Sashe 111
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya amsa sannan ya sauke wayar zuciyarsa na mugun ƙuna, zafi kirjinsa yake masa ga bacin rai da be san na minene ba, ya busar da iskar bakinsa ya jingina jikin kujerar for some seconds sannan ya mike tsaye tare da mug din ya shiga falon, shigarsa ta yi daidai da saukowar Waira dake fadin.
“Dakin yayi kyau Ummi komai ya ji”
Kallon kawai yayi ya kawar da idonsa, yana kokarin danne abun da yake ji na bacin rai a zuciyarsa, to me zai saka ma ya damu bayan ya san ya daukarwa kansa alkawari ba zai sake damuwa da duk wani abu da zai shiga tsakaninta da Ameer ba.
“Lemme get my keys ta jira ni waje”
Yana fadar hakan ya nufi stairs, Ummi ta kalli Fiyya tana murmushi ta ce.
“Ki jira shi a waje zai zo ya kai ki yanzu nan”
“Toh na gode, sai da safenku”
Ta musu sallama ta fice, Ameer ya haur sama ya shiga dakinsa domin yin wanka, Waira kuma ta zauna a kusa da Ummi ta aje wayarta tana kallon Ummi wanda ta nufi kitchen. Maleek be dade ba ya sauko rike da keys din a lokacin Waira ce kawai zaune a falon tana ganinsa ta sha jinin jikinta ta sauke kai kasa. Yana saukowa gabanta na faduwa har ya iso inda take zaune, tsayawa yayi yana kallonta har ya bude baki yayi magana sai wata zuciyar ta tuna masa da alkawarin da ya dauka. Jin yana tsaye a kanta ya saka ta dago kanta ta kalleshi da idanuwanta masu daukar hankali, raunin dake cikin idonta ya baibaiye fuskarta ya dira zuciyar Maleek a madadin ya ji haushinta sai tausayinta ya dirar masa.
“Oh Ya Rabbi”
Kawai tausayinta yake, zuciyarta ta kasa natsuwa da alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, ta dayan bangaren kuma yana jin damuwa ganinta da Ameer. Numfashi yaja ya sauke da karfi sannan ya dauke kai ya fice daga falon.
Da hannu yayi ma Fiyya alama da ta shiga motar da yake nufota, sai ta isa gurin taja ta tsaya kwarjininsa na cikata, har sai da ya shiga motar sannan ta bude ta shiga. Ta natsu sosai fiye da yadda ta saba natsuwa idan tana tafiya da mutumen da bata sani ba, kwararran motsi sai ta kasa yi, tana son ya juya ta kalli inda yake ta kasa, daga ita har shi hankalinsu yana gurin titi har ya isa bakin gate din gidan. Son ya tabbatar ta sauka lafiya ya saka shi yin horn aka bude masa gate ya shiga har ciki ya faka motar harabar dake kusa da kofar falon, sai a lokacin ta samu damar kallonsa shi ma kuma saboda ta yi masa godiya ne.
“Thank you”
Be kawota arajin kansa ba, dan haka ba godiyarsa ce abun da yake bukata a gurinta ba a yanzu. Ko kallon inda take be yi ba balle ma ya amsa tana fita motar yayi gaba a makeken compound din gidan ya juya motarsa ya fice. Da gangan ya yi ta tafiyar da zata dauke shi lokaci be dawo gida ba, and he don't know why. Bayan kusan awa daya da rabi a titi finally ya iso bakin gate din gidansu yayi horn masu gadi suka bude masa gate. To his surprise sai ya samu Abiey tsaye yana lasa wayarsa hannunsa. Maleek na fakawa ya bude motar ya fito yana matsa key din hannunsa ya nufi gurin mahaifinsa.
“Abiey lafiya?”
Abiey ya dago ya kalleshi a karo na biyu bayan kallon da yayi masa a lokacin da yake shigowa cikin gidan.
“Me ka gani?”
“Kawai dai na ga kamar ba lafiya ba, fuskarka ta nuna akwai damuwa”
Abiey yaja dogon numfashi ya sauke.
“Damuwar gidan nan ba zata wuce ta mahaifiyarku ba...”
Kamin Abiey ya kai aya Maleek yayi karaf ya karbe yana juyawa ya jera tare da Abiey.
