Sashe 62
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Turo qofar da aka sakeyi yasata daga kanta,shine dai ya sake dawowa dauke da wata roba dake fidda tururin ruwan zafi,hannunsa dayan riqe da towel,gabanta ya iso saitin qafar ya aje robar sannan ya jawo wani qaramin qawataccen stool dan gajere ya dora robar akai,bai kalleta ba ya kama qafar ya dora saman robar,zafi yasa ta saki 'yar qaramar qara zata riqe hannunsa sai kuma tayi saurin janyewa,tana ji ya dinga tsoma towel din yana matsewa gami da danna mata wurin,tun tana jin ciwo harya soma sake mata,radadin ya ragu,tunda ya soma aikin bai daga kai ya dubeta ba,lokaci lokaci idanunta kan fada kansa ba tare data shirya ba,amma ko sau daya taci sa'a basu hada ido ba,tsahon mintuna sannan ya miqe ya dauki towel da robar ya fice dasu.
Sake gwada miqewar tayi wannan karon saita dan taku,a daddafe ta samu ta tura qofar da zata sadaka da falonshi don dakinta takeson tafiya,sam bata qaunar zaman dakin nasa,a bakin qofar falon wadda zata sadaka da matattakalar benan suka kusa karo yana dawowa tana shirin sauka,fuskarnan a tsuke kaman baisan meye dariya ba yace
"Ina zaki haka?"
"Inda nafi wayo" ta amsashi tana duban ta inda zata rabashi ta wuce
"Koma ba inda zaki,kin dawo nan kenan harsai kin gane kece matar nice mijin,don na fuskanci baki banbance tazarar dake tsakaninmu ba" wani kallonsa tayi
"Ba inda zan koma,dakina xan koma" girarshi ya dage
"Ashe?,tunda kin yarda dakinki ne can ashe nine mai gidan ko?"
"Oho?" Tace tana juya masa baya gami da turo baki,anwar din yakai mata ko ina,ya soma quret,ta fuskanci duk abinda zaiyi ya qureta ya iya,saita soma qoqarin rabeshi,qyaleta yayi harsai data raba tsakiyarsa sannan ya cukukikuyeta gaba daya cikin qirjinsa ya mata wani kyakkyawan ruqo,karon farko shida ita a rayuwarsu,ihu ta saki kaman wadda taga abun tsoro tana qoqarin qwacewa,daukarta yayi cak kamar yadda ya saba mata,abinda tafi tsana kenan,saboda idan yayi hakan gani take kaman ya raina mata wayo,bai sauketa ko ina ba bandaki,ya ajeta saman toilet sit,ta bude baki zatayi magana yasa yatsa ya dalle mata bakin gami da cewa
"Shshshs,karki sake ki mana surutu a bandaki" yana maganar yana zaro ido kaman wanda yakewa qaramin yaro,bacin rai ya hanata magana,saita qyaleshi tana kallonsa ya daura mata alwalar,zai sake sungumota ya fito da ita ta zille,ta tashi tana dingisawa ta fito,fafur taqi zama a bedroom dinsa sai a falo,a nan tayi sallarta.
