Sashe 27
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba daya jin jikinta tayi tamkar an zare dukkan wata laka data yi saura,,nutsuwa tayi qaura daga jikinta a take,idanunta cikin nashi a hankali taga yana juye mata daga anwar data sani zuwa wani mutum daban,matashin saurayi mai kyau kwarjini kamala da haiba,matashin saurayi daya jiqu da hutu da naira,matashin saurayi mai cikar zati,tsayayyen namiji wanda tambarin ilimi nutsuwa da wata qasaita ta daban ta bayyana muraran kan fuskarshi,dukkan wani abu daya gani tattare da ita shekarun baya suka soma dawowa idanunshi daya bayan daya,hotunan da idan ya tuno dasu suke hanashi bacci duk dare,ganinta cikin halin maye,jinin zubda ciki na gangarowa daga qafafunta,yaci gaba da kallonta yana takowa inda take tsaye cak,sai yaga kaman a sannan ne abinda ke jikin hotunan ke faruwa,take cikin 'yan sakannin da bai wuce ka qirgasu da yatsunta biyu zuwa hudu ba idanunsa ya sauya launi,jijiyar kanshi ta motsa ta tashi,sai daya zo dab da ita sannan yace
"Kina nufin a haka zaki baiwa yaran mutane tarbiyya?,a haka kike koyar da yaran jama'a?,na tambayeki ma me kike koya musu?,uhmmm gayamin,?,yadda zasu....." Sai kuma ya kasa qarasawa ya kaiwa iska wafta da hannunshi sannan ya dunquleshi tsam kaman zai tatse dukkan jinin dake cikin hannun nashi gaba daya,dai dai sanda shugaba kula da dukka sashen makarantar ya iso ganin shuru har yanzu bai iso ba,cikin girmamawa ya rusuna
"Sir....."
"Dakata!" Ya tsaidashi cikin tsawa
"Dama irin wadan nan malaman kuke baiwa yara su koyar?" Cikin mamaki ya dubi shahida da yake nuna masa,wadda take tsaye qam a wajen kaman an dasata idanunta kan anwar,tana jin wani fushi na ratsata amma tana ta qoqarin hana hakan tasiri
"Sir.....kodai wani akasi aka samu,amma malama shahida na daya daga cikin malaman da kaf makarantar nan babu kamarsu a kowanne sashe"
"Sauraramin" ya kuma dakatar dashi wannan karon har yana daga mishi hannu,ya maida idanunsa cikin nata
"Indai wannan ce malamar da babu kamarta tabbas bakusan abinda kuke ba,babu abinda ta iya!,bata iya komai ba!,daga yau na koreta!,na koreta cikin malaman makarantar nan.....kar qafarki ta sake tako mana makaranta,you are fired!" Dukkan wani qwarin gwiwa da taso tattarowa ya tarwatse da kalmarshi na qarshe saboda yadda sautin ya fito ya bada amsa kuwwa cikin ajin,qoqarin tattaro abinda zata fada take saidai bakinta ya gaza fidda sautin saboda karayar da zuciyarta tayi,idanunta suka hada qwalla fal suna shirin ga gangarowa,saiya sake saka idanunsa cikin nata cikin wani qwarin gwiwa da yake ji yace
"Uhmm...kina da wani abun cewa ne?....say it....say it mana!" Ya kuma fada cikin hargagi yana dan dukan qirjinsa da yatsunshi gaba daya,jakar dake kafadarta ce ta sulmiyo saboda yadda jikinta ya soma rawa,gaba daya kayan ciki suka tarwatse a wajen ciki harda kwalaben magungunan huda,a kansu idanunsa suka soma sauka,wani tashin hankali da baisan na meye ba ya rufto masa,saiya daga kai da sauri yana kallonta,sam ko daya bata da nutsuwar da zata iya tsaiwa ta tattare kayayyakinta ko ta dauki jakar,hakan yasa ta juya da sauri ta soma takawa,fatanta da burinta kawai shine tabar makarantar,tabar wajen,tabar inuwar da anwar yake tsaye a cikinta,burinta shine ta nesanta dashi kawai,ta daina ganinsa ta kuma daina jin sautinsa
"Ki dawo ki debi wannan kayan zatar naki" maimakon dawowar kamar yadda ya buqata saita qara sauri kamar wadda aka biyo,don burinta shine ficewa daga makarantar ta tserewa sautinsa,wannan sautin da ta jima da neman tsari dashi da mamallakinsa.