“Zuwan Ameer gidan nan ko? Ni ma bana son haka, sai kuma na kyale ne kawai saboda Ummi ta samu natsuwa da kwanciyar hankali, amman ina jin tsoron kar Ameer ya sake sakata cikin tashin hankali wata kila ba saboda kwanciyar hankalinta ya dawo, zai iya amfani da Waira ya cimma wsni burinsa ne sannan ya jefar da ita, na nunawa Ummi haka amman ta kasa fahimta sai kokarin ganin laifina take, alakarsa da Waira tana kokarin wuce gona da iri, ita bata da hankali da wayon da zata gane”
Abiey ya sauke wayar da yake latsa gaba daya yana kallon dansa da mamaki, domin Maleek ya bude cikinsa ne ba tare da ya sani ba, shi dai kawai yana neman abokin tattaunawa ne.
“A cikin zaman Ameer a gidan nan da kuma alakarsa da Waira wanne ya fi kona maka rai?”
Kai tsaye ya amsa.
“Alakarsa da Waira mana Abiey, gida ai yana da hakkin zama saboda ka amince masa kuma mahaifiyarsa tana ciki, amman miya kawo issues din Waira a ciki? Why her? Idan ya lalata mata rayuwa fa? Na nunawa Ummi haka amman ta kasa ganewa, ina tausayin yarinyar nan Abiey tausayi take ba ni, bana son alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, kawai dai ina dauke idona ne a yanzu saboda Ummi ta bukaci haka, but still ina jin kamar ba zan iya jurewa ba”
Maleek ya karashe maganar har wani furzar da numfashi yake saboda abun da yake ji a zuciyarsa. Da mugun mamaki da kuma tunani kala kala Abiey ke kallon dansa, this is the first time da ya zama mutum kamar kowa, yake jin kishi akan wani abu da ada can baya damunsa, wani abu da be taba samu muhalli a rayuwarsa ba. Ya dade da ganin canji a rayuwarsa ďansa, sai dai canjin ba irin wannan ba, abun da matarsa Zahra ta dade tana mafarkin faruwarsa da kuma tana jiran zuwansa.
“Kana jin ba dadi idan ka ganshi tare da ita right?”
“Yes kawai ina controlling kaina ne, if not Wallahi ko duka zan iya masa”
Abiey yayi murmushi yana jin dadin a ransa, hannunsa daya ya kai yana bubbuga kafadar Maleek.
“Karka damu, zan daukar masa mataki, ba zamu bari ya lalata rayuwar yarinya karama ba, kuma ya kamata mu maida hankali mu san waye iyayenta ko dan gaba”
Maleek ya sauke numfashi yana kallon wani gurin na dabam.
“Haka ne, amman dai for now kamata yayi mata ace ka yi duk wani abu da zai yanke hulda tsakaninsu, if ba haka ba shakuwa zata shiga kuma zai iya amfani da wannan damar ya cutar da ita”
“Haka ne, karka damu na san abun da zan yi, amman kai ma ya kamata ka rika kyautata mata, ka rika sake mata tana jin sanyinka, ita tunanin yana amfani da weakness dinta ne ya yana janta a jikinsa”
“No ni ba zan iya haka ba, ai sai ta raina ni, kuma na fi damuwa da alakarsu da Ameer ba wai dole sai ta saki jiki da ni ba”
Abiey yayi murmushi
“Ba zaka gane ba Maleek. Apart from wayar da ka tarar ina yi a yanzu ina magana da Doctor Hassan ya fada min abubuwan da ya kamata ace mahaifiyarka tana yi saboda lafiyarta amman taki, ban san yadda zan yi convince dinta ta yarda ba, musamman a yanzuda Ameer ya dawo gidan nan”
Abiey ya tattauna da shi akan abubuwa da yawa suka shafi Ummi, sai kusan ten Abiey ya shiga bangarensa Maleek kuma ya nufo bangaren Ummi. Yana shiga falon Waira ya fara cin karo da ita kwance a kujerar daya barta, sai dai wannan karon tana rumgume da zomonta ne, sai sharbar Bacci take kamar wacce ta yi wani aiki ta gaji. Tsaye yayi a kanta yana kallon fuskarta, bachi ma kyau yake mata kamar yadda idan tana farke take kara kyau da haiba. Wayarsa ya ciro ya shiga instagram for few seconds sannan ya dago kansa ya duba ko'ina na kusuwar falon, ganin shi kadai ne sai Waira ya ba shi kwarin guiwa fitowa daga Insta ya shiga camera ya saita wayar saitin fuskar Waira ya dauke ta hoto har sau biyu sannan ya maida wayar aljihunsa ya kai hannunsa ya buga gefen kujerar sai ta farka a firgice ta kalleshi.
