Sashe 20
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta bangaren shahida kuwa mahaifinta ne ya turo qofa ya tsinceta cikin wannan halin,wanda hakan ba qaramin kadashi yayi ba,bai gane a cikin maye take ba sai daya kamata zuwa cikin gida yaji tana surutai irin na wanda yasha wani abu ya bugu,saiya saketa suka zuba mata idanu shida ummanta suna kallonta,kasa tsaiwa tayi saita fadi luuu ta zube nata ci gaba da surutanta,wanda a nata tunanin anwar take kira ya tsaya tayi masa bayani,kuka umma ta fashe dashi yayin da abbanta cikin tashin hankali yace
"Ina kika barmin 'yata taje mariya?"
"Ina kuwa zan barta taje abba?,gaisuwar mutuwa suka je ita da qawarta" ta fada cikin tsananin tashin hankali da kuma kuka
"Wallahi wallahi ki tabbatar da cewa indai wani mummunan abu ya samu 'yata toki kuka da kanki" ya fada cikin hargagi yana nunata da yatsa,a ranar dai umma babu bakin magana ta diyarta take,salati kawai take tana duba jikin shahida daya lalace da jini,bandaki ta kaita tayi mata wanka wanda shiya sanya bacci ya kwasheta bayan ta dawo da ita daki.
🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍
Da salati ta farka tana qarewa dakin kallo,ko ba'a fada ba tasan dakin ummanta ne,a hankali ta soma tuna me ya faru da ita,tun daga barinsu inda sukaje zuwa gidan qawar fiddausi,sauketa da saurayin yayi a qofar gidansu,daga nan zaren tunanin nata ya yanke,tayi tayi ta sake tuno abinda ya faru ta kasa,zuciyarta na gaya mata taga anwar,wata zuciyar tana ce mata bashi bane.
Muryar umma ta jiyo tana kiranta cikin kakkausar murya wadda tasa hanjin cikinta kadawa
"Shahida....ina kikaje jiya?" Saita kasa amsa mata,indai har a wannan yanayin ta shigo gidansu to tabbas bata da bakin kare kanta,kafin ta sake cewa wani abu umman ta zube dukka kwalaben da suka fado a jakarta wanda tuni ta gama karantawa ta kuma fahimci kayan shaye shaye ne a ciki,idanun umman jajur tace mata
"Meye wannan shahida?" Kasa hada ido tayi da umman,hankalinta yayi qololuwar tashi,lafiyayyen mari umman ta sauke mata wanda ya gigitata,sannan yayi dai dai da shigowar abbanta dakin,wanda tunda ya fita sallar asuba daya daga cikin maqotansa ya masa jajen anga shahida an kawota qofar gida an yasar me ya sameta bai sake samun sukuni ba,yasan tabbas maganar akayita tattaunawa a jiya ana kuma sauya mata kamanni,yasan halin anguwar da 'yan unguwar kaf.
"Ai kibar dukanta bari na gaya miki mariya,koma meye shahida ta zama laifinki ne,kin zaki baki kin kasa bawa diyata tarbiyya shine yanzu zaki zo kina wani hargagin banza da wofi?" Cikin bacin rai da shiga zafi biyu ta maida masa amsa
"Indai shahida ta lalace ne kaima akwai laifinka,tunda kaima ubane ai ba'a dauke nauyin haqqin kula da ita daga kanka ba"
"Au haka ma zaki ce?"
"Eh na fada din,dame kakeso naji ne iye?"