Titi kawai ta miqa bata ko waiwaye,bata buqatar abun hawa don ji take kaman qafafunta zasuyi mata aiki fiye da abun hawan,sauri kawai take zubawa wani irin radadi na keta zuciyarta kamar ana yankarta da reza,anwar dai anwar dai?,tabbas da tasan akwai wata rana da zasu sake haduwa kaman haka da tuni ta yiwa kanta kandagarki da ita,wannan wace irin baqar rana ce a wajenta
"Anty shahida...anty shahida" taji ana qwalla mata kira wanda sam bata tsaya ba har sai da akasha gabanta,shugaban sashe ne riqe da jakarta ya miqa mata
"Don girman Allah kiyi haquri anty shahida,ya dauki hukuncin da dukkanmu bamu isa mu sauya shi ba"
👑 *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karkiyi sharing,idan kina buqatar siya ki tuntubi wadan nan numbers din*
07067124863
*ko kuma*
09032345899
*kuyi subscribing youtube channel dina don samun damar ganin shirye shiryenmu,subscribe kyauta ne!*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos
*Alqawarin Allah*
1️⃣9️⃣
"sabon abune wannan a wajenmu,abinda bamu taba gani yayi ba tunda muke dashi,kowa ya shaidai wannan kirkin nasa....anty shahida kodai wani abu kika masa?,mutumin qwarai irin haka canzawarsa...."da sauri ta yanke masa hanzari
"Na gode malam,haka Allah ya qaddara" gaba tayi da sauri don ita kadai tasan me take ji,ita daya tasan ya take ji,baifi taku biyar ba adaidaita sahu tasha gabanta tana tambayarta ina zata je?,sai data shiga sannan ta gaya mishi inda zai kaita,duk yadda taso daure zuciyarta ta bari saita isa gida saita kasa,ta tattakura ta rushe da kuka wanda har sai da dan sahun ya waiwayo
"Hajiya...lafiya?,kiyi haquri komai yayi zafi maganinsa Allah" ita dai bata iya tanka masa ba illa kukanta data ci gaba dayi.
Komao nata ta wurgar tsakar dakinta sannnan ta zauna dirshan tana risgar kuka,tanajin kaman ranta zai fita ne,duk wata nutsuwarta a yanzu babu ita,anwar dai shi idanunta suka gani?,anwar shine ya mata wannan tozarcin?,wanne abu tayi mai munin da har zaikai anwar ya kasa mantawa irin haka ya sake binta da mummunan shaida da wulaqanci?.
Kusan haka ta dauki dogon lokaci,wanda ita din batasan wadanne awanni ta shafe haka ba,sai tsintar muryoyin anty zubaida tayi da huda,taso qwarai ta tashi amma ta kasa saboda wani mugun ciwo da kanta yake mata,da qyar take iya motsawa bayaga idanunta da suka zama tamkar fulawar da aka zubawa yeast,muryar saddiq taji yana cewa
"Mummy...tana dakinta" a hankali anty zubaida ta turo qofar tana cewa
"Alhmdlh,shahida kin daga mana hankali,ina kika shiga haka ke kuwa don Allah" ta qarashe maganar tana qarasowa kanta,zaro ido anty zubaida tayi ganin irin rawar darin da take yi
"Subhanallahi,ashe bakyajin dadi" ta qaraso gefan gadon shahida ta zauna tana qoqarin yaye rufar da tayi,da qyar da taimakon anty zubaidan ta tashi ta zauna sosai,qarya tayi mata kan tana shiga makaranta zazzabi ya saukar mata shi yasa ta dawo bata kai ga zuwa dakin hutun ba ganin yadda duk suka damu daga anty zubaidan har su saddiq,farouq anty zubaida ta saka ya hada mata ruwan wanka,saddiq ya zubo mata abinci,ita taimaka mata ta shiga bandaki tayi wanka gami da daura alwalar sallar azahar da magariba da duka bata samu yinsu ba,bata bar dakin ba sai data ga taci abinci ta kuma sha magani sannan.
