Sashe 48
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari qarfe goma na safe tana gaban mudubi a zaune tana kallon yadda fuskarta ta qojale saboda kukan data kwana tana yi wayar ta sake burari,wannan karonma anwar ne a maimakon mima,bata da mafita tilas ta daga wayar ta sake gaya masa kalaman da zasu tabbatar masa da cewa ta rabu dashi kp hakan zai tsoratashi ya janye nufinsa
"Karka sake kirana matsawar kana kan qudurinka na hada aurena da wata macen daban,na gaya maka tun jiya nikam nafisa bazan aureka ba anwar muddin kana a matsayin mijin mace biyu,na haqura dakai har abada" daga haka ta yanke kiran,saiya furzar da numfashi daga bakinsa ya baiwa banza ajiyarta,ya aje wayarshi yaci gaba da shirinsa,shikam ya yankema ransa babu sauran wata mace da zata sake bashi wahala,bazai sake son wata ba bare ta gasa mishi zuciya yadda ya faru dashi a baya,ya saki qaramin murmushi sanda ya tuna cewa da sonta yake da tuni yanzu yana cikin tashin hankali da dimuwa a sanda tace bata sonshi,yanzun kam hankalinshi kwance yake jinsa,saidai kuma wani bari na zuciyarsa yana dan jin damuwa,musamman idan ya tuna da mahaifanta yadda zasu dauki maganar,da wannan tunanin ya gama shirinsa ko abinci yau bai saurara ba ya dauki muqullinsa ya fito,kafin ya tashi motarsa ya tsaya ya turawa anty usaina yadda sukayi da nafisan,don baison kiranta ma bare ta bijiro da wani abun da zai hanashi uzurinsa nayau.
***** ****** ****** *****
"Wannan sakarcin banza ne ai sakarcin wofi,ta isa ta haramta abinda Allah ya halatta?" Alhj abba mahaifin nafisa ya fada cikin fushi da bacin rai yana duban mummy mahaifiyarta,kai ta gyada itama,sau tari tana mamakin halayen nafisan,ta rasa inda take debo wasu baqaqen halayen,abubuwa da yawa ita dai ta sani ba halayyarta bace kota mahaifinta ba
"Atoh,nayi mata magana daxun da safe ta nunamin tana kan bakanta" mummy ta baiwa alhj abba amsa,shikam anwar yana daga gefe kanshi a qasa cikin girmamawa yana saurarensu,baice komai ba sai a sannan
"Kuyi mata uzuri,duba da yadda zancan ya sameta a qurarren lokacin da bata zata ba,ni kaina bani da masaniyar abun zai kasance haka sai gab da zanyi tafiya,sai naga yafi kyau idan na dawo na shaida mata mu fahimci juna,to sai kuma aka samu sabanin fahimta"
"Qarancin hankali da tunani dai,ita zata zauna maka da ita?,ko ita haqqin kula da ita yake kanta?,bilki....kiramin ita maza" a nutse hajiyan ta miqe ta fice zuwa dakin nafisan.
Kwance take rub da ciki tana aikin kuka,tana son anwar tana tsoron rabuwa dashi,tana tsoron yaqi janye qudurinsa,don itakam ba abinda zai sata ta sauka daga kan bakanta,matsawar ta yarda ta aureshi to yaqin da tayi shekara da shekaru tana yi,kudinta data kashe,lokacinta data fansar duka sun tashi a babin badinuhu bataci riba ba kenan
"Kin hadu da aiki kuma kin gama kanki da wahala wallahi,tunda kin daukama kanki aqidar banza da wofi,ki tashi kije mahaifinki nason ganinki" cewar mummy daga haka bata qara ba ta juya tayi ficewarta.