"To mariya nidai tsakanina dake saidai nace Allah ya isa ban yafe ba..." Cikin qaraji gana zubda hawaye tace
"Nima Allah...." Qarar da shahida ta saki ita ta katse sauran magabar da umman tata taso furtawa,kuka take sosai hawaye wani yana bin wani
"Ku dainawa juna Allah ya isa kune sila....dukanku ku kuka zama silar koma meye na koma a yau...ku ku kaini ga afkawa halin da nake ciki a yau,wannan abun da kukeyi shiya janyo komai,duk d'a na halak bazaiso yaga rana guda tak data zama ranar da mahaifansa sukai cecekuce ko jayayya ba a gabanshi,sai gashi ni nawa mahaifan a gabana suke xagin juna,a gabana suke aibata juna,a gabana suke debewa juna albarka,a gabana suke fada da junansu,duk yadda naso da ganin gyaruwar al'amarin hakan ya gaza,duk habyar da nabi ta ganin kun gyaru ba wadda ta bulle min,zafi da radadin haka yasa na nemowa kaina gurbatacciyar mafita,nake shan abinda ni a nawa tunanin bacci kawai zao sanyi ni,ban sani ba cewa ya shiga cikin abinda annabi ya haramta tunda zai gusar da hankali,zai saka maye,idan zanyi kuka bazanyi da d'aya saga cikinku ba,zanyi kuka ne sa dukkaninku,kun kasa fahimtata a sansa ya dace,kun kasa gane illar abinda kuke aikatawa a gabamu mu 'ya'yanku"daga haka ta miqe ta miqe jiri da kuma rashin qwarin jiki ya sanya ta dinga layi,amma bata dakata ba har sai data fice daga dakin zuwa nata dakin.
Dukkaninsu sai jikinsu yayi sanyi,kowannensu ya shiga nazari da dogon tunani,bai sake cewa komai ba abban ya fice daga dakin,saiya zura takalmansa ma da niyyar ficewa daga gidan gaba daya.
Yana sanya qafarsa a waje yaci karo da mutum uku cikin maqotansa
"Yauwa malam nuraini...dama yanzu muke neman yaron da zai mana sallama dakai" qoqarin dai daita fuskarshi yayi ya basu hannu suka gaisa
"Ashe haka abu ya faru?,wallahi sam bamuji dadi ba,yarinyar da kowa ke mata kallon hankali da nutsuwa" daya daga cikin maqotan nashi da ake kira da malam sallau ya fada
"Wallahi kuwa malam sallau,amma nidai ina kyautata zaton sharrin qawaye ne tunda kowa ya shaidi nutsuwar yarinyar....amma cire ciki aiba qaramin abu bane,sanda haruna ke gayan qaryatashi nayi saida yatabbatar min da kunnensa yaji saurayin yana fada" a hautsine abban shahida ya dago yana musu wani bahagon kallo,kusan bai fahimci me suke fada ba gaba daya
"Yata shahida ce tayi ciki harta cire?" Sai suka koma kallon kallo tsakaninsu,malam sallau ya dubi abban
"Errrhmmm malam nuraini kodai mata sun maka irin halin nasu ne an boye maka bakasa me yake faruwa cikin gidanka ba?,banda haka wannan zancan ai ya karade unguwarnan daga daren jiya zuwa safiyar yau"
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un" ya dinga maimaitawa yana dafe da kanshi,me yayi jama'ar unguwarsu haka sa cikin qanqanin lokaci zasu jefi diyar cikinsa da wannan sharrin,kansa ya dafe da yaji ya soma juya mishi sai kawai ya juya zuwa cikin gida
"Allah ya tsare gaba ya kiyaye" ya juyo malam sallau yana fada cikin daga murya,dai dai sanda shahida data fito don shiga bayi ta kama ruwa ta saki butar hannunta cikin tsananin tashin hankali ta koma dakinta,dukka jikinta rawa yake,tana tariyar kalaman da saurayin ya dinga fada bayan ya saketa a qofar gidan,kenan duk abinda ya fada sun yarda dashi?,kenan yanzu kallon da kowa zai dinga mata?,innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,Allahumma ajirni fi musibati wa akhlifni khairan minha"shine abinda ta dinga maimaitawa kenan.
