Sashe 51
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegarima kusan fitar wuri tayi,tana tsaye a kitchen tana shan ruwan dumi anty zubaida ta taras da ita
"Ba zakiga kayan ba kenan zaki fita" agogonta ta kalla sannan ta sauke hannu
"Sauri nake anty"
"Hakan yasanya jiya nace a tasoki ki gani ai" baki ta tabe a fakaice tana tuna haushin da hasina taso tura mata ajiyan da yadda ta matsanta mata,kayan da bataga abinda anwar zai zuba a ciki da zasu burgeta ba
"Idan na dawo na gani,saina dawo anty" ta fada cikin hanzari bayan ta dauki jakarta data aje ta rataya tana ficewa da hanzari,kasa cewa komai anty zubaida tayi sai binta da kallo kawai da tayi harta fice sannan ta girgiza kanta tana tadi ita da zuciyarta,ko ba'a fada ba tasan ganin kayanne bata sonyi.
Kwana uku tana cewa anty zubaidan zata gani amma bata yarda taje inda sukebama bare ta gani,dole ta gaji ta zuba mata idanu,a haka har akaci kwana goma sha biyu,ga tsammanin anty zubaida shahidan zata dauki hutu wajen aiki,saidai taga ko ajikinta bata fasa fita aikin na,sake qara mata kwana biyu tayi taga ko zata dakata da fitar,saidai ranar daya rage biki saura kwana bakwai cif da safe anty zubaida ta sameta a falo tana karyawa ta gama shiryawa tsaf,kallonta sosai take taga da gaske take fita aiki zatayi?,kallon harya sanya shahidan itama yin sak tana kallon anty zubaidan,saidata soma dan tsuke fuska sannan tace
"Ina zaki haka da safe?" Tambayar tadan baiwa shahida mamaki,ko maqota sunsan inda taje zuwa daga safiya zuwa yammaci bare anty zubaidan,don ita bata kawo tambayar tata nada alaqa da aurenta ba
"Office mana anty" ta fada cikin son gamsar da ita,kai anty zubaida ta girgiza
"Bakisan aurenki saura kwanaki bakwai ba ko lissafi ne ya qwace miki?,ko kuma duka kina sane saboda kinha na zuba miki ido ne?"wani abu ya taba zuciyar shahidan,ba zancan data tsana a yanzu irin zancan aurenta,tana sane saura kwanaki bakwai su qullashi to amma ita meye nata a ciki?,me zata zauna gida tayi
" to anty,ni menene nawa a ciki?,me zan zauna nayi a gida?"
"Eh babu komai naki a ciki tunda zubaida ce zatayi aure,so kike duniya ta zagemu ko?,tunda kike kin taba ganin amarya budurwar da aka aurar salin alin?,to banason sakarci,babu ruwana da wani abu daya taba gittawa tsakaninki da anwar ni aikina zanyi kawai,rawata zan taka,saboda haka ki koma ciki daga yau zansa abban huda ya dauka miki excuse,su baki hutun sati uku" kaman ta zunduma ihu haka taji sanda anty zubaida ke maganar,abinda ta dauka wasa ne gashi yana neman tabbata,ba damar musu da ita saboda yadda ta tsare gida sosai,haka shahidan ta soma takawa don komawa dakinta
"Eheennn...jimana" anty zubaida ta sake fada,saita tsaya gami da waiwayowa tana dubanta,sai data kallo agogo sannan tace da ita
"Qarfe sha daya na rana zamu fita dake,ki zauna cikin shirin" kai ta gyada kamar kazar da qwai ya fashewa cikin cikinta,haka ta dinga tafiya harta isa daki,ta watsar da duka kayanta kanta na daukar zafi,me yasa anwar yake son ya soma da nasara da sa'a a kanta?,me yasa anwar ya dawo cikin rayuwarta bayan bata da buqatarsa?,haka ta dinga yiwa kanta tambaya ranta na zafi.