Daidai sanda ta idar wayarta tayi tsuwwa,lokaci daya idanunsu suka sauka kan jakar,ya rigata saka hannu ya dauki jakar ya zuge ya ciro wayar,zai daga ta dubeshi
"Karka daga min waya,bani abata" fuska a tsuke ya daga kai daga daga wayar da yayi niyya yi
"Saboda baki da gaskiya?" Saita ware ido tana kallonshi
"Eh bani da gaskiyar,duk abinda zakace kace,ka fadima abinda yafi hakan idan kaso,bakinka rayuwarka kuma zuciyarka ba tawa ba" ta qarashe cikin hasala,yana tsaye cak yana kallonta saiya saki murmushi ya dauke idanunsa daga kanta
"Ko baki fada ba dama ai haka yake,dama ai zuciyata ce ba taki ba,haka rayuwata vata taba zama taki ba ki rubuta ki aje" daga haka ya daga wayar ya kara a kunnesa,hakanan taji kalaman sun samata ciwo,saita jefa masa harara ta dauke kanta wani sashe daban
"Lpy qalau....eh,to" kawai taji ya fada ya latse wayar,yana shirin maidata wayar jakar aka sake kira
"Triple R company" ya furta a fili,ta waiwayo da sauri ta dubeshi,da alama kira ne daga kamfaninsu,saita samu kanta tana addu'ar Allah yasa ba daga cikin maza abokan aikinta bane,bata gama wannan tunanin ba tajishi yana bada amsa
"Maigidanta zaishigo ya samu boss dinku,zamuyi magana dashi" daga haka itama ya yanke wayar,tana kallo ya juya wajen da layi yake ya ciroshi,ya fidda layin saiya soma lanqwasashi
"Karka karyamin layina" ta fada cikin hanzari,saidai ina tuni ya karyashin ya watsashi cikin dan qaramin abun sharar dake kusa dasu sannan ya dubeta
"Namiji ne ya kiraki yana tambayar ba'asin rashin zuwanki aiki yau,baisan kina da aure ba?,ko baya ga haka dole ki rabu da wannan layin,bazan lamunci kici gaba da amfani dashi ba" ya qureta matuqa ta kasa daure bacin ranta ya bayyana muraran
"Wai me ya dameka da rayuwata ne?,ina ruwanka dani?,me yasa kakeson shishshigema rayuwata bayan ni bayan ni gana shigewa taka?,bayan ni ban damu da taka rayuwar ba?,me na tsare maka?,ohk....alwashinka kakeson ka cimma ko na quntatawa rayuwata shine kake aiwatarwa yanzu?" Tsaf ya xuba ido yana kallonta ba tare daya motsa ko yace wani abu ba,mamaki take bashi idan tana masifa wanda ko iyawa ma batayi ba,batasan me yake ji cikin zuciyarsa bane,batasan wanne hali yaje ciki ba,da yana da ikon maida bara bana daya dawo da ita ya goge dukkan wani tabo da aibu,ba zata fahimci komai ba,ba zata gane komai ba,tanata amfani da zahiri ne ba tare data binciki me badinin ta haifar ba,saiya saki hannuwansa kawai gami da fidda qaramin murmushi,indai ba tunzurata yayi ba bazai taba jin muryarta ba,idan bai tunzurata ba yasan halinta sarai ba zata taba yin magana dashi ba ko zasu shekare a haka,yasan halinta tsaf,baijin baya ga mahaifanta akwai wanda yasan halinta sama dashi
"Donke baki damu da rayuwata ba saime?,akwai dubbai da suka damu da ita,don na taimakeki ma na rabi rayuwar taki shine kike wani zaqalqalewa kina zaton ke watace a wajena?" Ido da baki duka ta saka tana son tantance me yake cewa,daidai lokacin da qararrwar dake nuna akwai baqi can falon qasa ta soma kadawa,saiya miqe kawai yana tabe mata baki ya fice ya sauka qasa.
Daada ce ita da mubina da khadija,su sukayi waya dazu kan zasu rakota,tun bikin daada bata koma ba umma tace saitayi sati uku,sai yanzu ta soma shirin komawa,zuwanshi gidan wajen daada hira babu adadi,ta fuskanci abubuwa da dama game da zamansu ba tare daya gaya mata ba,da batayi niyyar zuwa gidan ba sam,amma taga ya kamata ta danyi gyara ko yaya ne kafin ta wuce karta tafi tabar baya da qura,don tasan umman shahidan koda wasa ba zata taba taka gidan shahida a yanzu ba,donko hira ake bata sanya baki,yaji qishin qishin din zata zo din yau dalili kenan dayasa ya tsare shahidan a sama don kar daada ta ramfo komai,don hausawa sunce babba babba ne,abinda zai gano ko kahau bishiyar rimi ba zaka hangoshi ba.