Sanda ta isa falon anwar ta soma gani,kishinsa ya sake lullubeta ganin yadda kamar ma sake kyau da fresh yayi abinsa tsakanin kwanakin da ita take fama da quncin zuciya,gefan abban nata ta zauna ya dubeta
"Nafi,wanne irin shashanci da sakalci kike shirin aikatawa haka?,saboda Allah ya halatta masa auren daga daya zuwa hudu saikice ba zaki aureshi ba saboda haka?,zaki sauya hukuncin Allah kenan?,koke kikayi kanki?to kar naji karna gani,banason wannan shirmen banza,yana da damarma yace biyu zaiyi kece ata uku" Kuka ta saki sosai
"Abba...wallahi bazan aureshi ba,bazan iya zama dashi da wata ba"baki bude alhj abba ya watsa mata daquwa
"Kinci gidanku,kajimin fitinanniyar yarinya?,to saikin aureshin naga wanda ya isa ya hana" miqewa tayi cikin kuka
"Wallahi abba zan gudu,zan barku idan aka aura min shi" mummy na shirin kai mata duka saboda takaici ta fice a guje daga falon.
Shuru ne ya ratsa falon,kunya da takaici na kama alhj abba da hajiya bilkisu,sai suka rasa ta inda zasu kama zancan,sunsan halin nafisa sarai sai addu'a,karta aikata wani abu da zai zama musu illa nan gaba,anwar ya fahimci shurunsu saboda haka yace
"Alhj,karka damu,Dukkaninmu ni da kai da mummy bamu da ikon da zamu sauya mata ra'ayi,sannan duk yadda mukaso abin itace zata zauna,dole saida gamsuwarta sannan komai zai tafi yadda ake buqata"ajiyar zuciya suka saki dukansu kusan a tare cikin bacin rai da takaici
"Yarone ka haifeshi baka haifi halinsa ba,kayi haquri anwar" cewar alhj abba yana jin babu dadi har cikin ransa,yana jin kaman ya muzanta
"Haka Allah ya qaddara" anwar din ya furta kanshi a qasa,shima yana jin babu dadi saboda yadda sukejin laifin kaman a kansu yake.
Tana zaune har yanzu inda ta zauna tana rusar kuka a haka mummy ta tura qofar dakin ta sameta,da hanzari ta daga kai cikin fargaba da razani tare da taraddin furucin da zai fito daga bakin mummyn,tana son anwar tana fata ace ya karbi muradinta
"Shikenan ko?,burinki ya cika?,saikije ki samo wani mijin wanda yafi anwar" daga haka ta juya abinta ta fice tabar mata dakin,cikin tashin hankali ta miqe kaman zata bi bayan mommy don samun qarin bayani,sai kuma ta dawo da baya qwaqwalwarta na gaya mata ma'anar maganar mummyn,anwar ya barta?,anwar ya zabi shahida akanta?,wahalarta ta tashi a banza kenan?,kai ta shiga girgizawa tana fadin bazaiyiwu ba,ta dauki wayarta ta soma kiran layin mima ba qaqqautawa don tana da buqatarta a yau fiye da kullum,saidai amsar dai daya ce wayar a kashe take.
A qalla ta kwashi awa kusan biyu a haka,bata da wata mafita ayanzu banda ta kira anwar,ta soma laluben number dinsa ta kira.
Fitowarsa kenan daga kitchen dauke da cup na coffe wanda ya shiga ya hada da kansa,cikin mamaki yake duban mai kiran,saiya samu daya daga cikin kujerun falon ya zauna yana amsa wayar
"Ni zaka yiwa haka anwar?,ni nafisa zaka gujewa saboda wata banzar shahida da bata kama qafata wajen qaunarka ba?,idan baki sani ba bari yau na fada maka,ni nafisa nice silar duk wani arzqinka,nice silar duk wani matsayi daka taka a yau,nice silar zamantowa abinda kake a yanxu,amma sakayyar da zaka yimin kenan?,ka zabi wata akaina?"
"Kin gama?" Ya furta a nutse yana saurarenta,jin batace komai ba yasa ya dora
"Na farko ba wani bawa daya isa ya azurta wani bawa dukkaninmu muna cine cikin taskar ubangiji,abu na biyu banyi zabe ba hakan ban fifita ba,kece wadda kika zabarwa kanki haka,ko a yanxu kika yarda da abinda nazo dashi,kika amince da cewa qaddararmu ce gaba daya ina maraba da hakan,saboda haka zabi ya rage game shiga rijiya" daga haka ya datse kiran ya aje wayar gefanshi,yadda yake tsammanin zai damu ko zaiji ciwo saiyaga duka ba haka bane,abu daya cikin daruruwan daya sanya ya kasa baiwa nafisa koda digo daya cikin dari na so ko qauna a zuciyarsa kenan,bata da lafazin magana,bata da tarbiyya yiwa kai waigi a duk sanda rai ya baci,ya godewa Allah daya sanya ya maida dukkan kudaden da kamfani da kuma alhj abba ya bashi a wancan lokacin ya zabi yaci gashin kanshi ba tarema da yasan waye yayi silar zuwanshi wajen ba,saiya dauki coffensa a hankali ya soma kurba ba tare daya ji wata gagarumar damuwa ba.