Sha dayan da 'yan mintina suka fita ita da anty zubaidan kawai,bata tambayeta ina zasuje ba har saida suka isa gidan sannan ta fahimci wajen gyaran jiki ta kawota,tamkar wata doluwa haka ta dinga bin anty zubaida da kallo har suka gama gaisawa da matar da gabatar da shahida wajen matar a matsayin amaryar da za'a yiwa bikin
"Kai tubarkalla masha Allah,wannan badon hausawa suna cewa idan kana da kyau ka qara da wanka ba ai bata buqatar komai,saida nasan gyaran ba qaramin hawanta zaiba zubaida" tana jinsu harta gama surutunta ta soma hada kayayyakin gyaran jikin ta buqaci shahida ta sauya wani zani na daban data dauko.mata,fuska ta bata tana duban anty zubaida ranta na baci ta wani gefan,yanzu saboda anwar ne aka kawota nan wajen
"Anty,don Allah abar abunnan,batamin kaya kawai zaiyi" dago idonta tayi daga wayarta da take dannawa ta watsawa shahidan harara,hakanan tana ji tana gani ta sauya zanin aka shiga mata gyaran,bakinta gum tana bin matar da kallo kaman ta mangareta saboda yadda takebin fatarta da kayyakin tana shafeta dasu.
Tana ganin kawai bata lokaci da bata kudi ne.
A qalla sun kusa kashe awa biyu cur ana abu daya,bin jikin nata take da kallo yadda ya soma wani santsi sulbi da sheqi na musamman,tabe bakinta tayi data tuna saboda me akayi mata,sai taji gyaran sam bai burgeta ba,tana maida kayanta wani qamshi na tashi daga jikinta duk sanda ta motsa,turarukan qarshe da aka murje mata jikinta dasu.
Basu jima ba suka isa gida,a falonta zauna cikinsu huda wadanda ke kallo,faruq ya kalleta
"Anty harkin fara canzawa,kaman bakeba akan dazun da kuka fita'binsa tayi da ido kawai ba tare datace komai ba,kafin ta gama tunanin da take ta jiyo muryar huda
"anty...zamuyi kewarki,tafiya zakiyi yanzu ki barmu?"ta qarasa fada a shagwabe kaman zata saki kuka,nan take ran shahida yaso ya sake baci da tuna hakan da tayu,anty zubaida ce ta katse komai tana tambatar faruq me suka dafa musu,yace white rice ne bazai iya miya ba,hararsa tayi
"Daga kai har haidar din a rasa wanda zaiyi miya?" Huda na gefa na musu dariya,kai ya langabar
"Allah ummi shi yasa nace ki samo mai aiki fa" tsaki taja sai shahida ta miqe
"Bari na hada" tafurta tana yin gaba zuwa kitchen.
Kayan miya ta diba ta soma gyarawa sannan tayi blending,dukka rabin hankalinta da nutsuwarta nakan tunani,data hada miyar saita zauna cikin kitchen din tana duban agogo,tasan zuwa sanda zata gama hudu tayi saita da alwala kawai gaba daya.
Miyar na soyuwa haidar ya shigo yana shaida mata tazo inji anty zubaida,saita rage wutar can qasa yadda ba zata kama ba kafin ta dawo ta fito zuwa falon,a zaune ta sameta da tulin kaya a gaba da alama sabbabi dinkuna ne tana dagawa tana kalla gami da ware wasu gefe
"Kije waje kinyi baqo"gabanta yadan fadi,tadan bata fuska
" waye haka da la'asar din na"
"Ban sani ba nima,idan kinje zaki gani" hakan yadan kwantar mata da hankali jin ba wanda ta tsani ganin bane,nan kan kujera ta dauki mayafinta data dawo dazu dashi ta yafa sannan ta fice.
Matashin saurayine mai kyau da aji tsaye jikin motarsa,sanye yake da shadda riga da wando dinkin tazarce,hankalinsa duka nakan wayarshi a haka ta kusa cimmasa,bata sanshi ba amma sai take ganin tasan fuskar a wani waje daban ko can da dadewa,sallama ta masa ganin baisan da isowarta ba,ya daga kai da hanzari yana amsawa fuskarsa ta fadada da fara'a
"Barkanki da yamma kin wuni lpy"
"Lafiya alhmdlh" ta amsashi a taqaice
"Ya mutanen gidan kowa da kowa lafiya?"