Shi ya tarbesu daada tahau baza ido
"Ina ita waccar ja'irar,kaine kake tarar baqin ita kuma tana me?" Murmushi ya saki
"A'ah a'ah,kawai yaune na karbata,tana sama batajin dadi ne,ta samu targade a qafarta"
"To ce mata ta sauko,don tayi targade saboda tsabar son jiki shine zata hau sama ta nade?,oh ni habiba,yaran yanzu saidai abarsu,kamar wadda ta karye"
"Yi haquri daada karki rudamin mata,kin manta ke mai laifi ce dama?" Ya fada cikin tsokana,da ido ta bishi baki sake
"Iyeeee....au wato harka soma bin bayan matarka?" Murmushi ya saki sosai sannan yace
"Yi haquri daadarmu,so so ne amma aisonkai yafi ko?" Kasa amsashi tayi,cikin zuciyarta tanajin sanyi da dadi na yadda ta fuskanci.yana kulawa da jikarta,ta cika da fata da addu'ar Allah yasa itama haka take masa kada ta basu kunya,kada kuma ta watsa musu qasa a ido,mubina yasa ta shiga kitchen ta hada musu abin motsa baki,sai dayaga ta shirya musu komai sannan ya zqri muqulli don zuwa ya sama musu abinci
"Ku hau saman daada ku sameta kafin na dawo"
"Kaga nifa ba zama zanyi ba,mai motar daya kawomu ma yana qofar gida yana jira in fito ya maidani,don yau ni kam kwanan garinmu zanyi" qememe taqi barinshi ya fita,tace saidai yahau sama ya sauko mata da shahida
"Kiyi haquri daada ki hau,ba zata iya saukowa ba"
"Ita sabon qashima taqi saukowa bare ni tsohon qashi za'ace nayi tattaki nahau,tunda goya mata baya kake tayita narkewa kaga tafiyarmu" daqyar ya lallaba daadan tahau saman,inda mubina da khadija sukayi xamansu nan falon suna kallo.
Har yanzu tana zaune saman abun sallah a haka daada ta shigo,sai taji dadin zuwan daadan,tana ganin tazo a daidai,ita ta qulla komai saboda haka dole ta yiwa anwar magana ya barta ta koma bakin aikinta,ba yabi ba fallasa ta gaidata,ta amsa tana qare mata kallo,bawani sauyi data gani tattare da shahidan na mace me aure,saita tabe baki,zata fara magana shahidan ta rigata cikin sautin wanda keson fashewa da kuka
"Daada ki masa magana ya barni na koma aikina,kinga tun asali da aikina ya ganni,sannan kuma baice min bazanyi ba sai jiya da nake gaya masa zan koma yace waina gama aiki,daxun nan kan ku shigo ya dauki wayata ya ballamin layina waina daina amfani dashi" rashin sani yafi dare duhu,wani kallo daadan ke mata akaikaice,sai data gama tsaf sannan tace
"Yo ai ni banga wani abun azo a gani dakika tabuka ba daxai nuna kinsan ma kina da aure,daga ke harshi banga wani sauyi tattare daku ba"
"Kai anwaru" ta kira sunanshi tana zare ido,ya amsa mata ta masa nuni da kusa da shahida
"Xauna nan" ba musu ya zauna yana qunshe dariya,daada sarkin rigimammu,da alama akwai magana a bakinta
"Tunda kuka tare ta taba maka kwanan turaka?" Ta jeho masa tambayar kanta tsaye,take qwaqwalwarsa ta gaya masa abinda take nufi,kunya ta rugo ta rarumeshi,bai taba tunanin tambayar da zata masa kenan ba,cikin hanzari yace
"Daada ai....