Tana daga kwancen amma hawaye take sharcewa masu dumi,duk yadda taso ga kaucewa anwar da shafe duk wani abu daya shafeshi amma haka yaci tura?,wai sai yaushe?,sai yaushe zaibar rayuwarta zuciyarta da kuma ruhinta ya huta?wunin ranar gaba daya wani irin wahalallen yini tayi,ba shakka anwar ya zamewa rayuwarta babban qalubale,har zuwa dare tana cikin yanayi guda wanda da qyar da sudin goshi ta samu wani wahalallen bacci ya dauketa.
********* **********
A hankali ya daga cup din qarshe na coffe din da yayi saura ya kwankwade wanda shi kansa baisan kofi nawa yasha ba tsahon awannin daya kwashe zaune a wajen,idanunsa jajur suke kai kace an badawa idanunsa yaji ne a ciki,saidai yaqi yarda ko kusa ko alama a kira masa likita ya dubashi,bugu da qari dumin jikinsa ya qaru sosai har kana iya juyo hucinsa idan ya fidda iska daga bakinsa.
Lumshe idanunsa yayi ya dora hannunsa saman sumarshi mai tauri saidai a gyare take matuqa yana yamutsata,buri yake inama ya iya kuka idan yana cikin tashin hankali ko tsanani,inama hawaye zasu fita daga idanunshi ko zai samu sauqin radadin da yake ji?,cikin sauri ya sake bude idanun shi wanda suka sake kadawa fiye da dazu,ko yaya ya runtsesu kwalaben da suka zubo daga jakarta yake gani,hakan yana nuna har yau bata bar dabu'arta ba?,waishin waye ne?,waye ya koya mata wannan dabi'ar?,babu shakka da zaisan waye shida ita duka saiya hadasu ya hukuntasu,dukan teburin gabansa yayi da hannunsa ko zaiji sauqin radadin da zuciyarsa ke masa amma a banza.
Knocking katafariyar qofar falon aka somayi wanda yana ji yayi funfurus,saidai ya cika ya batse saboda koma waye yana son sake birkita masa lissafi ne,bayan kuma ya riga da yaja kunnen duka ma'aikatan gidan na kada wanda ya sake yako doshi sashensa.
Knociking din jinsa yake har qwaqwalwarsa,hakan ya sanya ya miqe a fusace ya isa qofar ya budeta ya kuma bude baki don zazzagewa koma waye masifa,muhsin ne bayanshi likita ne tsaye cikin fararen kayan aiki,dole ya hadiye abinda yaso amayarwa ya saki qofar ya juya zuwa cikin falon ya zabi wata kujerar sabanin wadda ya tashi daga kai ya zube yana maida numfashi,kallo daya muhsin yayi masa baice dashi komai ba ya kalli likitan sannan ya maida idonsa ga anwar din
"Zaka iya aikinka" yace dashi,saiyaka jinjina kai ya soma takawa inda anwar ke zaune ya aje akwatinshi kana ya bude,ya ciro abun gwada B.P ya daura a hannun anwar ya soma gwadawa,cikin sakannin da basu wuce goma ba ya warware abun daga dantsensa ya samu kujerar dake daura dashi ya zauna sosai idanunsa a kanshi
"Yallabai....kasan yadda jininka ya sake hawa kuwa?" Ya tambayeshi kanshi tsaye
"Na sani" shima ya bashi amsa bayan ya sake bude dukka idanunshi akan likitan,cikin mamaki likitan ya maida dubanshi ga muhsin,saiya masa alama daya rubuta magani kawai ya qyaleshi,hakan kuwa akayi ya rubuta maganin ya baiwa muhsin takardar sannan ya tattara kayanshi ya yuwa muhsin din sallama ya wuce.