Kira ya sake shigowa wayar tashi,ya dauka itace dai sai yaga anty usaina,ya amsa wayar bayan sun gaisa ga gaya masa komai ya kammala kuma jibi ne zasu miqa lefan
"Shikenam babu damuwa,Allah ya nuna mana,saidai na nafisa ki ajesu wajenki,zan shigo gobe zamuyi magana"
"Allah ya nuna mana" ta amsa masa.
Wayarsa ya dauka yana duba jerin numbers din dake cikin wayar,kaf wayar babu number dinta,ba abun mamaki bane don yasan dama da zaman hakan,rabonshi da number dinta ta rabi wayarshi cikin xamanin da yake amfani da waya keypad,wayar da har yanzu bai rabu da ita ba,hakanan baisan dalilin qin rabuwa da ita ba,saiya koma neman number wayar sulaiman,bugu uku ya daga,suka gaisa ya gaya masa ya kaiwa daada wayar,ya shaida masa yana kusa da ita,sabida haka ya miqa mata wayar,bayan sun gaisa cikin mutunta juna sun dan taba wasa irin na jika da kaka da suke lokaci zuwa lokaci,don jin anwar din take kamar jikanta na jini
"Jibi xasu miqa kayan daada,na nemi number dinta ban samu ba,ko zaki nemi wani cikin gidan a shaida masa"
"Karka damu,sule nada lambar zubaida,yanzu zansa ya kirata ya gaya mata" hira suka dan qra tabawa kadan yana tsokanarta sannan sukayi sallama.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana kurban coffensa idanunsa saman tv da aka ragewa volume sosai,tunani nason fisgarsa yana jefashi wata duniya can,zamanin da dukkaninsu shida shahidan keda buri da fatan mallakar junansu,zamanin da kowannensu yake kwana ya kuma tashi da marari soyayya da begen dan uwanshi,a sannan dukkan mafarkinsu da fatansu ya ta'allaqa ne akan lokacin da zasu zama mallakin juna,lokacin da dukansu shida ita quruciyarsu ta ninka ta yanzj qwarai,bai mantawa wani lokaci daya je hira suna hirar qawar shahida da aka kaiwa lefe,ganin yadda yake nuna buri da fatan yiwa shahidan lefe mai yawa na kece sa'a yasa tace
"Nifa yaa anwar,basai ka takura kanka ba,nifa ba wani lefe da zakamin,ni ba kaya nakeso ba..."
"Me kikeso...?" Ya fada yana tsareta da ido cikin wani salon kallo da baisan yana mata ba saboda shagwabarta data tafi dashi,yasandai cewa sanda yake kallonta din soyayyarta da qaunarta na narkewa tana sake kwaranya cikin magudanan jininsa,kallon da yake mata ya sanyata jin kunya harta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana dariya
"Kai nakeso ni"
"Na sani shahida,amma kullum burina shine na daga darajar shahida cikin mata,kullum burina shahida tafi kowacce mace a duniya,indai ina dashi dole shahidana ta fita daban,kita min addu'a shahida,idan na tashi zan miki lefe irin wanda kowacce mace xatayi burinsa" idanunta ta zaro tana kallonshi
"Ya anwar?,ranar kuwa zanyi bacci?,ya anwar dina yayimin kaya irin haka ranar kowacce mace saidai ta biyo bayana"
"Qwarai kuwa,wannan dan qaramin bakinkin ya iya furta kalmomi masu zaqi da tsayawa a rai" dariya sukayi a tare tana kife fuskarta akan cinyarta.
