Sashe 44
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Qarfe sha biyu da minti arba'in da biyar tayi sallama falon daada,hasina 'yar gidan qanin abbanta ce zaune ta daga kai cikin mamaki da farinciki ta amsa sallamar
"Mutan kano,yau a gari?,ni har nayi fushi fa,wai shahida kizo har garin nan kwanaki amma ki kasa leqani,gaba daya kin watsar dani kaman wadda ta miki wani mugun laifi?" Murmushi shahida tayi tana zama kan daya daga cikin kujerun gami da cire mayafinta ta aje gefe,iskar fankar da aka qurewa gudu cikin falon tana kadata gami da shigarta tako ina sakamakon zafin da ake zabgawa da kuma uwar rana
"Kiyi haquri hasina,ba'a son raina ba wallahi,wannan tsohuwr ce ta min laifin daya shafeku,amma kiyi haquri zanzo in sha Allahu" cikin murmushi hasina ta tabe baki
"Kedai bansan me ya dameki ba,koda yake an auna arziqi da aka samu ma kika ci gaba da zuwa katsinar da kika yiwa yajin aiki wajen shekaru hudu" murmushin da baikai har zuci ba shahida tayi tana cire agogon hannunta
"Yanzun ma mawuyacine idan ban koma muku yajin aikin ba ai" ta qarshe fada wani abu na takore mata wuya idan ta tuna kasassabar dasu daada suka aikata mata,saidai takanji sassauci idan ta tuna tana da hope a yau,qasa qasa da murya hasina tayi
"Hala ta kusa kwatanta miki abinda taso yimin kenan?" Kallonta shahida take ba tare da tace komai ba tana son jin qarin bayani
"Wai in gaya miki matarnan daga zuwa mata hutu shikenan tasa aka mata kiran saurayina qafa da qafa wai ya kamata ya fito hakanan,wannan shekarar ta shirya aurar da jikokinta,wai basai ya dorawa kanshi wata dawainiya ba yayi abinda addini kawai yace masa ya wadatar Allah ya sawa auren albarka" tagumi da haba shahida tayi kawai tana jin wannan bayanin,ita kenan ta mata dakyau ma data amshi kudin aure,amma gwara hasina da ita sau dubu
"Hasina kukan dadi kike,kinsan me daada tayimin?" Kai ta girgixa tana duban shahida
"Kudin aurena da sadakina suka amsa gaba daya ba tare da na sani ba,kuma ba tare da nasan waye zan aura din ba,kawai don bincikensu ya basu managarcine suke ganin ya dace dani" idanu waje hasina ta fito dasu tana duban shahida,kafin tace wani abu suka jiyo maganar daada daga tsakar gida wadda ta fito da wanka ne tana fadin
"Da kika shigo kika bar akwatin naki rana na duka waye zai dauke miki" dole kowanne yaja bakinsa yayi shuru harta iso falon,saita kalli idanunsu na 'yan sakanni kana ta tabe baki
"Magulmatan banza da wofi" daga haka tayi wucewarta daki donta saka kaya,yayin da shahida cikin dacin rai da baqincikin daya taso mata ta fito tsakar gida ta shiga bandaki tayi fitsari sannan ta daura alwala nan bakin famfo ta shigo da akwatin nata.
Qarfe daya da minti ashirin na rana tana tashi daga saman abun sallarta wayarta ta dauki tsuwwa,hasina ta miqo mata ta duba,nuradden ke kira ko bai fada ba tasan ya iso ne,gabanta taji yayi mummunar faduwa ta daga idanunta ta kalli daada data qarawa fura da nono ruwa take sha,saita kalli hasina,suka hada idanu ta mata signa sannan ta fita tsakar gida,ba jimawa ta biyo bayanta,janta tayi bakin kitchen ta gaya mata abinda ke faruwa
"Tabdi,kina tunanin akwai abinda zai sauya dada?,amma arashin tayi akan bar arha,bari na gaya mata baqo zai shigo" ta juya tana komawa,kafin takai ga shiga falon yaro ya tamfatsa sallama yana rangada fadin wai ana sallama da shahida,daada dake zaune a rumfarta tayi katsu tana jiran taji wanda zaiyi magana cikinsu,shuru sukayi ba wadda ta amsa,sai daadan ta kira yaron ya qaraso bakin rumfar
"Waye yake sallama da ita?"