"Kina nufin a haka zaki baiwa yaran mutane tarbiyya?,a haka kike koyar da yaran jama'a?,na tambayeki ma me kike koya musu?,uhmmm gayamin,?,yadda zasu....." Sai kuma ya kasa qarasawa ya kaiwa iska wafta da hannunshi sannan ya dunquleshi tsam kaman zai tatse dukkan jinin dake cikin hannun nashi gaba daya,dai dai sanda shugaba kula da dukka sashen makarantar ya iso ganin shuru har yanzu bai iso ba,cikin girmamawa ya rusuna
"Sir....."
"Dakata!" Ya tsaidashi cikin tsawa
"Dama irin wadan nan malaman kuke baiwa yara su koyar?" Cikin mamaki ya dubi shahida da yake nuna masa,wadda take tsaye qam a wajen kaman an dasata idanunta kan anwar,tana jin wani fushi na ratsata amma tana ta qoqarin hana hakan tasiri
"Sir.....kodai wani akasi aka samu,amma malama shahida na daya daga cikin malaman da kaf makarantar nan babu kamarsu a kowanne sashe"
"Sauraramin" ya kuma dakatar dashi wannan karon har yana daga mishi hannu,ya maida idanunsa cikin nata
"Indai wannan ce malamar da babu kamarta tabbas bakusan abinda kuke ba,babu abinda ta iya!,bata iya komai ba!,daga yau na koreta!,na koreta cikin malaman makarantar nan.....kar qafarki ta sake tako mana makaranta,you are fired!" Dukkan wani qwarin gwiwa da taso tattarowa ya tarwatse da kalmarshi na qarshe saboda yadda sautin ya fito ya bada amsa kuwwa cikin ajin,qoqarin tattaro abinda zata fada take saidai bakinta ya gaza fidda sautin saboda karayar da zuciyarta tayi,idanunta suka hada qwalla fal suna shirin ga gangarowa,saiya sake saka idanunsa cikin nata cikin wani qwarin gwiwa da yake ji yace
"Uhmm...kina da wani abun cewa ne?....say it....say it mana!" Ya kuma fada cikin hargagi yana dan dukan qirjinsa da yatsunshi gaba daya,jakar dake kafadarta ce ta sulmiyo saboda yadda jikinta ya soma rawa,gaba daya kayan ciki suka tarwatse a wajen ciki harda kwalaben magungunan huda,a kansu idanunsa suka soma sauka,wani tashin hankali da baisan na meye ba ya rufto masa,saiya daga kai da sauri yana kallonta,sam ko daya bata da nutsuwar da zata iya tsaiwa ta tattare kayayyakinta ko ta dauki jakar,hakan yasa ta juya da sauri ta soma takawa,fatanta da burinta kawai shine tabar makarantar,tabar wajen,tabar inuwar da anwar yake tsaye a cikinta,burinta shine ta nesanta dashi kawai,ta daina ganinsa ta kuma daina jin sautinsa
"Ki dawo ki debi wannan kayan zatar naki" maimakon dawowar kamar yadda ya buqata saita qara sauri kamar wadda aka biyo,don burinta shine ficewa daga makarantar ta tserewa sautinsa,wannan sautin da ta jima da neman tsari dashi da mamallakinsa.