"Lafiya qalau" ta sake amsawa tana mamaki ina ya santa tare da zurfafa tunaninta ko zata iya tuna a inda ta sanshi,murmushi ya saki
"Nasan baki sanni ba,ni sunana muhsin,aboki kuma aminin anwar" lokaci daya maganar ta sauka a zuciyarta,sai yanayin fuskarta ya soma sauyawa,fuskarta ta soma tsukewa,duk da haka tadan dake hadi da qoqarin sassautawa,shima dubanta yake yana karantar sauyawar yanayinta lokaci kadan,bai sake cewa komai ba ya bude murfin motar da yake jingine a jiki ya zura hannu ya ciro wata babbar envalope da qarama ya miqa mata,kallon envalope din tayi sannan ta dawo da kallonta kanshi alamun neman ba'asi
"Katin gayyata ne na dinner ko zaki gayyaci qawayenki,wannan kuma kudine ko zaki buqaci wani abu" kai ta girgiza tana danja baya,a fuska tana ganin mutuncinsa amma baya ga haka so take taci masa mutunci ne shida wanda ya aikoshin,amma duk da haka ba zata kasa bashi saqo ba
"Ka maida masa dukkan kayansa,ka gaya masa aurensa baya buqatar wani shiri tunda a shiryensa aka qulla shi,kudi kuwa baiyi kudin bani ba a yanzu har zuwa nan gaba,ka gaida na gode" daga haka ta juya zuwa cikin gidan tana takawa a nutse,da kallo ya bita qwaqwalwarsa cunkushe da tunani da mamaki,kullum kwanan duniya sake mamaki yake kan meye haka mai girma daya raba kwanunansu ya tarwatsasu haka zuwa pieces suka kasa kuma daidaita tsahon shekarun?,amsar daya kasa samunta kenan haryau daga wajen anwar duk da sanda rabuwar ta afku shine mutum na farko daya sha wuya da anwar din kafin rayuwarshi ta daidaita,saiya xagaya ya bude murfin motar tasa ya shiga yana tuna yadda sukayi da anwar sanda zai ya shirya kudin da katin yace zai kaimata da sunanshi,har kusan haurawa sukayi kan koda zaikai din yakai amma bada sunanshi ba.
Iska ya furzar daga bakinsa lokacin da muhsin ke zaune kan daya daga cikin kujerun office din yana sake tambayarsa wanne laifi ya aikatawa shahida haka?,ya dubi envalope din daya fita dasu ya dawo dasu kamar yadda suke,hakan na nufin bata karba ba kenan
"Bata karbi kayan daka kai din ba kenan?" Anwar ya tambayi muhsin kai tsaye yana dubanshi,kai ya kada
"Ni duk ba wannan na tambayeka ba,inason gyara wannan barakar ne shi yafi damuna,banason alaqar taci gaba da tafiya a haka"
"Me ta gaya maka sanda kaje?" Ya sake jeho masa tambaya ba tare daya damu da nashi bayanan ba
"Batace komai ba" murmushin yaqe ya saki,takowa yayi kusa dashi kujerar dake fuskantarsa ya zauna
"Ta fadi maganganu a kaina,takuma ce ba zata karba bata buqata right?" Idanunsa cikin na muhsin ya fada,kauda idonsa muhsin yayi saboda shi kansa wasu lokutan anwar na masa kwarjini da yawa
"Kaga malam nidai bance maka haka ba,banason tone tone" miqewa yayi yana jijjiga kai
"Ta fada,na santa kamar yunwar cikina" gaban envalope din ya qarasa,ya farke dayar ya cire kudaden ciki ya janyo locker din office din nasa ya zubasu ciki,sannan ya janyo daya locker ya ciro wasu ya musanyasu dasu ya maidata ya manne muhsin na kallonsa,ya kwashesu duka ya aje masa key saman teburinsa
"Idan ka gama ka rufe ko ina" daga haka ya juya yana takawa sannu sannu zai fice daga office din
"Wait mana malam,ina zaka je?" Murmushi ya jefa masa ya fita ba tare daya amsashi ba.