"Wani ne,wai nuradden daga kano"
"Kano?" Ta sake tambayar yaron,saiya kada kai alamun eh,shuru na sakanni sannan tace
"Jeka ce masa ya shigo" juyawa yaron yayi ya fice ita kuma ta kira shahida da hasina gaba daya
"Xauna nan" ta nunawa shahida gefanta,ba musu ta zauna jiki a sanyaye,ta dubi hasina
"Bude firinjin can ki ciro ruwa da lemo" ba musu hasinar tayi yadda tace,dada ta nuna mata shimfidar daddumar data gama salla akai bata kai ga daukewa ba tace ta dora saman nan.
Cikin minti biyu kacal nuradden ya bayyana cikin falon,yaci manyan kaya yanata qamshi,bashi kadai bane shida wani abokinsa ko kuma ince amininsa ne,duk da dan uwanshi ne,cikin girmamawa suka zauna saman shimfidar suna gaida daada,ta amsa musu kadaran kadaham,yayin da idanun nuradden ke kan shahida.
Tayin ruwa da lemon tayi musu,Sayyid abokinsa ya bude ya zuzzuba musu a kofi,kusan shi kadai yasha,yana sha suna dan taba jira jifa jifa da daada tana tambayarshi kano,kasancewar ta dauki shekaru masu dama rabonta da ita,tun kafin rasuwar babansu shahida.
Sai da suka kammala tasa hasina ta zuba musu abinci,saidai sunce a qoshe suke,tilas ta rufe ta maida kitchen din,shuru ne ya ratsa na dan wani lokaci sannan sayyid yace
"Am...daada,abinda yake tafe damu dama magana ce game da shahida da kuma abokina nura,duk da nasan bata sanar miki da zuwanmu ba"
"Haka yake" a nutse sayyid ya fayyacewa daada komai,tayi gyaran murya tana dubansu
"Nasan cewa kuna da labarin an bada shahidan harma an karbi sadakinta,idan ma ta boye maka bata gaya maka ba ni ya zama wajibi na gaya maka gaskiyar abinda ake ciki"
"Ta fadama bata boye ba daada"
"Yauwa...an riga da an karbi sadakin yaron,kuma a shekarun da Allah ya bamu bai kamata kuma ace muna magana biyu ba,uwa uba sanin kanka ne cewa haramunne neman aure akan nema,koda ciniki akan ciniki ne haramun ne bare nema kan nema,matar mutum kabarinsa,Allah ya qaddari haka tun farko shi yasa ya hukunta jinkirin zuwanka garemu,saboda haka ina mai yaba maka bisa soyayyar daka nunawa jininmu,ina kuma mai maka fatan samun dacewa da wata matar data fita,sannan ina mai dorawa da baka haquri,kayi haquri,Allah ya sawa zuciyarka dangana" sayyid ne kawai ke amsawa da amin,yayin da gaba daya jikin nuradden ya mutu murus,zufa ta dinga yanko masa tako ina
"Mun gode sosai da karamcin da akayi mana" sayyid ya fada sanda suke miqewa bayan sun ajewa daada kudi
"A'ah yaro...nifa bazan karba ba,zoka dauka ku wuce Allah yayi maka zabi mafi alkhairi" qememe suka qi dauka haka suka fice,daada ta juya ta kalli shahida dake zaune gefanta tana sharbar qwalla
"Saikije ki sallamesu" daga haka ta miqe ta tayi wucewarta daki,sanda ta cimma qofar gidan tuni su nuradden sun wuce,sai tex daya turo mata na anjima zai kirata don yanzu baida nutsuwar tsaiwa,sulalewa tayi ta zauna gefan gadon,tana qoqarin hadiye kukanta.
