Sashe 12
Alkawarin Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARING🙏🏽*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*KO KUMA*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARING🙏🏽*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos
*Alqawarin Allah*
0️⃣9️⃣
Tun daga lokacin ta maida abincin anwar ya zama wajibinta,duk sanda ya nuna alamun turjiya na bazai amsa ba anan ne zasuyi fada,har hakanma ya zame masa jiki.
Gefe daya kuwa rayuwarshi sai hamdala kawai,kusan duk wani fadi tashi ya zame ma rayuwarshi jiki,ta fannin kudin registration kuwa ba wani ci gaba da aka samu,iyakar qoqarinsa bai hada komai ba kaman yadda ya saba,yaqi kuma sanarwa anty husaina,tun yana jin babu komai harya soma shiga damuwa,ganin lokaci yana quracewa,sannu a hankali ya soma yanke tsammanin samun kudin ma gaba daya,wanda hakan ya jefashi cikin damuwa mai tsanani,damuwar da tasa anty husaina ta gane halin da ake ciki,ta kirashi tayi masa fada sosai,ta kuma saida dan abinda ke gareta na kudi,saidai kudin basu cika ba,kaso d'aya aka samu cikin biyu,a lokacin ya rage saura kwanaki makarantar su rufe registration.
A hankali take takowa zuwa cikin soron nasu,niyyarta ta tsoratashi kaman yadda yayi mata shekaran jiya ya tsoratata,taji tsoro sosai ya koma gefe yana mata dariya yana fadin
"Ashe farar kura ce ke bansani ba?".
Yau da yazo kan dakalin qofar gidan nasu yaci burki,hakanan yake jin ranshi babu dadi,wanda hakan ya bayyana har gangar jiki da fuskarshi,saidai duk sanda ya tuna yanzu zaiga sanyin idaniyarsa sai yaji yanayin da yake ciki din ba komai bane,wayarshi dage aljihun wandonshi ta dauki qara,ya zura hannunshi a hankali ya zaro wayar,anty husaina ce ke kiranshi,yasan kuma kiran bai rasa nasaba da cikon kudin registration dinsa ba,zayaso kunnuwanta su jiye masa ya samu,saidai ba mai yiwuwa bane yayi mata qarya,abokin kuka shi ake gayawa mutuwa,sannan uwa uba bayaso wani abu ya kawowa karatunshi tsaiko,babban burinsa a yanzu shine ya kammala karatunsa ya samu aiki,ya auri shahidansa ya kuma kula da anty husaina,itama ta huta taji dadinsa
"Yaya dai muhammadu an samu cikon kuwa?" Ta tambayeshi bayan ya gama gaidata,cikin nuna kasawa da sarewa yace
"Anty ina ganin saidai nayi haquri....wannan karon duk wani qoqarina na samun cikon kudin na gaza,kudin sunqi samuwa....ina tsoron asarar karatuna..." Tausayinsa ya kama anty husaina,tasan abune mai wuya ganin karayar anwar
"Kaci gaba da addu'a,ina nan ina nawa qoqarin mu zubawa sarautar Allah ido,in sha Allahu yana tare da mu"
"A'ah anty.....karki takurawa kanki karki damu,nima zanci gaba da nawa qoqarin...".
A hankali ta koma da baya cikin tsananin mutuwar jiki,ba labe tayi musu ba amma ta kasa tafiya sanda yake wayar da anty husaina,cikin mutuwar jiki da karaya take juyawa zuwa cikin gidan,qirjinta ya quntata qwalla ta cika mata idanunta,dama akwai wani abu da anwar zai iya boye mata game dashi?,da wannan tunanin ta isa dakinta,gefan katifarta ta samu ta zauna tallafe da kumatunta,batasan adadin lokacin data dauka a haka ba har ya tarawa wayarta miscal bata gani ba,saida ummanta ta daga labulen dakin
"Wanne shashanci ne kike haka shahida?,kinsan ba zaki samu fita ba kikabar anwar qofar gida yana jiranki?" Hannayenta ta sauke tana cewa
"Yanzu zan fita umma" sakin labulen tayi ta juya ta fice tana mita
"To ke kuma ya isa haka malamar mita,tunda ta baki uzuri basai kija bakinki ki shuru ba?" Ta jiyo abbanta yana fada
"Kaga kar kace zakamin fada,don na mata magana laifi nayi?"
