← Book details Yar Sarki Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 61

Sashe 27

Yar Sarki Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Mahreen da Maha suna gidan Umma hankalin su kwance, sai kuma shirye shiryen zuwa Bauchi da suke yi, ranan saturday soja zai kaisu suje su gano Kakus. Adamawa Kuma sai Ummeyhn su tazo zasu je, dukda Maha ba qaunan maganan zuwa Adamawa take ba.
Zaune suke da Umma a palourn, suna kallo a TV, Maha ce tace "Umma nikam gaskiya in Ummeyh tazo kice bazan bisu Adamawa ba" ta faɗa tana shagwaɓe fuska. Umma ta kalle ta tace ko meeyasa bakyason zuwa doter? Allah Umma kekam nasan kina sona zaki fahim ce ni, Kinga Arɗo wlh zalina yake ci, duk in naje sai ya zaneni ko ya kwaɗa man sandan sa, kuma ranan inaji kamun Abeeyh yayi tafiya da yace masa zamu je Adamawan yace wai kar mu yarda mu je ba tare da miji ba in ba haka ba zai bada kyautan mu a can qauyen.
Haba doter karki damu kinji kekam kina da mijinki ba mai yin kyauta da ke, kuma Arɗo bazai taɓa ki ba yanzu ai kin girma. Kallon Umma tayi tace "Umma Nifa banda saurayi bare miji kuma bakisan halin Arɗo bane shiyasa Umma" ta faɗa kaman zata yi kuka.
Murmushin manya Umma tayi! Doter ai Arɗon in ya takura maki Tom kice shine mijin naki ya baki sadaki kuyi Aure, shikkenan ba?
Dariyar Maha ta sanya yauwa Ummata kin iya kawo dabara. Little dake kwance a cinyan Maha yace "ancii cice unkui ne mijin ci ba aiyo ba(Arɗo ba).
Mahreen da ke danna waya ne ta sa dariya tace "indai mu bazamu faɗa maki gaskiya ki yarda ba Tom ɗan ki ya faɗa maki ki auri uncle nasa shikkenan dama kune iyayen sa" qarasa magann tayi tana dariyan. Maha tura baki tayi ta harari Mahreen tace "Umma kinji yaya Mahreen ko" Umma ta murmusa tace "qyaleta doter zan saɓa mata kinji" ɗaga kai tayi ta koma kan Little tace "my son kana so mu ɓata? Gyaɗa kai little yayi alamun a'a tace "okay karka qara faɗan wannan maganan ko" sai ya ɗaga ka tace "that's my good boy. Dariya litttle ya san ya yaji an yabeshi!
Qira ne ya shigo wayan Mahreen, ganin Abeeyhn su ya sa ta ɗau da wuri tana murmushi!
"Assalamualaikum Abeey masahul khair" shiru tayi na ɗan wani lokaci kamun ta kuma cewa "duk muna lafiya Abeey ga Mahan nan. Miqawa Maha wayan tayi, amsa Maha tayi suka gaisa da Abeeyhn nasu, da suka gama tace "ga Umman nan a kusa Abee ba na bata" miqawa Umma wayan tayi.
Sanda suka gaisa sosai da Umma cikin girmamawa da fara'a ya tambayi Abba da su Ameera da soja, Umma tace "yayan ku yana lafiya, baban yara Ameera kuma jiya suka koma da mijin ta duk suna lafiya, soja ma yana lafiya ya fita, Inshà Allahu duk zasuji gaisuwa baban yara" faɗin Umma. Miqawa Mahreen wayan tayi nan suka fara larabci da mahaifin nata....
Chapter 27 · 0% Book details