Cikin kwana biyu kacal ta rame ta fige ta fita a hayyacinta,bata taba tunanin akwai tashin hankalin daya wuce na fadan iyayenta ba saiga wanda ya ninkashi ya risketa,duk ta silar kaucewa wancan bacin ran ashe zata fada wanda yafi wancan tsanani rusa farinciki dama ruguza rayuwa gaba daya.
Ba ita kadaiba gidanma gaba daya ya zama shuru,baya ga abinda ya faru abbanta ya kwanta ciwo sosai tun randa su sallau sukazo masa jaje,wanda ba komai bane ya taba ranshi irin maganar da suka furta,qarshe da aka aunashi jininsa ne yayi mugun hawa,hakan ya saga hankalin ummanta itama ta shiga wani sabon tashin hankalin da firgici.
Kwana uku amma shahidar jinta take akwai ya babu,gata nan dai kawai amma komai ya fice mata aka,ranar kwana na ukun da yammaci wani yaro yayi sallama tsakar gidan nasu dauke da takarda wanda yace gashi a baiwa shahidan.
Mubina ce ta bita har cikin daki a sannan tana kwance saman abun sallah ta miqa mata,saita saka hannu kawai ta amsa ta aje saman kanta tana ci gaba da lazuminta,wanda kusa fiye da rabi istigfari take da salatin annabi.
Sai data idar sannan ta dauko envalope din,tana daga kwance ta farketa,takarda ce qwaya daya a cikinta ta fado,sai wata azurfarta guda biyu data siya ta baiwa anwar ajiya,da sauri tasoma warware takardar tana zumudin jin daga gareshi,don tunda abun ya faru taji dif daga bangarensa,tana zaton wala'alla yazo ance mishi bata da lafiya,don bata da maraba da mai lalurar,ita kuma wani kunya da nauyin kiranshi take,gani take kaman daga muryarta zai karanci komai,zai karanci halin data fada,wasiqace cikin rubutun anwar din mai tsari
_Basai nayi miki sallama ba don baki cancanceta ba,saqo nake son isar miki dama ba wani mai tsaho ko yawa ba,shahida,sam baki dace dani ba,kuma sam bakiyi dai dai da rayuwata ba,tuntuni ina zaune dake ne kawai don bani da abinyi kuma bani da wata qwaqwaqwarar sana'a,gashi ina da buqatar macen da zan di ga rage dare a wajenta,to zuwa yanzu al'amura son suma yimin kyau,bana jin zan iya ci gaba da zama dake,ki sani ni muhammad anwar ban taba sonki ko qaunarki ba,na miki alfarma ne kawai a baya,kuma ki saka a ranki cewa baki taba soyayya da wani mai kama dani ko suna na bar har qarshen rayuwarki,wasiqar na tafe da guzurin sabuwar masoyiyita wadda nake da tabbacin ta fiki komai,idan nace komai ina nufin komai da komai da kikasan diya mace na mallaka_
Cikin rawar jiki ta miqe zaune dungurgur,sannan ta jawo envalope din ta sake lalubawa ciki,saiga hotuna guda shida rigis sun fado,dukkaninsu anwar ne cikin hotunan da wata matashiyar budurwa cikin kyakkyawar shiga ta alfarma,kana musu kallon farko zaka tabbatarwa kanka lallai masoya ne da sukayi zurfin cikin qaunar juna,saboda yadda kowanne ke kallon danuwanshi cikin fara'a da shauqi,sosai ta tsurawa fuskar yarinyar ido zuciyarta na wani qara gudu tamkar zata faso qirjinta,suya zuciyar tata take mata tanason yin kuka amma bataji koda alamarsa ba bare yazo,nazarin fuskar yarinyar take take ta tuno inda ta santa,ranar bikin umaima,ranar bikin umma zaune gaban motar daya amso don ya kaita ya daukota,saita saki hoton tana girgiza kai tare da laluben wayarta duka lokaci daya,tamkar tababba take zancan a fili ita kadai
"Nasan wasa kake min ya anwar ba zamu taba rabuwa....nasan wani ya kaima labarin abinda ya faru dani,ranka ya baci ka furta min wannan kalaman saboda kishina da kake" maganar tata ta katse sanda wayar ta shiga ta soma ringing.