"Ba laifi bane,mitar ne ni banason ji karki cikamana kunne"
"Wai yau cin mutuncin naka ne ya motsa baban shahida?" Ta saki abinda take ta zuba masa idanu tana tambayarsa,saiyayi banza da ita ya zubda ruwan daya kurkure bakinsa ya dauki hularsa ya fice,ajiyar zuciya shahida dake tsaye bakin window ta saki,ta godewa Alla daya taqaita cecekucen nasu baiyi tsaho ba har yaja hankalin anwar ko yajisu.
Katifarta taje ta daga,kudaden da uncle hisham ya bata ta dauko,ta zauna ta qirgasu a nutse sannan ta shiryasu,koda batasan nawa anwar ke buqata ba tasan cikon kudin bazaikai yawan kudaden dake hannunta ba,don kudaden da uncle anwar din ya bata suna da yawa,don taji ma anty amina na cewa mama su aje a karba a siyawa shahidan tukunya mai sha biyu a aje mata,lanqwashesu tayi sannan ta miqe ta gyara mayafinta ta fice.
Sanda ta koma yana zaune kan dakalin,ya zubawa qasa idanu wanda hasken farin wata ya haske jikinsa yake bashi hoton inuwarsa,a hankali ya dago kai idanunsu suka hadu da juna,wani sanyi yaji har cikin rai da zuciyarsa,saiya sakar mata murmushi yana jin kaso tamanin na quncin da zuciyarsa ke ciki ya tafi,kallon farko ana biyu ya karanci lallai akwai abinda yake damunta,duk sai yaji wani iri,yaji babu dadi,duk wata walwala da karsashinsa ya shiga yin nashi guri,shi ya amshi daddumar hannunta ya shimfida ya kuma yi mata nuni data zauna,batayi musu ba ta zauna din,yana tsaye qyam a kanta yana qare mata kallo,ya samu kanshi da kasa zama
"Mene ne yayi kutse cikin farincikin gimbiyata?"
"Kaine...." Ta fada kanta tsaye,cikin sanyin jiki ya samu dan wani dutse dake daura da ita ya zauna samanshi
"Bana fatan kasancewar wannan ranar....wane kuskure na tafka haka harya zama tarnaqi wa farincikin zuciyata?" Hawaye ta soma zubarwa,bana komai bane saina tausayinsa,zurfin cikinsa yayi yawa,kara da kawaicinsa sun baci,amma ko daya bata son ya sake boye mata wani abu daya danganceshi,tana ganin kaman hakan wani naqasu ne tattare da dangantakarsu,zai zama tamkar bai bata muhimmancin da take tsammanin ya bata ba
"Ashe dukan inda nake tunanin nakai bankai can ba a zuciyarka?"
"Ya salam" ya furta fuskarshi na nuna tsantsar tashin hankalin daya shiga,wanda har cikin zuciyarshi haka ne,wanda har yanajin ya zarce na rashin kudin registration da bai samu ba
"Shah......"
"Kar ka sake cemin komai....na kamaka da laifuka guda biyu kawo yanzu,ban taba boye maka komai daya danganceni ba....amma kai ka boyemin abubuwa har biyu,ban sani ba ko.matsayina baikai nasan wannan fannin ba...." Sanyi ya dinga ji yana ratsa qasan zuciyarshi,duk da bai fuskanci me yayi mata ba,dubanta yake cike da qaina soyayya sa shauqi mai yawa,ta damu da lamuransa fiye da tunanin mai tunani kamar yadda ya damu da nata,bai tsammaci zata soshi kamar yadda yakesonta ba,ya zaci zata soshi ne irin son da baikai ya kawo ba,kodon kyau da Allah ya bata,kodon gata data d'arashi,ko don saboda farinjini da Allah yayi mata
"Yanzu karatunka ba nawa bane?" Ta fada maganar quruciyarta na fitowa fili,hakanan ta b'ata rai sosai ta kuma tsareshi da ido,murmushi ya saki wanda ya bayyana fararen haqoranshi
"Nakine my shahida"
"Don me baka gayamin halin da kake ciki ba?" Dan shuru yayi yana tauna amsar da zai bata,tsahon minti guda kafin yace
"Shahida....kin wuce duk inda kike zato kike tsammani a wajena,tunda Allah ya busan numfashi ban taba qaunar wata d'iya mace ba saike,nine namiji,ni nake nema,kuma nine sama dake,bai cancanci ace dukkan wata wahalata tana wuyanki ba"
"Koda bani da abun da zan taimaka dashi ai na sanyaka cikin addu'o'ina ko?" Idanunsa ya lumshe idanunsa yayi yana sakin murmushi
"Ni na sani shahidana koda banda damuwa ba zata daina sakani a addu'arta ba"
"Ta yaya zan aminta cewar mun zama daya kana boyemin ire iren wadan nan abubuwan?"