"Aime?,idan baka da amsa to bari na amsa maka,bata taba ba,kalli qafafunta da wuyanta,idan tace ma eh to qarya take,oh la'ilaha illallahu muhammadarasulillahi sallallahu alaihi wasallam" ta debo salati tana tafa hannuwa
_afwa masu karatu,kunsan yadda sabgogi ke kutso kai cikin rayuwa_🙏🏽 *Alqawarin Allah*
39
"Karki kuskura ki fita" ya fada yana daga tsayen yana dubanta,kamarma bada ita yake ba haka taci gaba da takawa.
Sake gwada miqewar tayi wannan karon saita dan taku,a daddafe ta samu ta tura qofar da zata sadaka da falonshi don dakinta takeson tafiya,sam bata qaunar zaman dakin nasa,a bakin qofar falon wadda zata sadaka da matattakalar benan suka kusa karo yana dawowa tana shirin sauka,fuskarnan a tsuke kaman baisan meye dariya ba yace
"Ina zaki haka?"
"Inda nafi wayo" ta amsashi tana duban ta inda zata rabashi ta wuce
"Koma ba inda zaki,kin dawo nan kenan harsai kin gane kece matar nice mijin,don na fuskanci baki banbance tazarar dake tsakaninmu ba" wani kallonsa tayi
"Ba inda zan koma,dakina xan koma" girarshi ya dage
"Ashe?,tunda kin yarda dakinki ne can ashe nine mai gidan ko?"
"Oho?" Tace tana juya masa baya gami da turo baki,anwar din yakai mata ko ina,ya soma quret,ta fuskanci duk abinda zaiyi ya qureta ya iya,saita soma qoqarin rabeshi,qyaleta yayi harsai data raba tsakiyarsa sannan ya cukukikuyeta gaba daya cikin qirjinsa ya mata wani kyakkyawan ruqo,karon farko shida ita a rayuwarsu,ihu ta saki kaman wadda taga abun tsoro tana qoqarin qwacewa,daukarta yayi cak kamar yadda ya saba mata,abinda tafi tsana kenan,saboda idan yayi hakan gani take kaman ya raina mata wayo,bai sauketa ko ina ba bandaki,ya ajeta saman toilet sit,ta bude baki zatayi magana yasa yatsa ya dalle mata bakin gami da cewa
"Shshshs,karki sake ki mana surutu a bandaki" yana maganar yana zaro ido kaman wanda yakewa qaramin yaro,bacin rai ya hanata magana,saita qyaleshi tana kallonsa ya daura mata alwalar,zai sake sungumota ya fito da ita ta zille,ta tashi tana dingisawa ta fito,fafur taqi zama a bedroom dinsa sai a falo,a nan tayi sallarta.
Daidai sanda ta idar wayarta tayi tsuwwa,lokaci daya idanunsu suka sauka kan jakar,ya rigata saka hannu ya dauki jakar ya zuge ya ciro wayar,zai daga ta dubeshi
"Karka daga min waya,bani abata" fuska a tsuke ya daga kai daga daga wayar da yayi niyya yi
"Saboda baki da gaskiya?" Saita ware ido tana kallonshi
"Eh bani da gaskiyar,duk abinda zakace kace,ka fadima abinda yafi hakan idan kaso,bakinka rayuwarka kuma zuciyarka ba tawa ba" ta qarashe cikin hasala,yana tsaye cak yana kallonta saiya saki murmushi ya dauke idanunsa daga kanta
"Ko baki fada ba dama ai haka yake,dama ai zuciyata ce ba taki ba,haka rayuwata vata taba zama taki ba ki rubuta ki aje" daga haka ya daga wayar ya kara a kunnesa,hakanan taji kalaman sun samata ciwo,saita jefa masa harara ta dauke kanta wani sashe daban
"Lpy qalau....eh,to" kawai taji ya fada ya latse wayar,yana shirin maidata wayar jakar aka sake kira