"Ba zakiga kayan ba kenan zaki fita" agogonta ta kalla sannan ta sauke hannu
"Sauri nake anty"
"Hakan yasanya jiya nace a tasoki ki gani ai" baki ta tabe a fakaice tana tuna haushin da hasina taso tura mata ajiyan da yadda ta matsanta mata,kayan da bataga abinda anwar zai zuba a ciki da zasu burgeta ba
"Idan na dawo na gani,saina dawo anty" ta fada cikin hanzari bayan ta dauki jakarta data aje ta rataya tana ficewa da hanzari,kasa cewa komai anty zubaida tayi sai binta da kallo kawai da tayi harta fice sannan ta girgiza kanta tana tadi ita da zuciyarta,ko ba'a fada ba tasan ganin kayanne bata sonyi.
Kwana uku tana cewa anty zubaidan zata gani amma bata yarda taje inda sukebama bare ta gani,dole ta gaji ta zuba mata idanu,a haka har akaci kwana goma sha biyu,ga tsammanin anty zubaida shahidan zata dauki hutu wajen aiki,saidai taga ko ajikinta bata fasa fita aikin na,sake qara mata kwana biyu tayi taga ko zata dakata da fitar,saidai ranar daya rage biki saura kwana bakwai cif da safe anty zubaida ta sameta a falo tana karyawa ta gama shiryawa tsaf,kallonta sosai take taga da gaske take fita aiki zatayi?,kallon harya sanya shahidan itama yin sak tana kallon anty zubaidan,saidata soma dan tsuke fuska sannan tace
"Ina zaki haka da safe?" Tambayar tadan baiwa shahida mamaki,ko maqota sunsan inda taje zuwa daga safiya zuwa yammaci bare anty zubaidan,don ita bata kawo tambayar tata nada alaqa da aurenta ba
"Office mana anty" ta fada cikin son gamsar da ita,kai anty zubaida ta girgiza
"Bakisan aurenki saura kwanaki bakwai ba ko lissafi ne ya qwace miki?,ko kuma duka kina sane saboda kinha na zuba miki ido ne?"wani abu ya taba zuciyar shahidan,ba zancan data tsana a yanzu irin zancan aurenta,tana sane saura kwanaki bakwai su qullashi to amma ita meye nata a ciki?,me zata zauna gida tayi
" to anty,ni menene nawa a ciki?,me zan zauna nayi a gida?"
"Eh babu komai naki a ciki tunda zubaida ce zatayi aure,so kike duniya ta zagemu ko?,tunda kike kin taba ganin amarya budurwar da aka aurar salin alin?,to banason sakarci,babu ruwana da wani abu daya taba gittawa tsakaninki da anwar ni aikina zanyi kawai,rawata zan taka,saboda haka ki koma ciki daga yau zansa abban huda ya dauka miki excuse,su baki hutun sati uku" kaman ta zunduma ihu haka taji sanda anty zubaida ke maganar,abinda ta dauka wasa ne gashi yana neman tabbata,ba damar musu da ita saboda yadda ta tsare gida sosai,haka shahidan ta soma takawa don komawa dakinta
"Eheennn...jimana" anty zubaida ta sake fada,saita tsaya gami da waiwayowa tana dubanta,sai data kallo agogo sannan tace da ita
"Qarfe sha daya na rana zamu fita dake,ki zauna cikin shirin" kai ta gyada kamar kazar da qwai ya fashewa cikin cikinta,haka ta dinga tafiya harta isa daki,ta watsar da duka kayanta kanta na daukar zafi,me yasa anwar yake son ya soma da nasara da sa'a a kanta?,me yasa anwar ya dawo cikin rayuwarta bayan bata da buqatarsa?,haka ta dinga yiwa kanta tambaya ranta na zafi.