Shigowar daada dakin ya sanyata daga kai tana kallonta,tana daga tsaye ta soma magana
"Kin kyauta sosai da kika sanyashi yazo kika toxarta mu,daa can kinsan yana sonki baki bashi dama ba har saida muka yanke hukunci a kanki?,ko kina tsammanin mu warware maganar da mukayi kaman qananun mutane?,to idan ma zaki kwantar da hankalinki ki nutsu waje guda shiya fiye miki alkhairi,ki shirya kuma ki dakaci zuwan gobe,mijinki da yardar Allah zaizo kuga juna,idan kinga dama kuma idan yazo din ki watsa mana qasa a idanu" daga haka daadan ta juya tayi ficewarta,sai kawai shahidan ta bita da kallo ranta na quntata,koma meye shi ya janyo mata,kuma shima saiyaji a jikinsa da zuciyarsa yadda ya janyo mata bacin rai tsakar rana ba tare data shiryawa hakan ba.
***** ****** ****** *****
Tunda ta tashi washegarin take kwance abinta kamar ruwa taqi yin komai,saidai daga nan ta koma can,hasina tayi tayi ta tashi tayi wani abun ko taji qwarin jikinta amma ta qeqashe qasa,ko kallo bata ishi daada ba sangar gabanta kawai take,tana daga kwancen tana kallon daada,yadda ta cika fridge dinta da fura da nono mai kyau,lemuka da kuma ruwa,tasa hasina tayi total na kayan fulawa aka siyo komai hasina tayi dan dai dai aka adana komai,baki ta tabe ta dauke kai bacin rai na cinta sanda daada ta fito da sabuwar daddumarta da kawu ummaru ya bata sanda ya dawo daga umara ya fesheta da turare ta baiwa hasina taje ta shimfida a dakin soro.
Saida komai ya kammala hasina ta isketa kwance cikin kujera tana saqa da warwara ta zauna gefanta
"Ya kamata ki tashi ko ruwa ko watsa kyaji dadin jikinki?" Idanunta da suka sake girma saboda kwana biyu data yi bata saka musu kwalli ba ta watsawa hasina cikin salon tambaya
"Me kikeson cewa?,kice kawai na tashi na yi masa kwalliya saboda zaizo,mutuncina ya qara zuba a idanunsa ko?" Murmushi hasina ta saki tana kada kai
"Niba haka nake nufi ba,kawai nasan yadda kikeson wanka wuni guda kuma ace tun safe ga azahar ta shiga baki watsa ruwa ba bare kici wani abun ai babu dadi,a qalla kodon tsaftar jikinki ko?" Saita maida kanta ta kwantar gami da rufe ido sannan ta amsa mata
"Share kawai" dubanta hasinan tayi na wasu mintunan sannan ta miqe tana cewa
"Allah ya kyauta,ya kamata dai ki sawa ranki salama,tunda kinsan cewa aikin gama ya gama,kada madai azo gaba kina jin kunya yazo kiga ya miki ki kamu da sonshi,kinsan wallahi daada ba raga miki zatayi ba"da sauri ta sake bude idon ta dubi hasina
"So,bakisan nayi bikin binneshi ba?" Dariya ta qwacewa hasina ta kama baki tana kallonta
"Shi kuma wannan da kika kawo fa?,mutunci kuke kenan?"
"Nuradden?..inason in rama halaccin da yayi minne shekaru kusan hudu"
"Tabdi,kice gwara da Allah yasa daada ta zaba miki miji,ashema ba soyayya kuke ba kenan" kofin dake gefanta shahida ta wafto ta jefi hasina dashi Allah yasa ta kauce bai sameta ba,har ga Allah taso ta sametan don bata da bakinma ce mata ta fita saboda wani abu dake takore da wuyanta
"Na rantse da Allah na tashi hasina saidai daada ta fiddaki daga gidan nan" cikin dariya ta fice tana cewa
"A'ah,a'ah,bani nakar zomon ba,ratayarma kuma ba'a bani ba".
Qarfe uku na rana da 'yan mintina daada ta shigo ta sameta
"Tashi kiyi wanka ko yanzu nasa akaimin ke bandaki na sabeki" ta furta tana nuna da gaske take,saida ta gama taurin kanta ganin da gaske daadan take sannan ta shiga bandaki tayi wankan.
Sanda ta fito mai kawai ta shafa sai turarenta oily data gogawa fatarta,tasaka wasu riga da skert na atamfa ta zura dogon hijabinta daya sauka har saman qafafunta ta soma da nafila kafin ta gabatar da farillar sallar la'asar.