"Ina kika barmin 'yata taje mariya?"
"Ina kuwa zan barta taje abba?,gaisuwar mutuwa suka je ita da qawarta" ta fada cikin tsananin tashin hankali da kuma kuka
"Wallahi wallahi ki tabbatar da cewa indai wani mummunan abu ya samu 'yata toki kuka da kanki" ya fada cikin hargagi yana nunata da yatsa,a ranar dai umma babu bakin magana ta diyarta take,salati kawai take tana duba jikin shahida daya lalace da jini,bandaki ta kaita tayi mata wanka wanda shiya sanya bacci ya kwasheta bayan ta dawo da ita daki.
🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍🎍
Da salati ta farka tana qarewa dakin kallo,ko ba'a fada ba tasan dakin ummanta ne,a hankali ta soma tuna me ya faru da ita,tun daga barinsu inda sukaje zuwa gidan qawar fiddausi,sauketa da saurayin yayi a qofar gidansu,daga nan zaren tunanin nata ya yanke,tayi tayi ta sake tuno abinda ya faru ta kasa,zuciyarta na gaya mata taga anwar,wata zuciyar tana ce mata bashi bane.
Muryar umma ta jiyo tana kiranta cikin kakkausar murya wadda tasa hanjin cikinta kadawa
"Shahida....ina kikaje jiya?" Saita kasa amsa mata,indai har a wannan yanayin ta shigo gidansu to tabbas bata da bakin kare kanta,kafin ta sake cewa wani abu umman ta zube dukka kwalaben da suka fado a jakarta wanda tuni ta gama karantawa ta kuma fahimci kayan shaye shaye ne a ciki,idanun umman jajur tace mata
"Meye wannan shahida?" Kasa hada ido tayi da umman,hankalinta yayi qololuwar tashi,lafiyayyen mari umman ta sauke mata wanda ya gigitata,sannan yayi dai dai da shigowar abbanta dakin,wanda tunda ya fita sallar asuba daya daga cikin maqotansa ya masa jajen anga shahida an kawota qofar gida an yasar me ya sameta bai sake samun sukuni ba,yasan tabbas maganar akayita tattaunawa a jiya ana kuma sauya mata kamanni,yasan halin anguwar da 'yan unguwar kaf.
"Ai kibar dukanta bari na gaya miki mariya,koma meye shahida ta zama laifinki ne,kin zaki baki kin kasa bawa diyata tarbiyya shine yanzu zaki zo kina wani hargagin banza da wofi?" Cikin bacin rai da shiga zafi biyu ta maida masa amsa
"Indai shahida ta lalace ne kaima akwai laifinka,tunda kaima ubane ai ba'a dauke nauyin haqqin kula da ita daga kanka ba"
"Au haka ma zaki ce?"
"Eh na fada din,dame kakeso naji ne iye?"