Sha dayan da 'yan mintina suka fita ita da anty zubaidan kawai,bata tambayeta ina zasuje ba har saida suka isa gidan sannan ta fahimci wajen gyaran jiki ta kawota,tamkar wata doluwa haka ta dinga bin anty zubaida da kallo har suka gama gaisawa da matar da gabatar da shahida wajen matar a matsayin amaryar da za'a yiwa bikin
"Kai tubarkalla masha Allah,wannan badon hausawa suna cewa idan kana da kyau ka qara da wanka ba ai bata buqatar komai,saida nasan gyaran ba qaramin hawanta zaiba zubaida" tana jinsu harta gama surutunta ta soma hada kayayyakin gyaran jikin ta buqaci shahida ta sauya wani zani na daban data dauko.mata,fuska ta bata tana duban anty zubaida ranta na baci ta wani gefan,yanzu saboda anwar ne aka kawota nan wajen
"Anty,don Allah abar abunnan,batamin kaya kawai zaiyi" dago idonta tayi daga wayarta da take dannawa ta watsawa shahidan harara,hakanan tana ji tana gani ta sauya zanin aka shiga mata gyaran,bakinta gum tana bin matar da kallo kaman ta mangareta saboda yadda takebin fatarta da kayyakin tana shafeta dasu.
Tana ganin kawai bata lokaci da bata kudi ne.
A qalla sun kusa kashe awa biyu cur ana abu daya,bin jikin nata take da kallo yadda ya soma wani santsi sulbi da sheqi na musamman,tabe bakinta tayi data tuna saboda me akayi mata,sai taji gyaran sam bai burgeta ba,tana maida kayanta wani qamshi na tashi daga jikinta duk sanda ta motsa,turarukan qarshe da aka murje mata jikinta dasu.
Basu jima ba suka isa gida,a falonta zauna cikinsu huda wadanda ke kallo,faruq ya kalleta
"Anty harkin fara canzawa,kaman bakeba akan dazun da kuka fita'binsa tayi da ido kawai ba tare datace komai ba,kafin ta gama tunanin da take ta jiyo muryar huda
"anty...zamuyi kewarki,tafiya zakiyi yanzu ki barmu?"ta qarasa fada a shagwabe kaman zata saki kuka,nan take ran shahida yaso ya sake baci da tuna hakan da tayu,anty zubaida ce ta katse komai tana tambatar faruq me suka dafa musu,yace white rice ne bazai iya miya ba,hararsa tayi
"Daga kai har haidar din a rasa wanda zaiyi miya?" Huda na gefa na musu dariya,kai ya langabar
"Allah ummi shi yasa nace ki samo mai aiki fa" tsaki taja sai shahida ta miqe
"Bari na hada" tafurta tana yin gaba zuwa kitchen.
Kayan miya ta diba ta soma gyarawa sannan tayi blending,dukka rabin hankalinta da nutsuwarta nakan tunani,data hada miyar saita zauna cikin kitchen din tana duban agogo,tasan zuwa sanda zata gama hudu tayi saita da alwala kawai gaba daya.
Miyar na soyuwa haidar ya shigo yana shaida mata tazo inji anty zubaida,saita rage wutar can qasa yadda ba zata kama ba kafin ta dawo ta fito zuwa falon,a zaune ta sameta da tulin kaya a gaba da alama sabbabi dinkuna ne tana dagawa tana kalla gami da ware wasu gefe
"Kije waje kinyi baqo"gabanta yadan fadi,tadan bata fuska
" waye haka da la'asar din na"
"Ban sani ba nima,idan kinje zaki gani" hakan yadan kwantar mata da hankali jin ba wanda ta tsani ganin bane,nan kan kujera ta dauki mayafinta data dawo dazu dashi ta yafa sannan ta fice.
Matashin saurayine mai kyau da aji tsaye jikin motarsa,sanye yake da shadda riga da wando dinkin tazarce,hankalinsa duka nakan wayarshi a haka ta kusa cimmasa,bata sanshi ba amma sai take ganin tasan fuskar a wani waje daban ko can da dadewa,sallama ta masa ganin baisan da isowarta ba,ya daga kai da hanzari yana amsawa fuskarsa ta fadada da fara'a
"Barkanki da yamma kin wuni lpy"
"Lafiya alhmdlh" ta amsashi a taqaice
"Ya mutanen gidan kowa da kowa lafiya?"
