Sashe 99
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daddy na kaiwa nan ya mike tsaye yaja kujera baya, ya zagayo ta inda Ameer yake zaune ya dafa shi.
“Shin baka marmarin sanin waye mahaifinka? Su waye yan'uwan mahaifinka? Miye mahaifinka ya yi kamin ya rasu? Miye ma silar mutuwarsa? Baka son saduwa da yan'uwa da danginsa? This is right time da zaka kyautatawa iyayenka ka samu aljannarka cikin sauki, duk wanda zai fada maka wani abu bayan wannan ba masoyinka ba ne, ai yanzu ne lokacin da ya kamata ka yi hanzarin kwace muhallin duka yayan da Zahra take da su a zuciyarta, kai da ka zama ďan gata mai gida biyu iyaye hudu? Baya fika Ameer? Ka ci abinci lafiya...”
Daddy ya karasa yana bubbuga kafadarsa tare da murmushi sannan ya fice daga dinning din. Ameer ya juya yana kallon mahaifinsa sai kuma ya juyo ya kurawa abincin da yake ci ido, kalaman Daddy nata masa yawo a madafar tunanin da nazari, har ya fara tace su yana sakawa a babin lura. Kasa cin abincin yayi tun bayan four spoon da yayi a dazun duk kuwa da irin dadin da abincin yayi da kuma kasancewarsa favorite food dinsa. Tashi yayi ya fito daga bangaren Daddy ya fito waje ya tsaya yana kallon yadda Allah ya kawata saman da tausarari masu kyau da gaske.
Ya dauki tsawon lokaci a gurin sannan ya shiga parlour ya zauna for few minutes, ya tashi ya shiga dakinsa. Miss calls ya tarar kusan 9 daga number Ummi, daman kai ko da ta kira wayar na hannunsa ba zai yi picking ba balle kuma har yayi calling back. Shi be ga reason din da zai saka ta dame shi a yanzu ba, bayan ta kasa bashi kulawa a lokacin da ya fi bukata. Daddy was right idan zai bukaci wani abu a yanzu to tahirin mahaifinsa ne, not her or her family, ba zai son jin haka daga bakinta ba sai dai abu ya zame masa cilas shi ne tambayarta a ina yan'uwan mahaifinsa suke, a gurinsu yake son samun labarin komai ba a bakinta ba. Yana kokarin jifa da wayar akan gado wani kiran ya sake shigowa a take ya danna rejected. Kamin ya aje wayar sako ya shigo masa.
“Waira ce take son magana da kai, ta takura tana son ta tambaye ka wani abu”
Ya karanta sakon, kamin yayi decided zai dauka ko ba zai dauka ba, kiran ya sake shigowa, sai da ta kusa yankewa sannan ya daga ya saka wayar a hands-free, kuma yaki yayi magana har sai da Waira ta fara magana.
“Allo Ammir”
A dayan bangaren sai Ummi ta matso kusa ta karbi wayar ta saka hands-free saboda ta ji muryar ďanta.
“Ya aka yi?”
“Ina ta kira baka daga ba”
“Yanzu na daga ai”
“Baka son magana da ni?”
“Me yasa na daga wayar to?”
“Gashi nan kana bata fuska”
Ta fada ba dan ta ganshi ba, sai dan ta karanci hakan a muryarsa da yadda yake amsa mata. Ya nufi boutique dinsa ya tsaya gaban madubi yana kallon kansa, da gaske fuskarsa a hade take.
“Zan aje waya sai ka yi far'a sai na sake kira”
Ta fada. Jin haka sai ya saka ya sassauta fuskar yayi ya sauke numfashi.
“Wayar tana kusa da ke ko? Ita tace na ki fada min haka?”
Ummi ta yi saurin girgiza ma Waira kai.
“Aa Ummi tana dakinta”
“Ni na sauko ina falo”
Ya jimmm for some seconds sannan ya ce.
“Me mike son ki tambaye ni?”
“Abubuwa da yawa, na ce Ya Maleek ya kawo ni, sai yayi min ihu wai ba za a sake zuwa ba, kuma idan na sake yin maganarka ma sai ya min duka”
“Saboda shi ubanki ne?”
“Aa shi Ya Maleek ne”
“Baki da alaka da shi ai, ba shi da hujja”
“Shi yaron Ummi ne ai”
“Baki da alaka da Ummi baki da alaka da kowa a gidan nan, so babu wanda zai saka ki dole ko hana ki abun da kike so, idan ma akwai wannan to ni ne, domin ni na dauko ki daga daji, ni ne sikar zuwanki garin nan and that stupid house, remember?”