"To mariya nidai tsakanina dake saidai nace Allah ya isa ban yafe ba..." Cikin qaraji gana zubda hawaye tace
"Nima Allah...." Qarar da shahida ta saki ita ta katse sauran magabar da umman tata taso furtawa,kuka take sosai hawaye wani yana bin wani
"Ku dainawa juna Allah ya isa kune sila....dukanku ku kuka zama silar koma meye na koma a yau...ku ku kaini ga afkawa halin da nake ciki a yau,wannan abun da kukeyi shiya janyo komai,duk d'a na halak bazaiso yaga rana guda tak data zama ranar da mahaifansa sukai cecekuce ko jayayya ba a gabanshi,sai gashi ni nawa mahaifan a gabana suke xagin juna,a gabana suke aibata juna,a gabana suke debewa juna albarka,a gabana suke fada da junansu,duk yadda naso da ganin gyaruwar al'amarin hakan ya gaza,duk habyar da nabi ta ganin kun gyaru ba wadda ta bulle min,zafi da radadin haka yasa na nemowa kaina gurbatacciyar mafita,nake shan abinda ni a nawa tunanin bacci kawai zao sanyi ni,ban sani ba cewa ya shiga cikin abinda annabi ya haramta tunda zai gusar da hankali,zai saka maye,idan zanyi kuka bazanyi da d'aya saga cikinku ba,zanyi kuka ne sa dukkaninku,kun kasa fahimtata a sansa ya dace,kun kasa gane illar abinda kuke aikatawa a gabamu mu 'ya'yanku"daga haka ta miqe ta miqe jiri da kuma rashin qwarin jiki ya sanya ta dinga layi,amma bata dakata ba har sai data fice daga dakin zuwa nata dakin.
Dukkaninsu sai jikinsu yayi sanyi,kowannensu ya shiga nazari da dogon tunani,bai sake cewa komai ba abban ya fice daga dakin,saiya zura takalmansa ma da niyyar ficewa daga gidan gaba daya.
Yana sanya qafarsa a waje yaci karo da mutum uku cikin maqotansa
"Yauwa malam nuraini...dama yanzu muke neman yaron da zai mana sallama dakai" qoqarin dai daita fuskarshi yayi ya basu hannu suka gaisa
"Ashe haka abu ya faru?,wallahi sam bamuji dadi ba,yarinyar da kowa ke mata kallon hankali da nutsuwa" daya daga cikin maqotan nashi da ake kira da malam sallau ya fada
"Wallahi kuwa malam sallau,amma nidai ina kyautata zaton sharrin qawaye ne tunda kowa ya shaidi nutsuwar yarinyar....amma cire ciki aiba qaramin abu bane,sanda haruna ke gayan qaryatashi nayi saida yatabbatar min da kunnensa yaji saurayin yana fada" a hautsine abban shahida ya dago yana musu wani bahagon kallo,kusan bai fahimci me suke fada ba gaba daya
"Yata shahida ce tayi ciki harta cire?" Sai suka koma kallon kallo tsakaninsu,malam sallau ya dubi abban
"Errrhmmm malam nuraini kodai mata sun maka irin halin nasu ne an boye maka bakasa me yake faruwa cikin gidanka ba?,banda haka wannan zancan ai ya karade unguwarnan daga daren jiya zuwa safiyar yau"
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un" ya dinga maimaitawa yana dafe da kanshi,me yayi jama'ar unguwarsu haka sa cikin qanqanin lokaci zasu jefi diyar cikinsa da wannan sharrin,kansa ya dafe da yaji ya soma juya mishi sai kawai ya juya zuwa cikin gida
"Allah ya tsare gaba ya kiyaye" ya juyo malam sallau yana fada cikin daga murya,dai dai sanda shahida data fito don shiga bayi ta kama ruwa ta saki butar hannunta cikin tsananin tashin hankali ta koma dakinta,dukka jikinta rawa yake,tana tariyar kalaman da saurayin ya dinga fada bayan ya saketa a qofar gidan,kenan duk abinda ya fada sun yarda dashi?,kenan yanzu kallon da kowa zai dinga mata?,innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,Allahumma ajirni fi musibati wa akhlifni khairan minha"shine abinda ta dinga maimaitawa kenan.
Cikin kwana biyu kacal ta rame ta fige ta fita a hayyacinta,bata taba tunanin akwai tashin hankalin daya wuce na fadan iyayenta ba saiga wanda ya ninkashi ya risketa,duk ta silar kaucewa wancan bacin ran ashe zata fada wanda yafi wancan tsanani rusa farinciki dama ruguza rayuwa gaba daya.
