Sashe 29
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shine abun da ya fada ya aje telephone din, ya sake zaunawa wannan karon kofar shigowar yake kallon. Faruk be shigo office din ba sai takwas da rabi, ciki tsoro da fargaba ya shigo sanin waye Ameer zai iya cewa ya masa laifi, domin tun kamin ya shigo office dina ka fada masa Ameer na nemansa kuma shigowar safiya yayi. Da katinsa yayi amfani ya bude kofar sannan ya shigo Office din dake dauke da kyamarorin tsaro, kamar yadda ko wane Office yake. Da ido Ameer ya fara tsare shi sannan ya mike tsaye ya dauki pen din dake gurin ya yagi diary ya rubuta masa numbers dinsa duka biyu ya mika masa, da kamar tsoro Faruk din ya karasa ya karba.
“Ka karbi kudi gurin Cashier ka yi welcome back din layukan”
“Okay Sir”
Amsa da sauri yana jin sanyi sanyi a ransa ya juya da sauri ya fice, fridge Ameer ya sake budewa ya dauki gorar ruwa ya fice daga office.
MALEEK POV.
Sun samu Abiey a Station din yana jiran isowarsu, da gangan ya bari aka kama Nimra saboda ta san ransa ya bace kuma ta kiyaye sake aikata irin kuskure a gaba, ta wani bangaren kuma yana ganin kamar bata da laifi domin gani yake Ummi ce ta shirya mata haka saboda ta samawa Ameer mafita. Office din CP din aka shiga da su, yadda aka kawata dakin ba dan tarin hotuna da awards da kuma littafai da suke gurin ba sai ka rabtse ba Office ba ne, sanyin Ac ta ko'ina ga wani madaidaicin tv da aka saka a gafe bayan na'urar sanyaya ruwan sanyi da zafi a suke gefe daya. Kusan kamar hira Maleek ya samu mahaifinsa na yi da CP din da suke ganinsa kamar dan'uwan Abiey saboda shakuwa da suka yi tun kamin a kawo shi Abuja a matsayin CP sun san juna shi da Abiey.
Nimra ta kasa kallon inda mahaifinta yake ma balle ta karasa ta zauna a inda CP yake nuna mata.
“Ka kyaleta a nan ai duk ita ta jawa mutane matsala”
CP yayi murmushi yana kallon yarinyar da zai iya kiranta da yarsa daman bata wuce sa'ar yarsa ba.
“Yaran ne sai hakuri, kullum cikin janyo magana suke, zauna... Wannan... Nimra tambaya zan miki”
Ta zauna daker har lokacin kuka take marar sauti, kamin CP ya fara magana Abiey ya kalli Maleek ya ce.
“Ummi ce ta maka umarnin amsa cewar kai ka karbi motarta?”
Maleek ya girgiza kai.
“Aa saboda ni din ne dai”
Abiey ya kalli CP daman tun kan a iso da su aka fada ma CP abun da Maleek yayi shi kuma ya fadawa Mahaifinsa.
“Shashanci ne, ba shi ya aikata abun nan, kawai yana kokarin kare yar'uwarsa ne, Maleek ba shi da matsalar shiga sha'anin da babu ruwansa ko kuma janyo magana, ita ma kuma yanzu ne ta zama haka da can ba haka take ba”
From A to Z Nimra ta bada labarin abun da ya faru ciki har da haduwarsu, da adadin kudin data ba shi da kuma Alert din da ta gani na kudin da aka cire. CP ya girgiza kai Abiey kuma ya tabe baki.
“This is serious issues to shi yaron yana ina yanzu”
“Ban san inda yake ba Wallahi”
Ta amsa tana kuka, sai ya mika mata takardar da biro.
“Rubuta mana number da kika ba shi a nan zamu binciko inda yake, idan kuma kin san inda zamu ganshi ki fada mana”
“Idan ma an fada muku ai ba kamashi zaka yi CP sai dai ka bugawa Mahaifinsa ka fada masa ya boye dansa”
Cewar Abiey CP ya kyalkyale da dariya.
“Alhaji Aliyu kenan, to ai rayuwar duk haka take tafiya dole kowa ya ci Alfarmar, kasan shi arziki ba karyar ba ne ko da baka mutuncin da mutum balle kuma ana yi, kai ma yanzu da aka turo min case din nan Abuja da bayanin yarka ai kiranka na yi a waya na fada maka, kuma da baka aminta ba da Police ba su shiga sun kamata ba, so abun ya zama na gida ne gaba daya, sa'arku daya daga kai har shi Mr Bashir din yarinyar bata mutu ba, kuma babu wani abu da aka gani a tare da ita idan ba cizon maciji ba kuma Alhamdulillah tana asibitin a yanzu haka karkashin kulawar likitoci”
Abiey ya sauke ajiyar zuciya.
“Ina ya dauko yarinyar kuma?”
“To wannan kuma shi kadai zai iya amsa mana, amman dai yarinyar wata kala ce tun daga yanayin hoton da na nuna maka idan ka kalleta zaka ga yadda tufafin jikinta ma suka banbanta da mu”
“Ka kira mahaifinsa ka fada masa abun da ďansa ya sake aikatawa”
“Kana hanyar zuwa na kira wayarsa ban samu ba, amman anjima zan sake gwadawa ko kuma na aika masa da sako”
Abiey ya mike tsaye sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin aljihunsa mai dan dama ya dora saman teburin CP.
“Zan tafi da ita gida idan ya dawo ya fadi inda ya dauko yarinyar zan dawo”
CP ma tsaye yayi da katon cikinsa.