"Shahidaa...karki sake tunanin bamu zama daya ba,kin zama muhammad anwar,na zama rahamatulshahida" sunan ya bata dariya har sai data murmusa,tafin hannunta ta bude sannan ta miqa masa kudin hannunta
"Ungo qirgamin" amsa yayi yana zolayarta,sannan ya soma qirgawa yana cewa
"Shahidana ta zama hajjaju" sai daya gama qirgawa sannan ya dago ya dubeta yana gaya mata nawa ne,kai ta gyada duk da tasan nawa ne dama
"Kayi amfani dasu" sak ya tsaya yana dubanta kafin yace
"Shahida...." Idanunta ta ware masa tana dubansa itama,ya gane me take nufiSai ya saki murmushi
"Aro na baka,amma kayi duk amfanin da kakeson yi dasu"
"Kai amma wannan yarinya kin iya bada rance....to na gode Allah ya bani ikon biya" daga haka sukaci gaba da hirarsu,saidai rabin hankalinsa dukka yana kan halayen shahidan,yana sake godewa Allah tabbas baiyi zaben tumun dare ba,hakanan ya tabbatar bai miqa zuciyarshi inda bai cancanta ba.
Wannan abu da shahidan ta yiwa anwar ba qaramin qara mata qima yayi a idanun anty husaina ba,wata qauna take mata tamkar diyar cikinta tun kafin ma ta yiwa anwar hakan,ta yadda ta kuma yi amanna cewa anwar yayi dace da matar aure,ta kuma shiga sahun masu masa addu'ar Allah yasa shahidan ta zama mallakinsa.
Ta gefan anwar dinma tuni ya shiga bakunan 'yan uwan shahidan musamman 'yan gidansu da anty amina wadda sukafi dasawa da shahida duk cikin 'yan uwan mamanta,kasancewar tasu tafi zuwa daya da mamanta,kuma ita daya ke gaya mata magana itama maman da ita take shawara.
Cikin ikon Allah anwar yayi registration dinsa,komai yaci gaba da tafiya dai dai,rayuwarsu da shahida kuwa ta zama abar kwatance ga duk wanda ya sansu,kowa najin jinin danuwansa na yawo a nasa jikin,tun mutane na mamakin yadda sukeson juna har abun ma ya zame musu jiki,su kansu yadda suke nunawa kansu qauna basusan sunayi har haka ba saidai a gaya musu.
Sannu a hankali rayuwa taci gaba da juyawa,ta wanni fannin ana samun ci gaba yayin da wani bangaren yake zamowa koma baya da babban naqasu wajen bawa.
Zuwa sannan shahida sun shiga ss 3 term din farko,a sannan ne Allah ya yiwa mahaifin zunnurah rasuwa,hakan ya zama silar barinsu garin kano sukayi qaura suka koma katsina cikin danginsu,dalilin kenan daya sanya kusancin shahida da firdausi ya sake samun tagomashi mai yawa,ta maye mata gurbin zunnurah,yayin da ita da zunnurah ya zama sai a waya,lokaci lokaci idan sukayi waya tana sako mata zancan fiddausin tare da sake ja mata kunne kan tayi hankali da ita,murmushi shahida keyi yawancin lokaci,ta sake yarda Allah ne kadai.ya isa ya hada zukatan bayinsa,har yau bata tana ganin wani abu mai kama da abinda zunnurah ke tuhumar fiddausi dangane da ita ba.