Ta kalli Ummi sannan ta daga masa kai.
“Yes”
“Good so no one has power over you, tambaye ni abun da kike son ki sani”
Ummi ta yi saurin rada mata a kunne.
“Zaka zo sai na tambaye ka?”
“No”
“Please”
“No”
“Abubuwa da yawa ne, ina son na sani zaka zo saboda ni?”
“Aa”
“Baka damuwa da matsalar kowa kai?”
Yayi shiru, ya saka hannunsa ya taba hancinsa ya runtse ido ya bude.
“Dole sai na zo wai?”
“Eh”
“Zaki iya tambayata a waya”
“Bana so a waya, kai baka da tausayi Ameer ko? Shiyasa ka tafi ka bar ni a lokacin da maciji ya cije ni a daji, ban manta ba i will hate you more”
“Zan zo”
Ya amsa ba tare da shiri ba.
“Yanzu?”
“No”
“Gobe ina zuwa school da safe”
“Zan same ki school din”
“Kasan ina ne?”
“Ki turo min address a waya”
“Okay zan aje waya”
“Good night”
“Good Night”
“Yeah Good Night”
Sai ta sake fada.
“Good night”
“Okay sai da safe”
Sai da ta yanke kiran sannan ya fito daga dakin ya jefar da wayar akan bed, shi yana da alot of questions da zai mata, sai dai hakan ba yana nufi ko da ya tafi ya shiga gidan ba sai dai ya tsaya daga wani gurin ta zo ta same shi.
“Bata manta ba, mata suna rike abun da yayi musu ciwo a zuciyarsu”
Ya fada yana tuna zancen da ta yi masa cewar ya barta a daji bayan maciji ya cijeta.
“Storyteller”
He said, sannan ya nufi bathroom dinsa.
UMMI's POV.
Ummi da mamaki take kallon Waira, bata taba tunanin tana da wayo ba irin yau, a yanzu ta gane Waira ta tashi daga karamar yarinya da take mata kallo zuwa baba mai wayo da basira. Domin bayan maganar farko data rada mata cewar zai zo ta tambaye bata sake ce mata komai ba, ita ta tsara masa komai.
“Baki taba fada mana cewar kin san Ameer ba Waira, ashe shi ya dauko ki ya saka ki a motar Nimra?”
“Ban san waya saka ni ba, amman dai na ganshi kuma ya gan ni, yana kallona a lokacin da maciji ya cijeni na yi ta neman taimakonsa be taimaka min ba har na suma ban san an saka ni a mota ba, ni dai na gani a wani guri tare da Sulem”
Ummi ta shafa kanta ta sumbaceta ta rumgumeta.
“Ina kaunarki Waira, yanzu kin san abun da nake so da ke, gobe idan kin tafi school, school bus ba zata dawo da ke ba, ina son ki roke shi ya kawo ki gidan nan, na san zai yi domin na lura kina da wani sirri a muryarki da mu'alamarki dake karya duk wata izza da fushi ko girman kai a gurin namiji, daman ko wace mace da yadda Allah ya halicceta, kin ga ni da ina kamarki farinjini na yi sosai da kiriniya, step father na ya sha wahala ta a lokacin har karyashi an yi saboda ni, Mamana kuma ba a magana Allah dai yayi mata rahama (Lallai kam dan mahaifin Deen da Deen sun sha duka saboda Zahra)”
Waira ta amsa.
“Toh Ummi, amman Ya Maleek ba zai yi ihu ba?”
“Ba zai yi ba, babu abun da nake bukata a yanzu kamar kusanci da ďana”
Ummi ta dago Waira daga jikinta.
“Gobe zan miki cake mai dadi ki tafi da shi”
“Okay”
Ta nufi upstairs tana jindadi zata ga Ameer a gobe ta yi masa tambayoyi akan abun da ya shige mata duhu.
She wake-up early saboda ta kwana rumgume da baby rabbit dinta da kuma tunanin haduwarta da Ameer. Tun asuba ta sauko kasa da zomonta ko wanke baki bata yi ba, ta nufi kitchen domin ta san Ummi ke shirya mata abun zuwa makaranta kuma tun da har ta fadi cewar zata yi mata cake. Ta leka Kitchen din kamar yadda ta saba sai ta samu Ummi da Mahmood a ciki yana taya ta aiki. Da kuzarinta ta shiga Kitchen din.
