← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 170

Sashe 87

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajiya Jamila dake sanye da hijabi tana zaune gaban TV ta yi shiru for a seconds sannan ta ce.

“Gaskiya na fada masa, saboda ya bukaci na fada masa, kuma ya yi min ikirarin cewar idan na masa karya zai tsane ni, ba kuma zai sake yarda da ni ba, ba zan iya rusa wannan alakar dake tsakanina da Ameer ba, domin na fika sonsa, na san komai daren dadewa gaskiya zata bayyana”

“Da gaske kike yi? Ba duk gargadi da na yi miki?”

“Me yasa baka gargadi Zahra ba? Sai ni? Kana tunanin har yanzu kana da iko da ni? Ko kana tunanin zan manta irin butulcin da ka yi min bayan duk abin da na aikata saboda ka samu farinciki mu jidadin rayuwar aure na aikata? Amman duk baka duba wannan ba, a tsame ni a gidanka, ka raba ni da ďan da nake kallo a matsayin nawa, ďanta ruwan nonona ya taba zauna cikinsa, ďa daya tilo da na taba rumguma a hannuna a matsayin jaririna, ďan da duniya take kallo a matsayin ni na haife shi, kana tunanin duk zan manta da wannan? Ai kaima ka cancanci ka ji dacin da na ji”

“Idan har zaki iya fadawa Ameer gaskiya, to ba son gaskiya kike masa ba, kuma a yanzu na gode Allah da ya raba ni da ke tun wuri, kuma fada masa gaskiya ba zai canja komai ba, Ameer is still my son, babu wanda ya isa ya kwace hakan daga hannuna, har ita mai ikirarin uwarsa, na yi ma mijinta gargadi saboda ya ja mata kunne, idan kuma ba su ba, na san yadda zan yi da su all, and from today babu ke babu Ameer”

Ya yanke kiran ya nufi bangarensa yana takawa da karfi, kana ganinsa kasan ransa a bace yake. Ameer sai da ya kwatanta Daddy ya shige cikin sannan ya shiga bathroom dinsa ya wanke fuskarsa ya fito rike da towel yana goge fuskar. Boutique dinsa ya shiga ya tsaya a dakin yana kallon yadda Daddy ya zuba masa tufafin sakawa kamar shi ya fi kowa gata a duniya.

*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660 ki huta karanta na hakki*

Juyawa yayi kadan ya kalli kansa a katon madubin dake nuna har talkamin kafarsa. Zafin yana kirjinsa da idanuwansa, kansa yake kallo amman a badini gobensa yake hangowa, this is the most painful truth he has ever know gaskiya mai mugun daci da dafi a zuciyarsa. Hoton fuskar mahaifinsa dake jikin moton da Ummi ta ba shi yana ta dawo masa a ido yana ganin kansa a matsayin mahaifinsa. Ya jefar da tawul din a tsakar dakin ya fito kamshi na tsara shi ta ko'ina the women he thought is his step mom tana sakawa a gyara masa dakin a saka masa kamshi kamar yadda yake so saboda tasan abun da yake so kenan, kuma Daddy ya fada mata zaman lafiyarta ta yi ďansa abun da yake so.
Ya fito waje ya sauko falon ba tare da ya bar kowa ya ga fuskarsa ba, one of his fav Sis tana masa magana ya ki kulata ya fice daga falon. Cikin motarsa ya koma ya zauna ya dauko takardar yarjejeniyar ya sake karantawa countless times ya dauki hoton Deen ya kura masa ido, sai a yanzu ya lura sam baya kama da Daddy ta ko'ina, but how come be taba lura da hakan ba? Bude motar yayi ya fice rike da takardun bayan ya dauki wayarsa ya nufi bangaren Daddyn feel dizziness.

NAMRA POV.

Ta yi murmushi tana daidaita tsayuwarta.

“Mai jiki da sauki sosai”

“Maa Shaa Allah, Allah ya kara mata lafiya, ke fa ya kike?”

Shuraim ya tambaya a dayan bangaren.

“Ina nan kalau, saboda kana kusa ni, yaushe zaka sake shigowa kasan dai ba zaka wuce ba tare da mun sake ganin juna ba ko?”

“Zan zo hakan, ko dan ma yarinyar nan Waira, saboda na kasa manta yadda na barta a gidanku, tana ta kuka ta shiga damuwa, kanwarki ma na so na zo an dubata, amman ina tsoron yanayin da yan'uwanki ko iyayenki za su kalleni”

Iyakar kokarin da ta yi na danne abun da ta ji ne a lokacin da ya ambaci cewar zai so zuwa ko dan Waira.

“Ban gane ba, me ka gani a gurin iyayena kuma?”

“Sai na ga kamar ba jindadin zuwa na ba, bayan na gama bayyana musu ko ni waye, especially your Dad yanayin yadda yake amsa min ya nuna cewar ya san mahaifina, kuma kamar be yi maraba da ni ba”

Alamar mamaki ne ya cika fuskarta domin bata jin wannan ba, saboda ba a gabanta ya gaisa da su ba, kuma tashin hankalin da suka samu kansu a ciki na ciwon Nimra ya saka ba ta yi maganarsa da kowa ba.

“Ka fada masa wanin abun da be dace ba ne? Ko kuma akwai wani abu a nasabarka da be dace kowa ya sani ba?”