Ba ita kadaiba gidanma gaba daya ya zama shuru,baya ga abinda ya faru abbanta ya kwanta ciwo sosai tun randa su sallau sukazo masa jaje,wanda ba komai bane ya taba ranshi irin maganar da suka furta,qarshe da aka aunashi jininsa ne yayi mugun hawa,hakan ya saga hankalin ummanta itama ta shiga wani sabon tashin hankalin da firgici.
Kwana uku amma shahidar jinta take akwai ya babu,gata nan dai kawai amma komai ya fice mata aka,ranar kwana na ukun da yammaci wani yaro yayi sallama tsakar gidan nasu dauke da takarda wanda yace gashi a baiwa shahidan.
Mubina ce ta bita har cikin daki a sannan tana kwance saman abun sallah ta miqa mata,saita saka hannu kawai ta amsa ta aje saman kanta tana ci gaba da lazuminta,wanda kusa fiye da rabi istigfari take da salatin annabi.
Sai data idar sannan ta dauko envalope din,tana daga kwance ta farketa,takarda ce qwaya daya a cikinta ta fado,sai wata azurfarta guda biyu data siya ta baiwa anwar ajiya,da sauri tasoma warware takardar tana zumudin jin daga gareshi,don tunda abun ya faru taji dif daga bangarensa,tana zaton wala'alla yazo ance mishi bata da lafiya,don bata da maraba da mai lalurar,ita kuma wani kunya da nauyin kiranshi take,gani take kaman daga muryarta zai karanci komai,zai karanci halin data fada,wasiqace cikin rubutun anwar din mai tsari
_Basai nayi miki sallama ba don baki cancanceta ba,saqo nake son isar miki dama ba wani mai tsaho ko yawa ba,shahida,sam baki dace dani ba,kuma sam bakiyi dai dai da rayuwata ba,tuntuni ina zaune dake ne kawai don bani da abinyi kuma bani da wata qwaqwaqwarar sana'a,gashi ina da buqatar macen da zan di ga rage dare a wajenta,to zuwa yanzu al'amura son suma yimin kyau,bana jin zan iya ci gaba da zama dake,ki sani ni muhammad anwar ban taba sonki ko qaunarki ba,na miki alfarma ne kawai a baya,kuma ki saka a ranki cewa baki taba soyayya da wani mai kama dani ko suna na bar har qarshen rayuwarki,wasiqar na tafe da guzurin sabuwar masoyiyita wadda nake da tabbacin ta fiki komai,idan nace komai ina nufin komai da komai da kikasan diya mace na mallaka_
Cikin rawar jiki ta miqe zaune dungurgur,sannan ta jawo envalope din ta sake lalubawa ciki,saiga hotuna guda shida rigis sun fado,dukkaninsu anwar ne cikin hotunan da wata matashiyar budurwa cikin kyakkyawar shiga ta alfarma,kana musu kallon farko zaka tabbatarwa kanka lallai masoya ne da sukayi zurfin cikin qaunar juna,saboda yadda kowanne ke kallon danuwanshi cikin fara'a da shauqi,sosai ta tsurawa fuskar yarinyar ido zuciyarta na wani qara gudu tamkar zata faso qirjinta,suya zuciyar tata take mata tanason yin kuka amma bataji koda alamarsa ba bare yazo,nazarin fuskar yarinyar take take ta tuno inda ta santa,ranar bikin umaima,ranar bikin umma zaune gaban motar daya amso don ya kaita ya daukota,saita saki hoton tana girgiza kai tare da laluben wayarta duka lokaci daya,tamkar tababba take zancan a fili ita kadai
"Nasan wasa kake min ya anwar ba zamu taba rabuwa....nasan wani ya kaima labarin abinda ya faru dani,ranka ya baci ka furta min wannan kalaman saboda kishina da kake" maganar tata ta katse sanda wayar ta shiga ta soma ringing.