“Laaaa”
Ya juyo ya kalleta yana murmushi.
“Laa zaki ce yau ni nake taya Ummi aiki ko?”
Ya daga kai.
“Daddy ne ya raba mana aiki, yace yau idan na gobe Maleek ne, jibi Namra gata kuma ke, haka zamu yi ta yi har mu saba”
Ta juya ta kalli Ummi.
“Ummi Good Morning”
“Good Baby tafi ki wanke fuska ki yi wanka, zan hada miki tea yanzun nan kamin cake ya zama ready”
“Okay”
Ta juya ta fito daga kitchen din ta nufi stairs. hakan yayi daidai da shigowar Maleek falon, daman idan ya gama sallah azuba baya tashi a masallaci sai ya gama azkar dinsa, sannan yake shigowa gidan. Tsayawa ta yi sai da ya iso inda take ta gaishe shi kamar yadda ta Ummi ta koya mata.
“Good Morning”
Tsaye yayi yana kallonta sai ta sauke idonta kasa.
“Morning”
Ya amsa sannan ya wuce ya fara taka stairs din, bayansa ta bi, sai gashi ya tsaya ya juyo ya kalleta.
“Waye Ummi ta ce ki dauko waya a kira jiya da dare?”
“Malamina”
A take ta kirkiri karya ta fada masa abun da ba halinta ba. Domin bata yin karya mo matter what, a yanzun ma tana tsoron ya ce zai dake ta ne. Be ce mata komai ba ya juya ya haye sama, sannan ita ma ta shiga dakinta. Karfe bakwai da rabi school bus ta faka kofar gidan, sanin lokaci yayi ya saka Waira ta aje kofin tea da take sha ta ta dauki jakarta dake gefenta ta mike tsaye.
“Ummi time yayi”
Ummi ta so daga kujerarta ta matsa kusa da Waira ta sumbancin goshinta.
“Allah ya miki albarka, ga cake din na musamman ne na yi, yayi dadi sosai ki ci da yawa”
“Okay Ummi Thank you”
Ta karbi cake din ta nufi hanyar falo, Ummi kuma ta kalli Mahmood ta ce.
“Please fita ka fadawa driver bus din ba shi zai dawo da ita ba, za a zo a dauke ta ne”
Mahmood Ummi take yi ma magana amman Maleek ne yayi tambaya.
“Shin baka marmarin sanin waye mahaifinka? Su waye yan'uwan mahaifinka? Miye mahaifinka ya yi kamin ya rasu? Miye ma silar mutuwarsa? Baka son saduwa da yan'uwa da danginsa? This is right time da zaka kyautatawa iyayenka ka samu aljannarka cikin sauki, duk wanda zai fada maka wani abu bayan wannan ba masoyinka ba ne, ai yanzu ne lokacin da ya kamata ka yi hanzarin kwace muhallin duka yayan da Zahra take da su a zuciyarta, kai da ka zama ďan gata mai gida biyu iyaye hudu? Baya fika Ameer? Ka ci abinci lafiya...”
Daddy ya karasa yana bubbuga kafadarsa tare da murmushi sannan ya fice daga dinning din. Ameer ya juya yana kallon mahaifinsa sai kuma ya juyo ya kurawa abincin da yake ci ido, kalaman Daddy nata masa yawo a madafar tunanin da nazari, har ya fara tace su yana sakawa a babin lura. Kasa cin abincin yayi tun bayan four spoon da yayi a dazun duk kuwa da irin dadin da abincin yayi da kuma kasancewarsa favorite food dinsa. Tashi yayi ya fito daga bangaren Daddy ya fito waje ya tsaya yana kallon yadda Allah ya kawata saman da tausarari masu kyau da gaske.
Ya dauki tsawon lokaci a gurin sannan ya shiga parlour ya zauna for few minutes, ya tashi ya shiga dakinsa. Miss calls ya tarar kusan 9 daga number Ummi, daman kai ko da ta kira wayar na hannunsa ba zai yi picking ba balle kuma har yayi calling back. Shi be ga reason din da zai saka ta dame shi a yanzu ba, bayan ta kasa bashi kulawa a lokacin da ya fi bukata. Daddy was right idan zai bukaci wani abu a yanzu to tahirin mahaifinsa ne, not her or her family, ba zai son jin haka daga bakinta ba sai dai abu ya zame masa cilas shi ne tambayarta a ina yan'uwan mahaifinsa suke, a gurinsu yake son samun labarin komai ba a bakinta ba. Yana kokarin jifa da wayar akan gado wani kiran ya sake shigowa a take ya danna rejected. Kamin ya aje wayar sako ya shigo masa.