"Mutan kano,yau a gari?,ni har nayi fushi fa,wai shahida kizo har garin nan kwanaki amma ki kasa leqani,gaba daya kin watsar dani kaman wadda ta miki wani mugun laifi?" Murmushi shahida tayi tana zama kan daya daga cikin kujerun gami da cire mayafinta ta aje gefe,iskar fankar da aka qurewa gudu cikin falon tana kadata gami da shigarta tako ina sakamakon zafin da ake zabgawa da kuma uwar rana
"Kiyi haquri hasina,ba'a son raina ba wallahi,wannan tsohuwr ce ta min laifin daya shafeku,amma kiyi haquri zanzo in sha Allahu" cikin murmushi hasina ta tabe baki
"Kedai bansan me ya dameki ba,koda yake an auna arziqi da aka samu ma kika ci gaba da zuwa katsinar da kika yiwa yajin aiki wajen shekaru hudu" murmushin da baikai har zuci ba shahida tayi tana cire agogon hannunta
"Yanzun ma mawuyacine idan ban koma muku yajin aikin ba ai" ta qarshe fada wani abu na takore mata wuya idan ta tuna kasassabar dasu daada suka aikata mata,saidai takanji sassauci idan ta tuna tana da hope a yau,qasa qasa da murya hasina tayi
"Hala ta kusa kwatanta miki abinda taso yimin kenan?" Kallonta shahida take ba tare da tace komai ba tana son jin qarin bayani
"Wai in gaya miki matarnan daga zuwa mata hutu shikenan tasa aka mata kiran saurayina qafa da qafa wai ya kamata ya fito hakanan,wannan shekarar ta shirya aurar da jikokinta,wai basai ya dorawa kanshi wata dawainiya ba yayi abinda addini kawai yace masa ya wadatar Allah ya sawa auren albarka" tagumi da haba shahida tayi kawai tana jin wannan bayanin,ita kenan ta mata dakyau ma data amshi kudin aure,amma gwara hasina da ita sau dubu
"Hasina kukan dadi kike,kinsan me daada tayimin?" Kai ta girgixa tana duban shahida
"Kudin aurena da sadakina suka amsa gaba daya ba tare da na sani ba,kuma ba tare da nasan waye zan aura din ba,kawai don bincikensu ya basu managarcine suke ganin ya dace dani" idanu waje hasina ta fito dasu tana duban shahida,kafin tace wani abu suka jiyo maganar daada daga tsakar gida wadda ta fito da wanka ne tana fadin
"Da kika shigo kika bar akwatin naki rana na duka waye zai dauke miki" dole kowanne yaja bakinsa yayi shuru harta iso falon,saita kalli idanunsu na 'yan sakanni kana ta tabe baki
"Magulmatan banza da wofi" daga haka tayi wucewarta daki donta saka kaya,yayin da shahida cikin dacin rai da baqincikin daya taso mata ta fito tsakar gida ta shiga bandaki tayi fitsari sannan ta daura alwala nan bakin famfo ta shigo da akwatin nata.
Qarfe daya da minti ashirin na rana tana tashi daga saman abun sallarta wayarta ta dauki tsuwwa,hasina ta miqo mata ta duba,nuradden ke kira ko bai fada ba tasan ya iso ne,gabanta taji yayi mummunar faduwa ta daga idanunta ta kalli daada data qarawa fura da nono ruwa take sha,saita kalli hasina,suka hada idanu ta mata signa sannan ta fita tsakar gida,ba jimawa ta biyo bayanta,janta tayi bakin kitchen ta gaya mata abinda ke faruwa
"Tabdi,kina tunanin akwai abinda zai sauya dada?,amma arashin tayi akan bar arha,bari na gaya mata baqo zai shigo" ta juya tana komawa,kafin takai ga shiga falon yaro ya tamfatsa sallama yana rangada fadin wai ana sallama da shahida,daada dake zaune a rumfarta tayi katsu tana jiran taji wanda zaiyi magana cikinsu,shuru sukayi ba wadda ta amsa,sai daadan ta kira yaron ya qaraso bakin rumfar
"Waye yake sallama da ita?"