Titi kawai ta miqa bata ko waiwaye,bata buqatar abun hawa don ji take kaman qafafunta zasuyi mata aiki fiye da abun hawan,sauri kawai take zubawa wani irin radadi na keta zuciyarta kamar ana yankarta da reza,anwar dai anwar dai?,tabbas da tasan akwai wata rana da zasu sake haduwa kaman haka da tuni ta yiwa kanta kandagarki da ita,wannan wace irin baqar rana ce a wajenta
"Anty shahida...anty shahida" taji ana qwalla mata kira wanda sam bata tsaya ba har sai da akasha gabanta,shugaban sashe ne riqe da jakarta ya miqa mata
"Don girman Allah kiyi haquri anty shahida,ya dauki hukuncin da dukkanmu bamu isa mu sauya shi ba"
👑 *zafafa biyar na kudi ne,idan kika gani don GIRMAN ALLAH karkiyi sharing,idan kina buqatar siya ki tuntubi wadan nan numbers din*
07067124863
*ko kuma*
09032345899
*kuyi subscribing youtube channel dina don samun damar ganin shirye shiryenmu,subscribe kyauta ne!*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos
*Alqawarin Allah*
1️⃣9️⃣
"sabon abune wannan a wajenmu,abinda bamu taba gani yayi ba tunda muke dashi,kowa ya shaidai wannan kirkin nasa....anty shahida kodai wani abu kika masa?,mutumin qwarai irin haka canzawarsa...."da sauri ta yanke masa hanzari
"Na gode malam,haka Allah ya qaddara" gaba tayi da sauri don ita kadai tasan me take ji,ita daya tasan ya take ji,baifi taku biyar ba adaidaita sahu tasha gabanta tana tambayarta ina zata je?,sai data shiga sannan ta gaya mishi inda zai kaita,duk yadda taso daure zuciyarta ta bari saita isa gida saita kasa,ta tattakura ta rushe da kuka wanda har sai da dan sahun ya waiwayo
"Hajiya...lafiya?,kiyi haquri komai yayi zafi maganinsa Allah" ita dai bata iya tanka masa ba illa kukanta data ci gaba dayi.
Komao nata ta wurgar tsakar dakinta sannnan ta zauna dirshan tana risgar kuka,tanajin kaman ranta zai fita ne,duk wata nutsuwarta a yanzu babu ita,anwar dai shi idanunta suka gani?,anwar shine ya mata wannan tozarcin?,wanne abu tayi mai munin da har zaikai anwar ya kasa mantawa irin haka ya sake binta da mummunan shaida da wulaqanci?.
Kusan haka ta dauki dogon lokaci,wanda ita din batasan wadanne awanni ta shafe haka ba,sai tsintar muryoyin anty zubaida tayi da huda,taso qwarai ta tashi amma ta kasa saboda wani mugun ciwo da kanta yake mata,da qyar take iya motsawa bayaga idanunta da suka zama tamkar fulawar da aka zubawa yeast,muryar saddiq taji yana cewa
"Mummy...tana dakinta" a hankali anty zubaida ta turo qofar tana cewa
"Alhmdlh,shahida kin daga mana hankali,ina kika shiga haka ke kuwa don Allah" ta qarashe maganar tana qarasowa kanta,zaro ido anty zubaida tayi ganin irin rawar darin da take yi
"Subhanallahi,ashe bakyajin dadi" ta qaraso gefan gadon shahida ta zauna tana qoqarin yaye rufar da tayi,da qyar da taimakon anty zubaidan ta tashi ta zauna sosai,qarya tayi mata kan tana shiga makaranta zazzabi ya saukar mata shi yasa ta dawo bata kai ga zuwa dakin hutun ba ganin yadda duk suka damu daga anty zubaidan har su saddiq,farouq anty zubaida ta saka ya hada mata ruwan wanka,saddiq ya zubo mata abinci,ita taimaka mata ta shiga bandaki tayi wanka gami da daura alwalar sallar azahar da magariba da duka bata samu yinsu ba,bata bar dakin ba sai data ga taci abinci ta kuma sha magani sannan.