“Waira ce take son magana da kai, ta takura tana son ta tambaye ka wani abu”
Ya karanta sakon, kamin yayi decided zai dauka ko ba zai dauka ba, kiran ya sake shigowa, sai da ta kusa yankewa sannan ya daga ya saka wayar a hands-free, kuma yaki yayi magana har sai da Waira ta fara magana.
“Allo Ammir”
A dayan bangaren sai Ummi ta matso kusa ta karbi wayar ta saka hands-free saboda ta ji muryar ďanta.
“Ya aka yi?”
“Ina ta kira baka daga ba”
“Yanzu na daga ai”
“Baka son magana da ni?”
“Me yasa na daga wayar to?”
“Gashi nan kana bata fuska”
Ta fada ba dan ta ganshi ba, sai dan ta karanci hakan a muryarsa da yadda yake amsa mata. Ya nufi boutique dinsa ya tsaya gaban madubi yana kallon kansa, da gaske fuskarsa a hade take.
“Zan aje waya sai ka yi far'a sai na sake kira”
Ta fada. Jin haka sai ya saka ya sassauta fuskar yayi ya sauke numfashi.
“Wayar tana kusa da ke ko? Ita tace na ki fada min haka?”
Ummi ta yi saurin girgiza ma Waira kai.
“Aa Ummi tana dakinta”
“Ni na sauko ina falo”
Ya jimmm for some seconds sannan ya ce.
“Me mike son ki tambaye ni?”
“Abubuwa da yawa, na ce Ya Maleek ya kawo ni, sai yayi min ihu wai ba za a sake zuwa ba, kuma idan na sake yin maganarka ma sai ya min duka”
“Saboda shi ubanki ne?”
“Aa shi Ya Maleek ne”
“Baki da alaka da shi ai, ba shi da hujja”
“Shi yaron Ummi ne ai”
“Baki da alaka da Ummi baki da alaka da kowa a gidan nan, so babu wanda zai saka ki dole ko hana ki abun da kike so, idan ma akwai wannan to ni ne, domin ni na dauko ki daga daji, ni ne sikar zuwanki garin nan and that stupid house, remember?”
Ta kalli Ummi sannan ta daga masa kai.
“Yes”
“Good so no one has power over you, tambaye ni abun da kike son ki sani”
Ummi ta yi saurin rada mata a kunne.
“Zaka zo sai na tambaye ka?”
“No”
“Please”
“No”
“Abubuwa da yawa ne, ina son na sani zaka zo saboda ni?”
“Aa”
“Baka damuwa da matsalar kowa kai?”
Yayi shiru, ya saka hannunsa ya taba hancinsa ya runtse ido ya bude.
“Dole sai na zo wai?”
“Eh”
“Zaki iya tambayata a waya”
“Bana so a waya, kai baka da tausayi Ameer ko? Shiyasa ka tafi ka bar ni a lokacin da maciji ya cije ni a daji, ban manta ba i will hate you more”
“Zan zo”
Ya amsa ba tare da shiri ba.
“Yanzu?”
“No”
“Gobe ina zuwa school da safe”
“Zan same ki school din”
“Kasan ina ne?”
“Ki turo min address a waya”
“Okay zan aje waya”
“Good night”
“Good Night”
“Yeah Good Night”
Sai ta sake fada.
“Good night”
“Okay sai da safe”
Sai da ta yanke kiran sannan ya fito daga dakin ya jefar da wayar akan bed, shi yana da alot of questions da zai mata, sai dai hakan ba yana nufi ko da ya tafi ya shiga gidan ba sai dai ya tsaya daga wani gurin ta zo ta same shi.
“Bata manta ba, mata suna rike abun da yayi musu ciwo a zuciyarsu”
Ya fada yana tuna zancen da ta yi masa cewar ya barta a daji bayan maciji ya cijeta.
“Storyteller”
He said, sannan ya nufi bathroom dinsa.
UMMI's POV.
Ummi da mamaki take kallon Waira, bata taba tunanin tana da wayo ba irin yau, a yanzu ta gane Waira ta tashi daga karamar yarinya da take mata kallo zuwa baba mai wayo da basira. Domin bayan maganar farko data rada mata cewar zai zo ta tambaye bata sake ce mata komai ba, ita ta tsara masa komai.