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*KO KUMA*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sabbabi,karku manta ky danna SUBSCRIBE,kuyi LIKE sannan kuyi SHARING🙏🏽*
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
https://www.youtube.com/channel/UC4kJO342hmb_Pd2luKHBjFA/videos
*Alqawarin Allah*
0️⃣9️⃣
Tun daga lokacin ta maida abincin anwar ya zama wajibinta,duk sanda ya nuna alamun turjiya na bazai amsa ba anan ne zasuyi fada,har hakanma ya zame masa jiki.
Gefe daya kuwa rayuwarshi sai hamdala kawai,kusan duk wani fadi tashi ya zame ma rayuwarshi jiki,ta fannin kudin registration kuwa ba wani ci gaba da aka samu,iyakar qoqarinsa bai hada komai ba kaman yadda ya saba,yaqi kuma sanarwa anty husaina,tun yana jin babu komai harya soma shiga damuwa,ganin lokaci yana quracewa,sannu a hankali ya soma yanke tsammanin samun kudin ma gaba daya,wanda hakan ya jefashi cikin damuwa mai tsanani,damuwar da tasa anty husaina ta gane halin da ake ciki,ta kirashi tayi masa fada sosai,ta kuma saida dan abinda ke gareta na kudi,saidai kudin basu cika ba,kaso d'aya aka samu cikin biyu,a lokacin ya rage saura kwanaki makarantar su rufe registration.
A hankali take takowa zuwa cikin soron nasu,niyyarta ta tsoratashi kaman yadda yayi mata shekaran jiya ya tsoratata,taji tsoro sosai ya koma gefe yana mata dariya yana fadin
"Ashe farar kura ce ke bansani ba?".
Yau da yazo kan dakalin qofar gidan nasu yaci burki,hakanan yake jin ranshi babu dadi,wanda hakan ya bayyana har gangar jiki da fuskarshi,saidai duk sanda ya tuna yanzu zaiga sanyin idaniyarsa sai yaji yanayin da yake ciki din ba komai bane,wayarshi dage aljihun wandonshi ta dauki qara,ya zura hannunshi a hankali ya zaro wayar,anty husaina ce ke kiranshi,yasan kuma kiran bai rasa nasaba da cikon kudin registration dinsa ba,zayaso kunnuwanta su jiye masa ya samu,saidai ba mai yiwuwa bane yayi mata qarya,abokin kuka shi ake gayawa mutuwa,sannan uwa uba bayaso wani abu ya kawowa karatunshi tsaiko,babban burinsa a yanzu shine ya kammala karatunsa ya samu aiki,ya auri shahidansa ya kuma kula da anty husaina,itama ta huta taji dadinsa
"Yaya dai muhammadu an samu cikon kuwa?" Ta tambayeshi bayan ya gama gaidata,cikin nuna kasawa da sarewa yace
"Anty ina ganin saidai nayi haquri....wannan karon duk wani qoqarina na samun cikon kudin na gaza,kudin sunqi samuwa....ina tsoron asarar karatuna..." Tausayinsa ya kama anty husaina,tasan abune mai wuya ganin karayar anwar
"Kaci gaba da addu'a,ina nan ina nawa qoqarin mu zubawa sarautar Allah ido,in sha Allahu yana tare da mu"
"A'ah anty.....karki takurawa kanki karki damu,nima zanci gaba da nawa qoqarin...".
A hankali ta koma da baya cikin tsananin mutuwar jiki,ba labe tayi musu ba amma ta kasa tafiya sanda yake wayar da anty husaina,cikin mutuwar jiki da karaya take juyawa zuwa cikin gidan,qirjinta ya quntata qwalla ta cika mata idanunta,dama akwai wani abu da anwar zai iya boye mata game dashi?,da wannan tunanin ta isa dakinta,gefan katifarta ta samu ta zauna tallafe da kumatunta,batasan adadin lokacin data dauka a haka ba har ya tarawa wayarta miscal bata gani ba,saida ummanta ta daga labulen dakin
"Wanne shashanci ne kike haka shahida?,kinsan ba zaki samu fita ba kikabar anwar qofar gida yana jiranki?" Hannayenta ta sauke tana cewa
"Yanzu zan fita umma" sakin labulen tayi ta juya ta fice tana mita
"To ke kuma ya isa haka malamar mita,tunda ta baki uzuri basai kija bakinki ki shuru ba?" Ta jiyo abbanta yana fada
"Kaga kar kace zakamin fada,don na mata magana laifi nayi?"