"Lafiya qalau" ta sake amsawa tana mamaki ina ya santa tare da zurfafa tunaninta ko zata iya tuna a inda ta sanshi,murmushi ya saki
"Nasan baki sanni ba,ni sunana muhsin,aboki kuma aminin anwar" lokaci daya maganar ta sauka a zuciyarta,sai yanayin fuskarta ya soma sauyawa,fuskarta ta soma tsukewa,duk da haka tadan dake hadi da qoqarin sassautawa,shima dubanta yake yana karantar sauyawar yanayinta lokaci kadan,bai sake cewa komai ba ya bude murfin motar da yake jingine a jiki ya zura hannu ya ciro wata babbar envalope da qarama ya miqa mata,kallon envalope din tayi sannan ta dawo da kallonta kanshi alamun neman ba'asi
"Katin gayyata ne na dinner ko zaki gayyaci qawayenki,wannan kuma kudine ko zaki buqaci wani abu" kai ta girgiza tana danja baya,a fuska tana ganin mutuncinsa amma baya ga haka so take taci masa mutunci ne shida wanda ya aikoshin,amma duk da haka ba zata kasa bashi saqo ba
"Ka maida masa dukkan kayansa,ka gaya masa aurensa baya buqatar wani shiri tunda a shiryensa aka qulla shi,kudi kuwa baiyi kudin bani ba a yanzu har zuwa nan gaba,ka gaida na gode" daga haka ta juya zuwa cikin gidan tana takawa a nutse,da kallo ya bita qwaqwalwarsa cunkushe da tunani da mamaki,kullum kwanan duniya sake mamaki yake kan meye haka mai girma daya raba kwanunansu ya tarwatsasu haka zuwa pieces suka kasa kuma daidaita tsahon shekarun?,amsar daya kasa samunta kenan haryau daga wajen anwar duk da sanda rabuwar ta afku shine mutum na farko daya sha wuya da anwar din kafin rayuwarshi ta daidaita,saiya xagaya ya bude murfin motar tasa ya shiga yana tuna yadda sukayi da anwar sanda zai ya shirya kudin da katin yace zai kaimata da sunanshi,har kusan haurawa sukayi kan koda zaikai din yakai amma bada sunanshi ba.
Iska ya furzar daga bakinsa lokacin da muhsin ke zaune kan daya daga cikin kujerun office din yana sake tambayarsa wanne laifi ya aikatawa shahida haka?,ya dubi envalope din daya fita dasu ya dawo dasu kamar yadda suke,hakan na nufin bata karba ba kenan
"Bata karbi kayan daka kai din ba kenan?" Anwar ya tambayi muhsin kai tsaye yana dubanshi,kai ya kada
"Ni duk ba wannan na tambayeka ba,inason gyara wannan barakar ne shi yafi damuna,banason alaqar taci gaba da tafiya a haka"
"Me ta gaya maka sanda kaje?" Ya sake jeho masa tambaya ba tare daya damu da nashi bayanan ba
"Batace komai ba" murmushin yaqe ya saki,takowa yayi kusa dashi kujerar dake fuskantarsa ya zauna
"Ta fadi maganganu a kaina,takuma ce ba zata karba bata buqata right?" Idanunsa cikin na muhsin ya fada,kauda idonsa muhsin yayi saboda shi kansa wasu lokutan anwar na masa kwarjini da yawa
"Kaga malam nidai bance maka haka ba,banason tone tone" miqewa yayi yana jijjiga kai
"Ta fada,na santa kamar yunwar cikina" gaban envalope din ya qarasa,ya farke dayar ya cire kudaden ciki ya janyo locker din office din nasa ya zubasu ciki,sannan ya janyo daya locker ya ciro wasu ya musanyasu dasu ya maidata ya manne muhsin na kallonsa,ya kwashesu duka ya aje masa key saman teburinsa
"Idan ka gama ka rufe ko ina" daga haka ya juya yana takawa sannu sannu zai fice daga office din
"Wait mana malam,ina zaka je?" Murmushi ya jefa masa ya fita ba tare daya amsashi ba.