Yana kawowa nan wani qaramin murmushi da bai shirya ba ya subuce saman fuskarsa,saiya aje cup din,lokaci guda wani abu yayi kutse cikin farincikin daya tsinci kasa,ya soma juyawa zuwa bacin rai,da sauri ya soma furta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin,saiya miqe ya dauki cup dinsa ya haura sama inda bedroom dinsa yake dashi.
"Karka sake kirana matsawar kana kan qudurinka na hada aurena da wata macen daban,na gaya maka tun jiya nikam nafisa bazan aureka ba anwar muddin kana a matsayin mijin mace biyu,na haqura dakai har abada" daga haka ta yanke kiran,saiya furzar da numfashi daga bakinsa ya baiwa banza ajiyarta,ya aje wayarshi yaci gaba da shirinsa,shikam ya yankema ransa babu sauran wata mace da zata sake bashi wahala,bazai sake son wata ba bare ta gasa mishi zuciya yadda ya faru dashi a baya,ya saki qaramin murmushi sanda ya tuna cewa da sonta yake da tuni yanzu yana cikin tashin hankali da dimuwa a sanda tace bata sonshi,yanzun kam hankalinshi kwance yake jinsa,saidai kuma wani bari na zuciyarsa yana dan jin damuwa,musamman idan ya tuna da mahaifanta yadda zasu dauki maganar,da wannan tunanin ya gama shirinsa ko abinci yau bai saurara ba ya dauki muqullinsa ya fito,kafin ya tashi motarsa ya tsaya ya turawa anty usaina yadda sukayi da nafisan,don baison kiranta ma bare ta bijiro da wani abun da zai hanashi uzurinsa nayau.
***** ****** ****** *****
"Wannan sakarcin banza ne ai sakarcin wofi,ta isa ta haramta abinda Allah ya halatta?" Alhj abba mahaifin nafisa ya fada cikin fushi da bacin rai yana duban mummy mahaifiyarta,kai ta gyada itama,sau tari tana mamakin halayen nafisan,ta rasa inda take debo wasu baqaqen halayen,abubuwa da yawa ita dai ta sani ba halayyarta bace kota mahaifinta ba
"Atoh,nayi mata magana daxun da safe ta nunamin tana kan bakanta" mummy ta baiwa alhj abba amsa,shikam anwar yana daga gefe kanshi a qasa cikin girmamawa yana saurarensu,baice komai ba sai a sannan
"Kuyi mata uzuri,duba da yadda zancan ya sameta a qurarren lokacin da bata zata ba,ni kaina bani da masaniyar abun zai kasance haka sai gab da zanyi tafiya,sai naga yafi kyau idan na dawo na shaida mata mu fahimci juna,to sai kuma aka samu sabanin fahimta"
"Qarancin hankali da tunani dai,ita zata zauna maka da ita?,ko ita haqqin kula da ita yake kanta?,bilki....kiramin ita maza" a nutse hajiyan ta miqe ta fice zuwa dakin nafisan.
Kwance take rub da ciki tana aikin kuka,tana son anwar tana tsoron rabuwa dashi,tana tsoron yaqi janye qudurinsa,don itakam ba abinda zai sata ta sauka daga kan bakanta,matsawar ta yarda ta aureshi to yaqin da tayi shekara da shekaru tana yi,kudinta data kashe,lokacinta data fansar duka sun tashi a babin badinuhu bataci riba ba kenan
"Kin hadu da aiki kuma kin gama kanki da wahala wallahi,tunda kin daukama kanki aqidar banza da wofi,ki tashi kije mahaifinki nason ganinki" cewar mummy daga haka bata qara ba ta juya tayi ficewarta.
Sanda ta isa falon anwar ta soma gani,kishinsa ya sake lullubeta ganin yadda kamar ma sake kyau da fresh yayi abinsa tsakanin kwanakin da ita take fama da quncin zuciya,gefan abban nata ta zauna ya dubeta
"Nafi,wanne irin shashanci da sakalci kike shirin aikatawa haka?,saboda Allah ya halatta masa auren daga daya zuwa hudu saikice ba zaki aureshi ba saboda haka?,zaki sauya hukuncin Allah kenan?,koke kikayi kanki?to kar naji karna gani,banason wannan shirmen banza,yana da damarma yace biyu zaiyi kece ata uku" Kuka ta saki sosai
"Abba...wallahi bazan aureshi ba,bazan iya zama dashi da wata ba"baki bude alhj abba ya watsa mata daquwa
"Kinci gidanku,kajimin fitinanniyar yarinya?,to saikin aureshin naga wanda ya isa ya hana" miqewa tayi cikin kuka
"Wallahi abba zan gudu,zan barku idan aka aura min shi" mummy na shirin kai mata duka saboda takaici ta fice a guje daga falon.