"Ba laifi bane,mitar ne ni banason ji karki cikamana kunne"
"Wai yau cin mutuncin naka ne ya motsa baban shahida?" Ta saki abinda take ta zuba masa idanu tana tambayarsa,saiyayi banza da ita ya zubda ruwan daya kurkure bakinsa ya dauki hularsa ya fice,ajiyar zuciya shahida dake tsaye bakin window ta saki,ta godewa Alla daya taqaita cecekucen nasu baiyi tsaho ba har yaja hankalin anwar ko yajisu.
Katifarta taje ta daga,kudaden da uncle hisham ya bata ta dauko,ta zauna ta qirgasu a nutse sannan ta shiryasu,koda batasan nawa anwar ke buqata ba tasan cikon kudin bazaikai yawan kudaden dake hannunta ba,don kudaden da uncle anwar din ya bata suna da yawa,don taji ma anty amina na cewa mama su aje a karba a siyawa shahidan tukunya mai sha biyu a aje mata,lanqwashesu tayi sannan ta miqe ta gyara mayafinta ta fice.
Sanda ta koma yana zaune kan dakalin,ya zubawa qasa idanu wanda hasken farin wata ya haske jikinsa yake bashi hoton inuwarsa,a hankali ya dago kai idanunsu suka hadu da juna,wani sanyi yaji har cikin rai da zuciyarsa,saiya sakar mata murmushi yana jin kaso tamanin na quncin da zuciyarsa ke ciki ya tafi,kallon farko ana biyu ya karanci lallai akwai abinda yake damunta,duk sai yaji wani iri,yaji babu dadi,duk wata walwala da karsashinsa ya shiga yin nashi guri,shi ya amshi daddumar hannunta ya shimfida ya kuma yi mata nuni data zauna,batayi musu ba ta zauna din,yana tsaye qyam a kanta yana qare mata kallo,ya samu kanshi da kasa zama
"Mene ne yayi kutse cikin farincikin gimbiyata?"
"Kaine...." Ta fada kanta tsaye,cikin sanyin jiki ya samu dan wani dutse dake daura da ita ya zauna samanshi
"Bana fatan kasancewar wannan ranar....wane kuskure na tafka haka harya zama tarnaqi wa farincikin zuciyata?" Hawaye ta soma zubarwa,bana komai bane saina tausayinsa,zurfin cikinsa yayi yawa,kara da kawaicinsa sun baci,amma ko daya bata son ya sake boye mata wani abu daya danganceshi,tana ganin kaman hakan wani naqasu ne tattare da dangantakarsu,zai zama tamkar bai bata muhimmancin da take tsammanin ya bata ba
"Ashe dukan inda nake tunanin nakai bankai can ba a zuciyarka?"
"Ya salam" ya furta fuskarshi na nuna tsantsar tashin hankalin daya shiga,wanda har cikin zuciyarshi haka ne,wanda har yanajin ya zarce na rashin kudin registration da bai samu ba
"Shah......"
"Kar ka sake cemin komai....na kamaka da laifuka guda biyu kawo yanzu,ban taba boye maka komai daya danganceni ba....amma kai ka boyemin abubuwa har biyu,ban sani ba ko.matsayina baikai nasan wannan fannin ba...." Sanyi ya dinga ji yana ratsa qasan zuciyarshi,duk da bai fuskanci me yayi mata ba,dubanta yake cike da qaina soyayya sa shauqi mai yawa,ta damu da lamuransa fiye da tunanin mai tunani kamar yadda ya damu da nata,bai tsammaci zata soshi kamar yadda yakesonta ba,ya zaci zata soshi ne irin son da baikai ya kawo ba,kodon kyau da Allah ya bata,kodon gata data d'arashi,ko don saboda farinjini da Allah yayi mata
"Yanzu karatunka ba nawa bane?" Ta fada maganar quruciyarta na fitowa fili,hakanan ta b'ata rai sosai ta kuma tsareshi da ido,murmushi ya saki wanda ya bayyana fararen haqoranshi
"Nakine my shahida"
"Don me baka gayamin halin da kake ciki ba?" Dan shuru yayi yana tauna amsar da zai bata,tsahon minti guda kafin yace
"Shahida....kin wuce duk inda kike zato kike tsammani a wajena,tunda Allah ya busan numfashi ban taba qaunar wata d'iya mace ba saike,nine namiji,ni nake nema,kuma nine sama dake,bai cancanci ace dukkan wata wahalata tana wuyanki ba"
"Koda bani da abun da zan taimaka dashi ai na sanyaka cikin addu'o'ina ko?" Idanunsa ya lumshe idanunsa yayi yana sakin murmushi
"Ni na sani shahidana koda banda damuwa ba zata daina sakani a addu'arta ba"
"Ta yaya zan aminta cewar mun zama daya kana boyemin ire iren wadan nan abubuwan?"