"Wani ne,wai nuradden daga kano"
"Kano?" Ta sake tambayar yaron,saiya kada kai alamun eh,shuru na sakanni sannan tace
"Jeka ce masa ya shigo" juyawa yaron yayi ya fice ita kuma ta kira shahida da hasina gaba daya
"Xauna nan" ta nunawa shahida gefanta,ba musu ta zauna jiki a sanyaye,ta dubi hasina
"Bude firinjin can ki ciro ruwa da lemo" ba musu hasinar tayi yadda tace,dada ta nuna mata shimfidar daddumar data gama salla akai bata kai ga daukewa ba tace ta dora saman nan.
Cikin minti biyu kacal nuradden ya bayyana cikin falon,yaci manyan kaya yanata qamshi,bashi kadai bane shida wani abokinsa ko kuma ince amininsa ne,duk da dan uwanshi ne,cikin girmamawa suka zauna saman shimfidar suna gaida daada,ta amsa musu kadaran kadaham,yayin da idanun nuradden ke kan shahida.
Tayin ruwa da lemon tayi musu,Sayyid abokinsa ya bude ya zuzzuba musu a kofi,kusan shi kadai yasha,yana sha suna dan taba jira jifa jifa da daada tana tambayarshi kano,kasancewar ta dauki shekaru masu dama rabonta da ita,tun kafin rasuwar babansu shahida.
Sai da suka kammala tasa hasina ta zuba musu abinci,saidai sunce a qoshe suke,tilas ta rufe ta maida kitchen din,shuru ne ya ratsa na dan wani lokaci sannan sayyid yace
"Am...daada,abinda yake tafe damu dama magana ce game da shahida da kuma abokina nura,duk da nasan bata sanar miki da zuwanmu ba"
"Haka yake" a nutse sayyid ya fayyacewa daada komai,tayi gyaran murya tana dubansu
"Nasan cewa kuna da labarin an bada shahidan harma an karbi sadakinta,idan ma ta boye maka bata gaya maka ba ni ya zama wajibi na gaya maka gaskiyar abinda ake ciki"
"Ta fadama bata boye ba daada"
"Yauwa...an riga da an karbi sadakin yaron,kuma a shekarun da Allah ya bamu bai kamata kuma ace muna magana biyu ba,uwa uba sanin kanka ne cewa haramunne neman aure akan nema,koda ciniki akan ciniki ne haramun ne bare nema kan nema,matar mutum kabarinsa,Allah ya qaddari haka tun farko shi yasa ya hukunta jinkirin zuwanka garemu,saboda haka ina mai yaba maka bisa soyayyar daka nunawa jininmu,ina kuma mai maka fatan samun dacewa da wata matar data fita,sannan ina mai dorawa da baka haquri,kayi haquri,Allah ya sawa zuciyarka dangana" sayyid ne kawai ke amsawa da amin,yayin da gaba daya jikin nuradden ya mutu murus,zufa ta dinga yanko masa tako ina
"Mun gode sosai da karamcin da akayi mana" sayyid ya fada sanda suke miqewa bayan sun ajewa daada kudi
"A'ah yaro...nifa bazan karba ba,zoka dauka ku wuce Allah yayi maka zabi mafi alkhairi" qememe suka qi dauka haka suka fice,daada ta juya ta kalli shahida dake zaune gefanta tana sharbar qwalla
"Saikije ki sallamesu" daga haka ta miqe ta tayi wucewarta daki,sanda ta cimma qofar gidan tuni su nuradden sun wuce,sai tex daya turo mata na anjima zai kirata don yanzu baida nutsuwar tsaiwa,sulalewa tayi ta zauna gefan gadon,tana qoqarin hadiye kukanta.