Shuru ne ya ratsa falon,kunya da takaici na kama alhj abba da hajiya bilkisu,sai suka rasa ta inda zasu kama zancan,sunsan halin nafisa sarai sai addu'a,karta aikata wani abu da zai zama musu illa nan gaba,anwar ya fahimci shurunsu saboda haka yace
"Alhj,karka damu,Dukkaninmu ni da kai da mummy bamu da ikon da zamu sauya mata ra'ayi,sannan duk yadda mukaso abin itace zata zauna,dole saida gamsuwarta sannan komai zai tafi yadda ake buqata"ajiyar zuciya suka saki dukansu kusan a tare cikin bacin rai da takaici
"Yarone ka haifeshi baka haifi halinsa ba,kayi haquri anwar" cewar alhj abba yana jin babu dadi har cikin ransa,yana jin kaman ya muzanta
"Haka Allah ya qaddara" anwar din ya furta kanshi a qasa,shima yana jin babu dadi saboda yadda sukejin laifin kaman a kansu yake.
Tana zaune har yanzu inda ta zauna tana rusar kuka a haka mummy ta tura qofar dakin ta sameta,da hanzari ta daga kai cikin fargaba da razani tare da taraddin furucin da zai fito daga bakin mummyn,tana son anwar tana fata ace ya karbi muradinta
"Shikenan ko?,burinki ya cika?,saikije ki samo wani mijin wanda yafi anwar" daga haka ta juya abinta ta fice tabar mata dakin,cikin tashin hankali ta miqe kaman zata bi bayan mommy don samun qarin bayani,sai kuma ta dawo da baya qwaqwalwarta na gaya mata ma'anar maganar mummyn,anwar ya barta?,anwar ya zabi shahida akanta?,wahalarta ta tashi a banza kenan?,kai ta shiga girgizawa tana fadin bazaiyiwu ba,ta dauki wayarta ta soma kiran layin mima ba qaqqautawa don tana da buqatarta a yau fiye da kullum,saidai amsar dai daya ce wayar a kashe take.
A qalla ta kwashi awa kusan biyu a haka,bata da wata mafita ayanzu banda ta kira anwar,ta soma laluben number dinsa ta kira.
Fitowarsa kenan daga kitchen dauke da cup na coffe wanda ya shiga ya hada da kansa,cikin mamaki yake duban mai kiran,saiya samu daya daga cikin kujerun falon ya zauna yana amsa wayar
"Ni zaka yiwa haka anwar?,ni nafisa zaka gujewa saboda wata banzar shahida da bata kama qafata wajen qaunarka ba?,idan baki sani ba bari yau na fada maka,ni nafisa nice silar duk wani arzqinka,nice silar duk wani matsayi daka taka a yau,nice silar zamantowa abinda kake a yanxu,amma sakayyar da zaka yimin kenan?,ka zabi wata akaina?"
"Kin gama?" Ya furta a nutse yana saurarenta,jin batace komai ba yasa ya dora
"Na farko ba wani bawa daya isa ya azurta wani bawa dukkaninmu muna cine cikin taskar ubangiji,abu na biyu banyi zabe ba hakan ban fifita ba,kece wadda kika zabarwa kanki haka,ko a yanxu kika yarda da abinda nazo dashi,kika amince da cewa qaddararmu ce gaba daya ina maraba da hakan,saboda haka zabi ya rage game shiga rijiya" daga haka ya datse kiran ya aje wayar gefanshi,yadda yake tsammanin zai damu ko zaiji ciwo saiyaga duka ba haka bane,abu daya cikin daruruwan daya sanya ya kasa baiwa nafisa koda digo daya cikin dari na so ko qauna a zuciyarsa kenan,bata da lafazin magana,bata da tarbiyya yiwa kai waigi a duk sanda rai ya baci,ya godewa Allah daya sanya ya maida dukkan kudaden da kamfani da kuma alhj abba ya bashi a wancan lokacin ya zabi yaci gashin kanshi ba tarema da yasan waye yayi silar zuwanshi wajen ba,saiya dauki coffensa a hankali ya soma kurba ba tare daya ji wata gagarumar damuwa ba.