"Shahidaa...karki sake tunanin bamu zama daya ba,kin zama muhammad anwar,na zama rahamatulshahida" sunan ya bata dariya har sai data murmusa,tafin hannunta ta bude sannan ta miqa masa kudin hannunta
"Ungo qirgamin" amsa yayi yana zolayarta,sannan ya soma qirgawa yana cewa
"Shahidana ta zama hajjaju" sai daya gama qirgawa sannan ya dago ya dubeta yana gaya mata nawa ne,kai ta gyada duk da tasan nawa ne dama
"Kayi amfani dasu" sak ya tsaya yana dubanta kafin yace
"Shahida...." Idanunta ta ware masa tana dubansa itama,ya gane me take nufiSai ya saki murmushi
"Aro na baka,amma kayi duk amfanin da kakeson yi dasu"
"Kai amma wannan yarinya kin iya bada rance....to na gode Allah ya bani ikon biya" daga haka sukaci gaba da hirarsu,saidai rabin hankalinsa dukka yana kan halayen shahidan,yana sake godewa Allah tabbas baiyi zaben tumun dare ba,hakanan ya tabbatar bai miqa zuciyarshi inda bai cancanta ba.
Wannan abu da shahidan ta yiwa anwar ba qaramin qara mata qima yayi a idanun anty husaina ba,wata qauna take mata tamkar diyar cikinta tun kafin ma ta yiwa anwar hakan,ta yadda ta kuma yi amanna cewa anwar yayi dace da matar aure,ta kuma shiga sahun masu masa addu'ar Allah yasa shahidan ta zama mallakinsa.
Ta gefan anwar dinma tuni ya shiga bakunan 'yan uwan shahidan musamman 'yan gidansu da anty amina wadda sukafi dasawa da shahida duk cikin 'yan uwan mamanta,kasancewar tasu tafi zuwa daya da mamanta,kuma ita daya ke gaya mata magana itama maman da ita take shawara.
Cikin ikon Allah anwar yayi registration dinsa,komai yaci gaba da tafiya dai dai,rayuwarsu da shahida kuwa ta zama abar kwatance ga duk wanda ya sansu,kowa najin jinin danuwansa na yawo a nasa jikin,tun mutane na mamakin yadda sukeson juna har abun ma ya zame musu jiki,su kansu yadda suke nunawa kansu qauna basusan sunayi har haka ba saidai a gaya musu.
Sannu a hankali rayuwa taci gaba da juyawa,ta wanni fannin ana samun ci gaba yayin da wani bangaren yake zamowa koma baya da babban naqasu wajen bawa.
Zuwa sannan shahida sun shiga ss 3 term din farko,a sannan ne Allah ya yiwa mahaifin zunnurah rasuwa,hakan ya zama silar barinsu garin kano sukayi qaura suka koma katsina cikin danginsu,dalilin kenan daya sanya kusancin shahida da firdausi ya sake samun tagomashi mai yawa,ta maye mata gurbin zunnurah,yayin da ita da zunnurah ya zama sai a waya,lokaci lokaci idan sukayi waya tana sako mata zancan fiddausin tare da sake ja mata kunne kan tayi hankali da ita,murmushi shahida keyi yawancin lokaci,ta sake yarda Allah ne kadai.ya isa ya hada zukatan bayinsa,har yau bata tana ganin wani abu mai kama da abinda zunnurah ke tuhumar fiddausi dangane da ita ba.