“Tashi ki je daki ki kwanta”
“Dakin yayi kyau Ummi komai ya ji”
Kallon kawai yayi ya kawar da idonsa, yana kokarin danne abun da yake ji na bacin rai a zuciyarsa, to me zai saka ma ya damu bayan ya san ya daukarwa kansa alkawari ba zai sake damuwa da duk wani abu da zai shiga tsakaninta da Ameer ba.
“Lemme get my keys ta jira ni waje”
Yana fadar hakan ya nufi stairs, Ummi ta kalli Fiyya tana murmushi ta ce.
“Ki jira shi a waje zai zo ya kai ki yanzu nan”
“Toh na gode, sai da safenku”
Ta musu sallama ta fice, Ameer ya haur sama ya shiga dakinsa domin yin wanka, Waira kuma ta zauna a kusa da Ummi ta aje wayarta tana kallon Ummi wanda ta nufi kitchen. Maleek be dade ba ya sauko rike da keys din a lokacin Waira ce kawai zaune a falon tana ganinsa ta sha jinin jikinta ta sauke kai kasa. Yana saukowa gabanta na faduwa har ya iso inda take zaune, tsayawa yayi yana kallonta har ya bude baki yayi magana sai wata zuciyar ta tuna masa da alkawarin da ya dauka. Jin yana tsaye a kanta ya saka ta dago kanta ta kalleshi da idanuwanta masu daukar hankali, raunin dake cikin idonta ya baibaiye fuskarta ya dira zuciyar Maleek a madadin ya ji haushinta sai tausayinta ya dirar masa.
“Oh Ya Rabbi”
Kawai tausayinta yake, zuciyarta ta kasa natsuwa da alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, ta dayan bangaren kuma yana jin damuwa ganinta da Ameer. Numfashi yaja ya sauke da karfi sannan ya dauke kai ya fice daga falon.
Da hannu yayi ma Fiyya alama da ta shiga motar da yake nufota, sai ta isa gurin taja ta tsaya kwarjininsa na cikata, har sai da ya shiga motar sannan ta bude ta shiga. Ta natsu sosai fiye da yadda ta saba natsuwa idan tana tafiya da mutumen da bata sani ba, kwararran motsi sai ta kasa yi, tana son ya juya ta kalli inda yake ta kasa, daga ita har shi hankalinsu yana gurin titi har ya isa bakin gate din gidan. Son ya tabbatar ta sauka lafiya ya saka shi yin horn aka bude masa gate ya shiga har ciki ya faka motar harabar dake kusa da kofar falon, sai a lokacin ta samu damar kallonsa shi ma kuma saboda ta yi masa godiya ne.
“Thank you”
Be kawota arajin kansa ba, dan haka ba godiyarsa ce abun da yake bukata a gurinta ba a yanzu. Ko kallon inda take be yi ba balle ma ya amsa tana fita motar yayi gaba a makeken compound din gidan ya juya motarsa ya fice. Da gangan ya yi ta tafiyar da zata dauke shi lokaci be dawo gida ba, and he don't know why. Bayan kusan awa daya da rabi a titi finally ya iso bakin gate din gidansu yayi horn masu gadi suka bude masa gate. To his surprise sai ya samu Abiey tsaye yana lasa wayarsa hannunsa. Maleek na fakawa ya bude motar ya fito yana matsa key din hannunsa ya nufi gurin mahaifinsa.
“Abiey lafiya?”
Abiey ya dago ya kalleshi a karo na biyu bayan kallon da yayi masa a lokacin da yake shigowa cikin gidan.
“Me ka gani?”
“Kawai dai na ga kamar ba lafiya ba, fuskarka ta nuna akwai damuwa”
Abiey yaja dogon numfashi ya sauke.
“Damuwar gidan nan ba zata wuce ta mahaifiyarku ba...”
Kamin Abiey ya kai aya Maleek yayi karaf ya karbe yana juyawa ya jera tare da Abiey.