Kira ya sake shigowa wayar tashi,ya dauka itace dai sai yaga anty usaina,ya amsa wayar bayan sun gaisa ga gaya masa komai ya kammala kuma jibi ne zasu miqa lefan
"Shikenam babu damuwa,Allah ya nuna mana,saidai na nafisa ki ajesu wajenki,zan shigo gobe zamuyi magana"
"Allah ya nuna mana" ta amsa masa.
Wayarsa ya dauka yana duba jerin numbers din dake cikin wayar,kaf wayar babu number dinta,ba abun mamaki bane don yasan dama da zaman hakan,rabonshi da number dinta ta rabi wayarshi cikin xamanin da yake amfani da waya keypad,wayar da har yanzu bai rabu da ita ba,hakanan baisan dalilin qin rabuwa da ita ba,saiya koma neman number wayar sulaiman,bugu uku ya daga,suka gaisa ya gaya masa ya kaiwa daada wayar,ya shaida masa yana kusa da ita,sabida haka ya miqa mata wayar,bayan sun gaisa cikin mutunta juna sun dan taba wasa irin na jika da kaka da suke lokaci zuwa lokaci,don jin anwar din take kamar jikanta na jini
"Jibi xasu miqa kayan daada,na nemi number dinta ban samu ba,ko zaki nemi wani cikin gidan a shaida masa"
"Karka damu,sule nada lambar zubaida,yanzu zansa ya kirata ya gaya mata" hira suka dan qra tabawa kadan yana tsokanarta sannan sukayi sallama.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana kurban coffensa idanunsa saman tv da aka ragewa volume sosai,tunani nason fisgarsa yana jefashi wata duniya can,zamanin da dukkaninsu shida shahidan keda buri da fatan mallakar junansu,zamanin da kowannensu yake kwana ya kuma tashi da marari soyayya da begen dan uwanshi,a sannan dukkan mafarkinsu da fatansu ya ta'allaqa ne akan lokacin da zasu zama mallakin juna,lokacin da dukansu shida ita quruciyarsu ta ninka ta yanzj qwarai,bai mantawa wani lokaci daya je hira suna hirar qawar shahida da aka kaiwa lefe,ganin yadda yake nuna buri da fatan yiwa shahidan lefe mai yawa na kece sa'a yasa tace
"Nifa yaa anwar,basai ka takura kanka ba,nifa ba wani lefe da zakamin,ni ba kaya nakeso ba..."
"Me kikeso...?" Ya fada yana tsareta da ido cikin wani salon kallo da baisan yana mata ba saboda shagwabarta data tafi dashi,yasandai cewa sanda yake kallonta din soyayyarta da qaunarta na narkewa tana sake kwaranya cikin magudanan jininsa,kallon da yake mata ya sanyata jin kunya harta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana dariya
"Kai nakeso ni"
"Na sani shahida,amma kullum burina shine na daga darajar shahida cikin mata,kullum burina shahida tafi kowacce mace a duniya,indai ina dashi dole shahidana ta fita daban,kita min addu'a shahida,idan na tashi zan miki lefe irin wanda kowacce mace xatayi burinsa" idanunta ta zaro tana kallonshi
"Ya anwar?,ranar kuwa zanyi bacci?,ya anwar dina yayimin kaya irin haka ranar kowacce mace saidai ta biyo bayana"
"Qwarai kuwa,wannan dan qaramin bakinkin ya iya furta kalmomi masu zaqi da tsayawa a rai" dariya sukayi a tare tana kife fuskarta akan cinyarta.
Yana kawowa nan wani qaramin murmushi da bai shirya ba ya subuce saman fuskarsa,saiya aje cup din,lokaci guda wani abu yayi kutse cikin farincikin daya tsinci kasa,ya soma juyawa zuwa bacin rai,da sauri ya soma furta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin,saiya miqe ya dauki cup dinsa ya haura sama inda bedroom dinsa yake dashi.