"Triple R company" ya furta a fili,ta waiwayo da sauri ta dubeshi,da alama kira ne daga kamfaninsu,saita samu kanta tana addu'ar Allah yasa ba daga cikin maza abokan aikinta bane,bata gama wannan tunanin ba tajishi yana bada amsa
"Maigidanta zaishigo ya samu boss dinku,zamuyi magana dashi" daga haka itama ya yanke wayar,tana kallo ya juya wajen da layi yake ya ciroshi,ya fidda layin saiya soma lanqwasashi
"Karka karyamin layina" ta fada cikin hanzari,saidai ina tuni ya karyashin ya watsashi cikin dan qaramin abun sharar dake kusa dasu sannan ya dubeta
"Namiji ne ya kiraki yana tambayar ba'asin rashin zuwanki aiki yau,baisan kina da aure ba?,ko baya ga haka dole ki rabu da wannan layin,bazan lamunci kici gaba da amfani dashi ba" ya qureta matuqa ta kasa daure bacin ranta ya bayyana muraran
"Wai me ya dameka da rayuwata ne?,ina ruwanka dani?,me yasa kakeson shishshigema rayuwata bayan ni bayan ni gana shigewa taka?,bayan ni ban damu da taka rayuwar ba?,me na tsare maka?,ohk....alwashinka kakeson ka cimma ko na quntatawa rayuwata shine kake aiwatarwa yanzu?" Tsaf ya xuba ido yana kallonta ba tare daya motsa ko yace wani abu ba,mamaki take bashi idan tana masifa wanda ko iyawa ma batayi ba,batasan me yake ji cikin zuciyarsa bane,batasan wanne hali yaje ciki ba,da yana da ikon maida bara bana daya dawo da ita ya goge dukkan wani tabo da aibu,ba zata fahimci komai ba,ba zata gane komai ba,tanata amfani da zahiri ne ba tare data binciki me badinin ta haifar ba,saiya saki hannuwansa kawai gami da fidda qaramin murmushi,indai ba tunzurata yayi ba bazai taba jin muryarta ba,idan bai tunzurata ba yasan halinta sarai ba zata taba yin magana dashi ba ko zasu shekare a haka,yasan halinta tsaf,baijin baya ga mahaifanta akwai wanda yasan halinta sama dashi
"Donke baki damu da rayuwata ba saime?,akwai dubbai da suka damu da ita,don na taimakeki ma na rabi rayuwar taki shine kike wani zaqalqalewa kina zaton ke watace a wajena?" Ido da baki duka ta saka tana son tantance me yake cewa,daidai lokacin da qararrwar dake nuna akwai baqi can falon qasa ta soma kadawa,saiya miqe kawai yana tabe mata baki ya fice ya sauka qasa.
Daada ce ita da mubina da khadija,su sukayi waya dazu kan zasu rakota,tun bikin daada bata koma ba umma tace saitayi sati uku,sai yanzu ta soma shirin komawa,zuwanshi gidan wajen daada hira babu adadi,ta fuskanci abubuwa da dama game da zamansu ba tare daya gaya mata ba,da batayi niyyar zuwa gidan ba sam,amma taga ya kamata ta danyi gyara ko yaya ne kafin ta wuce karta tafi tabar baya da qura,don tasan umman shahidan koda wasa ba zata taba taka gidan shahida a yanzu ba,donko hira ake bata sanya baki,yaji qishin qishin din zata zo din yau dalili kenan dayasa ya tsare shahidan a sama don kar daada ta ramfo komai,don hausawa sunce babba babba ne,abinda zai gano ko kahau bishiyar rimi ba zaka hangoshi ba.