Tana daga kwancen amma hawaye take sharcewa masu dumi,duk yadda taso ga kaucewa anwar da shafe duk wani abu daya shafeshi amma haka yaci tura?,wai sai yaushe?,sai yaushe zaibar rayuwarta zuciyarta da kuma ruhinta ya huta?wunin ranar gaba daya wani irin wahalallen yini tayi,ba shakka anwar ya zamewa rayuwarta babban qalubale,har zuwa dare tana cikin yanayi guda wanda da qyar da sudin goshi ta samu wani wahalallen bacci ya dauketa.
********* **********
A hankali ya daga cup din qarshe na coffe din da yayi saura ya kwankwade wanda shi kansa baisan kofi nawa yasha ba tsahon awannin daya kwashe zaune a wajen,idanunsa jajur suke kai kace an badawa idanunsa yaji ne a ciki,saidai yaqi yarda ko kusa ko alama a kira masa likita ya dubashi,bugu da qari dumin jikinsa ya qaru sosai har kana iya juyo hucinsa idan ya fidda iska daga bakinsa.
Lumshe idanunsa yayi ya dora hannunsa saman sumarshi mai tauri saidai a gyare take matuqa yana yamutsata,buri yake inama ya iya kuka idan yana cikin tashin hankali ko tsanani,inama hawaye zasu fita daga idanunshi ko zai samu sauqin radadin da yake ji?,cikin sauri ya sake bude idanun shi wanda suka sake kadawa fiye da dazu,ko yaya ya runtsesu kwalaben da suka zubo daga jakarta yake gani,hakan yana nuna har yau bata bar dabu'arta ba?,waishin waye ne?,waye ya koya mata wannan dabi'ar?,babu shakka da zaisan waye shida ita duka saiya hadasu ya hukuntasu,dukan teburin gabansa yayi da hannunsa ko zaiji sauqin radadin da zuciyarsa ke masa amma a banza.
Knocking katafariyar qofar falon aka somayi wanda yana ji yayi funfurus,saidai ya cika ya batse saboda koma waye yana son sake birkita masa lissafi ne,bayan kuma ya riga da yaja kunnen duka ma'aikatan gidan na kada wanda ya sake yako doshi sashensa.
Knociking din jinsa yake har qwaqwalwarsa,hakan ya sanya ya miqe a fusace ya isa qofar ya budeta ya kuma bude baki don zazzagewa koma waye masifa,muhsin ne bayanshi likita ne tsaye cikin fararen kayan aiki,dole ya hadiye abinda yaso amayarwa ya saki qofar ya juya zuwa cikin falon ya zabi wata kujerar sabanin wadda ya tashi daga kai ya zube yana maida numfashi,kallo daya muhsin yayi masa baice dashi komai ba ya kalli likitan sannan ya maida idonsa ga anwar din
"Zaka iya aikinka" yace dashi,saiyaka jinjina kai ya soma takawa inda anwar ke zaune ya aje akwatinshi kana ya bude,ya ciro abun gwada B.P ya daura a hannun anwar ya soma gwadawa,cikin sakannin da basu wuce goma ba ya warware abun daga dantsensa ya samu kujerar dake daura dashi ya zauna sosai idanunsa a kanshi
"Yallabai....kasan yadda jininka ya sake hawa kuwa?" Ya tambayeshi kanshi tsaye
"Na sani" shima ya bashi amsa bayan ya sake bude dukka idanunshi akan likitan,cikin mamaki likitan ya maida dubanshi ga muhsin,saiya masa alama daya rubuta magani kawai ya qyaleshi,hakan kuwa akayi ya rubuta maganin ya baiwa muhsin takardar sannan ya tattara kayanshi ya yuwa muhsin din sallama ya wuce.