“To ban sani ba a halin yanzu, har sai na samu mahaifin mun yi magana da shi, amman ni ma san babu wata illa a nasabata sai dai kamin na tafi ina bukatar sake ganin ki gaskiya, kuma ina son ganin yarinyar nan please”

“Kana dai son ganinta, ba da ni ba”

“Both ke da ina ina mamarin ganinku, ita saboda na kwantar mata da hankali ta natsu, ke kuma saboda nawa hankalin ya kwanta, so please ki saka mana meeting point kuma ki zo min da ita”

“When?”

“Yau if possible, idan kuma ba zai samu ba zan hakura har zuwa gobe, ba dan haka ba babu abun da zai saka na sake kwana garin Abuja”

“Zan kiraka idan abun da kake bukata zai samu”

“Ganinki mai samuwa ne na sani, sai dai fitowa da Waira ne ba ni da tabbaci, amman dai ki min kokari please”

“Okay”

“That's my Babe Girl i love you ”

Ta samu kansa ta kasa amsa masa da i love you too kamar yadda ta saba sai sakon godiya data aika masa ta kashe wayar, ta juyo yana kallon Nimra dake bachi. Me yasa Abiey yayi masa haka shi ne abun da ya fara zuwa a ranta kamin ta fara jin kamar ta tsani Waira saboda yawan maganarta da Shuraim yake dan zuwan nan da ya yi. Daf da zata zauna aka turo kofar dakin sai ta fasa zaman ta kalli Maleek da ya shigo fuska babu walwala ba kuma zata ce ransa ne a bace ba, domin ba ta ga alamun haka ba, ya kusa cin karfin damuwarsa dan haka bata bayyana a fuskarsa ba, yana a wani yanayi da abu ne mai wahala ka bayyana halin da yake ciki, damuwa ce ko bakinciki ko rashin lafiya da jindadi ba kuma zaka ce yana cikin farinciki ba, haka kuma baka isa ka ce yana nishadi ba.

“Sannu da zuwa”

Da kai ya amsa mata ya zauna a kujerar dake fuskantar Nimra, yana kallon kanwarsa ta rame sosai kamar ba ita ba, har yanzu oxygen ne a bakinta da hancinta numfashinta na tafiya wahala kamar dai wanda yake daf da bankwana da duniya.

“Ya jikinta?”

“Da sauki, gashi har ta samu bachi, da bata iya bachi kuma likitan yana tsoron yayi mata allurar bachi saboda yanayinta, amman ga dukan alamu yanzu sauki ya fara zuwa”

Hannu ya kai ya shafa kanta da babu dankwali yana jin tausayinta, domin ta fada tarkon mutumen da ya tabbatar ko sama da kasa za su hade ba zai aureta ba, gashi tana ta wahala akansa. Namra ma kallonta take har sai da wayar Maleek tayi ringing sannan hankalinta ya koma gurinsa.

“Ina asibiti gurin Nimra”

“Akwai maganar da nake son mu yi mai muhimmanci Maleek, akwai abun da ya kamata ka sani”

Mahmood ya fada a dayan bangaren.

“Akan ciwon Ummi?”

“No akan Ameer”

“Me ya kuma ya faru?”

“I can't tell you on the phone, sai dai fada min inda kake ko kuma ka same ni”

“Kana ina?”

“King and his Kingdom”

“Okay gani nan zuwa”

Ya sauke wayar, gabansa na faduwa zuciyarsa na raya masa ko Ameer ya sake shirya wani abun ne, domin King and his Kingdom ba gurin zuwan Mahmood ba ne, it's a very right or appropriate place for rich kids like them amman ba gurin zuwansu ba ne, kara shi ma yana dan taba fita da abokansa sometimes amman Mahmood ya zama Mommy's boy, idan ya dade ya be dawo gida ba har kira take ta ji yana ina, not like Maleek da ta san baya son zaman gida saboda halinsa a can ba, duk da haka kuma ba zata yi bachi ba sai duka yaranta sun dawo gida. Waceaganar ce da ba zai iya fada masa ta waya ba? Shi ne dalilin karin kuzarin Maleek na fice daga asibitin ba tare da jiran kanwarsa ta farka ba...

©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
Ya shiga falon Daddy a wani yanayi da be taba shiga ba, wannan ne karon farko da yake jin wani abu mai kamar kunya da bakinciki saboda zai tunkari Daddy yayi magana da shi, tafiyarsa ma ta banbanta da yadda ya saba yinta. A kofar dakin Daddy ya tsaya ya share hawayen da suke masa zuba sannan ya kai hannu ya kwankwasa kofar ďakin sai kuma ya fasa ya duka a gurin ya dafe kansa hawayen da tsaya suka dawo suna masa zuba. Ganin yake kamar ba gane ba ne ace Daddy ba mahaifinsa ba ne, ya kuma kasa karbar karyar da zuciyarsa take masa. Sai da yayi da gaske sannan ya iya controlling kansa ya share hawayensa ya mike tsaye ya kwankwasa kofar dakin.

“Yes come in”

Gabansa na mugun faduwa ya tura kofar dakin ya shiga, kunyar da bata san ta ina ta fito ba ta lullube ya kasa kallon Daddy har ya zauna a couch, Daddy ya aje wayar hannunsa yana kallon Ameer cikin wani yanayi na tsoron da gargabar rasa ďansa.
Chapter 87 · 0% Book details