“Baki taba fada mana cewar kin san Ameer ba Waira, ashe shi ya dauko ki ya saka ki a motar Nimra?”
“Ban san waya saka ni ba, amman dai na ganshi kuma ya gan ni, yana kallona a lokacin da maciji ya cijeni na yi ta neman taimakonsa be taimaka min ba har na suma ban san an saka ni a mota ba, ni dai na gani a wani guri tare da Sulem”
Ummi ta shafa kanta ta sumbaceta ta rumgumeta.
“Ina kaunarki Waira, yanzu kin san abun da nake so da ke, gobe idan kin tafi school, school bus ba zata dawo da ke ba, ina son ki roke shi ya kawo ki gidan nan, na san zai yi domin na lura kina da wani sirri a muryarki da mu'alamarki dake karya duk wata izza da fushi ko girman kai a gurin namiji, daman ko wace mace da yadda Allah ya halicceta, kin ga ni da ina kamarki farinjini na yi sosai da kiriniya, step father na ya sha wahala ta a lokacin har karyashi an yi saboda ni, Mamana kuma ba a magana Allah dai yayi mata rahama (Lallai kam dan mahaifin Deen da Deen sun sha duka saboda Zahra)”
Waira ta amsa.
“Toh Ummi, amman Ya Maleek ba zai yi ihu ba?”
“Ba zai yi ba, babu abun da nake bukata a yanzu kamar kusanci da ďana”
Ummi ta dago Waira daga jikinta.
“Gobe zan miki cake mai dadi ki tafi da shi”
“Okay”
Ta nufi upstairs tana jindadi zata ga Ameer a gobe ta yi masa tambayoyi akan abun da ya shige mata duhu.
She wake-up early saboda ta kwana rumgume da baby rabbit dinta da kuma tunanin haduwarta da Ameer. Tun asuba ta sauko kasa da zomonta ko wanke baki bata yi ba, ta nufi kitchen domin ta san Ummi ke shirya mata abun zuwa makaranta kuma tun da har ta fadi cewar zata yi mata cake. Ta leka Kitchen din kamar yadda ta saba sai ta samu Ummi da Mahmood a ciki yana taya ta aiki. Da kuzarinta ta shiga Kitchen din.
“Laaaa”
Ya juyo ya kalleta yana murmushi.
“Laa zaki ce yau ni nake taya Ummi aiki ko?”
Ya daga kai.
“Daddy ne ya raba mana aiki, yace yau idan na gobe Maleek ne, jibi Namra gata kuma ke, haka zamu yi ta yi har mu saba”
Ta juya ta kalli Ummi.
“Ummi Good Morning”
“Good Baby tafi ki wanke fuska ki yi wanka, zan hada miki tea yanzun nan kamin cake ya zama ready”
“Okay”
Ta juya ta fito daga kitchen din ta nufi stairs. hakan yayi daidai da shigowar Maleek falon, daman idan ya gama sallah azuba baya tashi a masallaci sai ya gama azkar dinsa, sannan yake shigowa gidan. Tsayawa ta yi sai da ya iso inda take ta gaishe shi kamar yadda ta Ummi ta koya mata.
“Good Morning”
Tsaye yayi yana kallonta sai ta sauke idonta kasa.
“Morning”
Ya amsa sannan ya wuce ya fara taka stairs din, bayansa ta bi, sai gashi ya tsaya ya juyo ya kalleta.
“Waye Ummi ta ce ki dauko waya a kira jiya da dare?”
“Malamina”
A take ta kirkiri karya ta fada masa abun da ba halinta ba. Domin bata yin karya mo matter what, a yanzun ma tana tsoron ya ce zai dake ta ne. Be ce mata komai ba ya juya ya haye sama, sannan ita ma ta shiga dakinta. Karfe bakwai da rabi school bus ta faka kofar gidan, sanin lokaci yayi ya saka Waira ta aje kofin tea da take sha ta ta dauki jakarta dake gefenta ta mike tsaye.
“Ummi time yayi”
Ummi ta so daga kujerarta ta matsa kusa da Waira ta sumbancin goshinta.
“Allah ya miki albarka, ga cake din na musamman ne na yi, yayi dadi sosai ki ci da yawa”
“Okay Ummi Thank you”
Ta karbi cake din ta nufi hanyar falo, Ummi kuma ta kalli Mahmood ta ce.
“Please fita ka fadawa driver bus din ba shi zai dawo da ita ba, za a zo a dauke ta ne”
Mahmood Ummi take yi ma magana amman Maleek ne yayi tambaya.