“Zuwan Ameer gidan nan ko? Ni ma bana son haka, sai kuma na kyale ne kawai saboda Ummi ta samu natsuwa da kwanciyar hankali, amman ina jin tsoron kar Ameer ya sake sakata cikin tashin hankali wata kila ba saboda kwanciyar hankalinta ya dawo, zai iya amfani da Waira ya cimma wsni burinsa ne sannan ya jefar da ita, na nunawa Ummi haka amman ta kasa fahimta sai kokarin ganin laifina take, alakarsa da Waira tana kokarin wuce gona da iri, ita bata da hankali da wayon da zata gane”
Abiey ya sauke wayar da yake latsa gaba daya yana kallon dansa da mamaki, domin Maleek ya bude cikinsa ne ba tare da ya sani ba, shi dai kawai yana neman abokin tattaunawa ne.
“A cikin zaman Ameer a gidan nan da kuma alakarsa da Waira wanne ya fi kona maka rai?”
Kai tsaye ya amsa.
“Alakarsa da Waira mana Abiey, gida ai yana da hakkin zama saboda ka amince masa kuma mahaifiyarsa tana ciki, amman miya kawo issues din Waira a ciki? Why her? Idan ya lalata mata rayuwa fa? Na nunawa Ummi haka amman ta kasa ganewa, ina tausayin yarinyar nan Abiey tausayi take ba ni, bana son alakar dake shiga tsakaninta da Ameer, kawai dai ina dauke idona ne a yanzu saboda Ummi ta bukaci haka, but still ina jin kamar ba zan iya jurewa ba”
Maleek ya karashe maganar har wani furzar da numfashi yake saboda abun da yake ji a zuciyarsa. Da mugun mamaki da kuma tunani kala kala Abiey ke kallon dansa, this is the first time da ya zama mutum kamar kowa, yake jin kishi akan wani abu da ada can baya damunsa, wani abu da be taba samu muhalli a rayuwarsa ba. Ya dade da ganin canji a rayuwarsa ďansa, sai dai canjin ba irin wannan ba, abun da matarsa Zahra ta dade tana mafarkin faruwarsa da kuma tana jiran zuwansa.
“Kana jin ba dadi idan ka ganshi tare da ita right?”
“Yes kawai ina controlling kaina ne, if not Wallahi ko duka zan iya masa”
Abiey yayi murmushi yana jin dadin a ransa, hannunsa daya ya kai yana bubbuga kafadar Maleek.
“Karka damu, zan daukar masa mataki, ba zamu bari ya lalata rayuwar yarinya karama ba, kuma ya kamata mu maida hankali mu san waye iyayenta ko dan gaba”
Maleek ya sauke numfashi yana kallon wani gurin na dabam.
“Haka ne, amman dai for now kamata yayi mata ace ka yi duk wani abu da zai yanke hulda tsakaninsu, if ba haka ba shakuwa zata shiga kuma zai iya amfani da wannan damar ya cutar da ita”
“Haka ne, karka damu na san abun da zan yi, amman kai ma ya kamata ka rika kyautata mata, ka rika sake mata tana jin sanyinka, ita tunanin yana amfani da weakness dinta ne ya yana janta a jikinsa”
“No ni ba zan iya haka ba, ai sai ta raina ni, kuma na fi damuwa da alakarsu da Ameer ba wai dole sai ta saki jiki da ni ba”
Abiey yayi murmushi
“Ba zaka gane ba Maleek. Apart from wayar da ka tarar ina yi a yanzu ina magana da Doctor Hassan ya fada min abubuwan da ya kamata ace mahaifiyarka tana yi saboda lafiyarta amman taki, ban san yadda zan yi convince dinta ta yarda ba, musamman a yanzuda Ameer ya dawo gidan nan”
Abiey ya tattauna da shi akan abubuwa da yawa suka shafi Ummi, sai kusan ten Abiey ya shiga bangarensa Maleek kuma ya nufo bangaren Ummi. Yana shiga falon Waira ya fara cin karo da ita kwance a kujerar daya barta, sai dai wannan karon tana rumgume da zomonta ne, sai sharbar Bacci take kamar wacce ta yi wani aiki ta gaji. Tsaye yayi a kanta yana kallon fuskarta, bachi ma kyau yake mata kamar yadda idan tana farke take kara kyau da haiba. Wayarsa ya ciro ya shiga instagram for few seconds sannan ya dago kansa ya duba ko'ina na kusuwar falon, ganin shi kadai ne sai Waira ya ba shi kwarin guiwa fitowa daga Insta ya shiga camera ya saita wayar saitin fuskar Waira ya dauke ta hoto har sau biyu sannan ya maida wayar aljihunsa ya kai hannunsa ya buga gefen kujerar sai ta farka a firgice ta kalleshi.
“Tashi ki je daki ki kwanta”