data gama shirin komawa gida,duqawa tayi don daukar botikan taga an sako hannu an dauka,da hanzari ta dago don ganin waye?,ta tsammaci ma su ahmadi ne ma basu gargadin da aka musu jiya ba yau suka dawo,saidai ga mamakinta saurayin jiya ne,gaba yayi abinsa sai tabi bayansa sukaci gaba da tafiya ba tare da kowa yace da d'an uwansa wani sbu ba.
Basuyi wani nisa ba ya janye ta koma ita ce a gaba shi yana baya,bata kawo komai a ranta ba ta tsammaci bazai gane gidan nasu ba shi yasa yayi hakan,kamar tafiyar jiya har suka je inda ya dakata a jiya ya aje mata botikin,saidai yau din ta daga ido ta kalleshi,akaci sa'a shima ya kalleta a sannan,wani irin zallar kyau da kwarjini idanunta suka gani,sai taji wani abu tun daga qwaqwalwarta har tafin qafarta,mazewa tayi gami da d'auke kai tana jin izzarta ta diya mace na motsawa,a nashi bangaren ma wani abu mai qarfi yaji yana janshi game da ita tamkar maganadisu da mayen qarfe,sai bakinsa yayi nauyi,bai furta mata komai ba ya juya ya soma takawa don barin wajen,daga manyan idanunta tayi tana bin bayanshi da kallo har sai daya bacewa ganinta,batasan me yasa ba bakuma tasan sanda ta saki murmushi ba ta daukin botikin nata ta fada gida.