Shigowar daada dakin ya sanyata daga kai tana kallonta,tana daga tsaye ta soma magana
"Kin kyauta sosai da kika sanyashi yazo kika toxarta mu,daa can kinsan yana sonki baki bashi dama ba har saida muka yanke hukunci a kanki?,ko kina tsammanin mu warware maganar da mukayi kaman qananun mutane?,to idan ma zaki kwantar da hankalinki ki nutsu waje guda shiya fiye miki alkhairi,ki shirya kuma ki dakaci zuwan gobe,mijinki da yardar Allah zaizo kuga juna,idan kinga dama kuma idan yazo din ki watsa mana qasa a idanu" daga haka daadan ta juya tayi ficewarta,sai kawai shahidan ta bita da kallo ranta na quntata,koma meye shi ya janyo mata,kuma shima saiyaji a jikinsa da zuciyarsa yadda ya janyo mata bacin rai tsakar rana ba tare data shiryawa hakan ba.
***** ****** ****** *****
Tunda ta tashi washegarin take kwance abinta kamar ruwa taqi yin komai,saidai daga nan ta koma can,hasina tayi tayi ta tashi tayi wani abun ko taji qwarin jikinta amma ta qeqashe qasa,ko kallo bata ishi daada ba sangar gabanta kawai take,tana daga kwancen tana kallon daada,yadda ta cika fridge dinta da fura da nono mai kyau,lemuka da kuma ruwa,tasa hasina tayi total na kayan fulawa aka siyo komai hasina tayi dan dai dai aka adana komai,baki ta tabe ta dauke kai bacin rai na cinta sanda daada ta fito da sabuwar daddumarta da kawu ummaru ya bata sanda ya dawo daga umara ya fesheta da turare ta baiwa hasina taje ta shimfida a dakin soro.
Saida komai ya kammala hasina ta isketa kwance cikin kujera tana saqa da warwara ta zauna gefanta
"Ya kamata ki tashi ko ruwa ko watsa kyaji dadin jikinki?" Idanunta da suka sake girma saboda kwana biyu data yi bata saka musu kwalli ba ta watsawa hasina cikin salon tambaya
"Me kikeson cewa?,kice kawai na tashi na yi masa kwalliya saboda zaizo,mutuncina ya qara zuba a idanunsa ko?" Murmushi hasina ta saki tana kada kai
"Niba haka nake nufi ba,kawai nasan yadda kikeson wanka wuni guda kuma ace tun safe ga azahar ta shiga baki watsa ruwa ba bare kici wani abun ai babu dadi,a qalla kodon tsaftar jikinki ko?" Saita maida kanta ta kwantar gami da rufe ido sannan ta amsa mata
"Share kawai" dubanta hasinan tayi na wasu mintunan sannan ta miqe tana cewa
"Allah ya kyauta,ya kamata dai ki sawa ranki salama,tunda kinsan cewa aikin gama ya gama,kada madai azo gaba kina jin kunya yazo kiga ya miki ki kamu da sonshi,kinsan wallahi daada ba raga miki zatayi ba"da sauri ta sake bude idon ta dubi hasina
"So,bakisan nayi bikin binneshi ba?" Dariya ta qwacewa hasina ta kama baki tana kallonta
"Shi kuma wannan da kika kawo fa?,mutunci kuke kenan?"
"Nuradden?..inason in rama halaccin da yayi minne shekaru kusan hudu"
"Tabdi,kice gwara da Allah yasa daada ta zaba miki miji,ashema ba soyayya kuke ba kenan" kofin dake gefanta shahida ta wafto ta jefi hasina dashi Allah yasa ta kauce bai sameta ba,har ga Allah taso ta sametan don bata da bakinma ce mata ta fita saboda wani abu dake takore da wuyanta
"Na rantse da Allah na tashi hasina saidai daada ta fiddaki daga gidan nan" cikin dariya ta fice tana cewa
"A'ah,a'ah,bani nakar zomon ba,ratayarma kuma ba'a bani ba".
Qarfe uku na rana da 'yan mintina daada ta shigo ta sameta
"Tashi kiyi wanka ko yanzu nasa akaimin ke bandaki na sabeki" ta furta tana nuna da gaske take,saida ta gama taurin kanta ganin da gaske daadan take sannan ta shiga bandaki tayi wankan.
Sanda ta fito mai kawai ta shafa sai turarenta oily data gogawa fatarta,tasaka wasu riga da skert na atamfa ta zura dogon hijabinta daya sauka har saman qafafunta ta soma da nafila kafin ta gabatar da farillar sallar la'asar.