Shi ya tarbesu daada tahau baza ido
"Ina ita waccar ja'irar,kaine kake tarar baqin ita kuma tana me?" Murmushi ya saki
"A'ah a'ah,kawai yaune na karbata,tana sama batajin dadi ne,ta samu targade a qafarta"
"To ce mata ta sauko,don tayi targade saboda tsabar son jiki shine zata hau sama ta nade?,oh ni habiba,yaran yanzu saidai abarsu,kamar wadda ta karye"
"Yi haquri daada karki rudamin mata,kin manta ke mai laifi ce dama?" Ya fada cikin tsokana,da ido ta bishi baki sake
"Iyeeee....au wato harka soma bin bayan matarka?" Murmushi ya saki sosai sannan yace
"Yi haquri daadarmu,so so ne amma aisonkai yafi ko?" Kasa amsashi tayi,cikin zuciyarta tanajin sanyi da dadi na yadda ta fuskanci.yana kulawa da jikarta,ta cika da fata da addu'ar Allah yasa itama haka take masa kada ta basu kunya,kada kuma ta watsa musu qasa a ido,mubina yasa ta shiga kitchen ta hada musu abin motsa baki,sai dayaga ta shirya musu komai sannan ya zqri muqulli don zuwa ya sama musu abinci
"Ku hau saman daada ku sameta kafin na dawo"
"Kaga nifa ba zama zanyi ba,mai motar daya kawomu ma yana qofar gida yana jira in fito ya maidani,don yau ni kam kwanan garinmu zanyi" qememe taqi barinshi ya fita,tace saidai yahau sama ya sauko mata da shahida
"Kiyi haquri daada ki hau,ba zata iya saukowa ba"
"Ita sabon qashima taqi saukowa bare ni tsohon qashi za'ace nayi tattaki nahau,tunda goya mata baya kake tayita narkewa kaga tafiyarmu" daqyar ya lallaba daadan tahau saman,inda mubina da khadija sukayi xamansu nan falon suna kallo.
Har yanzu tana zaune saman abun sallah a haka daada ta shigo,sai taji dadin zuwan daadan,tana ganin tazo a daidai,ita ta qulla komai saboda haka dole ta yiwa anwar magana ya barta ta koma bakin aikinta,ba yabi ba fallasa ta gaidata,ta amsa tana qare mata kallo,bawani sauyi data gani tattare da shahidan na mace me aure,saita tabe baki,zata fara magana shahidan ta rigata cikin sautin wanda keson fashewa da kuka
"Daada ki masa magana ya barni na koma aikina,kinga tun asali da aikina ya ganni,sannan kuma baice min bazanyi ba sai jiya da nake gaya masa zan koma yace waina gama aiki,daxun nan kan ku shigo ya dauki wayata ya ballamin layina waina daina amfani dashi" rashin sani yafi dare duhu,wani kallo daadan ke mata akaikaice,sai data gama tsaf sannan tace
"Yo ai ni banga wani abun azo a gani dakika tabuka ba daxai nuna kinsan ma kina da aure,daga ke harshi banga wani sauyi tattare daku ba"
"Kai anwaru" ta kira sunanshi tana zare ido,ya amsa mata ta masa nuni da kusa da shahida
"Xauna nan" ba musu ya zauna yana qunshe dariya,daada sarkin rigimammu,da alama akwai magana a bakinta
"Tunda kuka tare ta taba maka kwanan turaka?" Ta jeho masa tambayar kanta tsaye,take qwaqwalwarsa ta gaya masa abinda take nufi,kunya ta rugo ta rarumeshi,bai taba tunanin tambayar da zata masa kenan ba,cikin hanzari yace
"Daada ai....
"Aime?,idan baka da amsa to bari na amsa maka,bata taba ba,kalli qafafunta da wuyanta,idan tace ma eh to qarya take,oh la'ilaha illallahu muhammadarasulillahi sallallahu alaihi wasallam" ta debo salati tana tafa hannuwa
_afwa masu karatu,kunsan yadda sabgogi ke kutso kai cikin rayuwa_🙏🏽 *Alqawarin Allah*
39
"Karki kuskura ki fita" ya fada yana daga tsayen yana dubanta,kamarma bada ita yake ba haka taci gaba da takawa.