“Kwana biyu kana ta zirya CID kuma be kamata ana ganinka a nan ba, indai ba abun ya fi karfin yadda nake tunani ba, to ba sai ka dawo ba zan iya rufe case din na san shi ma Mr Bashir haka zai bukata, kuma hakan zai fi tun da abun ya zama duk gida ne, idan ya fada mana inda yarinyar take zamu maida ita gurin iyayenta then case closed”
Abiey ya mika masa hannu suka gaisa.
“Thank You, when you done with the case Maleek ko Mahmood zai kawo maka cash”
“Godiya nake, a sauka lafiya, Nimra sai a kiyaye gaba ko?”
Ya karasa yana kallon Nimra, sai ta daga masa kai ta juya ta bi bayan mahaifinta. Motarsa dabam direba ke janshi ita da Maleek suka shiga mota daya. Kasa kallon inda Maleek yake ta yi har suka isa gida daman ta san shi ba zai ce mata komai ba, ita kuma bata san abun da zata fada masa ba.
Su kadai suka isa gida, Maleek na faka mota Nimra ta fita ta rigashi shiga falon, kusan cin karo suka yi da Namra da fuskarta ke dauke da tashin hankali, tana ganin yar'uwarta ta rumgume ta da sauri domin bata san abun da yake faruwa ba sai da Mahmood ya kira a waya ya sanar mata a dole ta bar gurin aikinta ta dawo gida.
“Oh ya Rabbb Thank You, lafiya kike?”
“Lafiya kalau ina Ummi?”
“Tana ciki bachi take Mahmood yace min bata jindadi”
Maleek na jin hakan sai ya haura saman ya tura dakin mahaifiyarsa a hankali ya shiga, har kusa da gadonta ya isa ya daga blanket din da ta lulluba da shi ya kalli fuskarta ganin bachin take ya saka ya maida blanket din ya fito tare da ja mata kofar...
Kamar wadanda aka yi ma mutuwa haka suka wuni a gidan, sai dai Ummi ta dan samu sauki saboda ganin Nimra ta dawo lafiya ba tare da an tsareta ba, amman babu walwala a fuskokinsu, Namra da Mahmood sai tsinewa Ameer suke, Ummi ta kasa cewa komai likewise Nimra ma bata iya yaba masa ko aibantashi.
Bayan Sallah Isha'i Nimra na dakinta zaune Ummi ta shigo, ganin mahaifiyarta ya saka ta aje wayar dake hannunta ta share hawayenta.
“Kiransa kike yi?”
“Me zai saka na kira butulu Ummi? Mutumen dake son jefa rayuwata a cikin hatsari”
“Amman kin damu da shi”
Ta dauke kai daga barin kallon Ummi ta kasa cewa komai, Hajiya Zahra ta zauna kusa da ita kamin tace komai Nimra ta ce.
“Abiey na turawa sakon ban hakuri”
“Ba ni labarin yadda kuka hada har shakuwa ta shiga tsakaninku?”
Ummi ta tambaya ba tare da ta kalleta ba a lokacin da Nimra ta dago ta kalleta sai ta ga ba ita Ummi ke kallo ba. Ko ace wadannan abubuwan ba su faru ba ba zata iya boye mata komai ba, balle kuma yanzu da abubuwan suka zo mata a haka.
“Na hadu da shi a gurin da na saba zama ina hutawa tare da kawata, busar sarewar sa muka fara ji, sai na leka na duba shi...... ”
Daga haka ta fara labarta mata haduwarsu. Ummi ta maida hawayen dake son taruwa a idonta ta kalli Nimra.
“Nimra zaki iya bin umarnina?”
“Zan bi Ummi”
Ummi ta kama hannayenta ta rike.
“Ina son ki fita hanyar yaron nan, kar wata alaka ta sake shiga tsakaninku, ko kallonsa karki sake yi, matukar kina son mu zauna lafiya da ke a gidan nan, kuma kina kallon yadda mahaifinki ya dauki fushi idan har kina son faranta masa rai dole ne ki gujewa Ameer, kuma kin fi kowa sanin abun da yayi ma dan'uwanki saboda haka ko tunaninsa bana son na ga kina yi”
Kamar wanda aka yi shokin Nimra ta ji, sai dai hakan be hanata daukarwa mahaifiyarta alkawarin da bata da tabbacin ko zata iya cika mata shi.
“Toh Ummi, ba zan sake ba”
“Allah ya miki albarka”
“Ameen”
Ta amsa sannan ta bi Ummi da kallo har ta fice daga dakin.
AMEER POV.
Yana isowa gida Momy ta tarbe shi da zancen mahaifinsa yana son ganinsa.
“Lafiya?”
“Ban sani ba, amman ina kyautata zaton haka, ya kira wayar Office aka ce ka fito ya kira ni na fada masa ban same ka a gidan ba, kuma wayoyinka idan an kira duka a kashe”
“Alright”
Ya juya ya koma cikin motar zuciyarsa bata kawo masa komai ba sai lamarin Nimra. Kuma ya canka daidai domin yana isa Asibitin Daddy ya ce masa.
“Be honest with me, karka min karya”
Ya gyara zamansa yana kallon Daddy.
“Miya faru?”
“Miye tsakaninka da kanwar abokinka wanda kuka samu matsala?”
Kawai dan Daddy yace masa ya fadi gaskiya ne, kuma ya san idan yace masa to be honest yana nufin tsantsar gaskiyar.
“Ka karbi kudi gurin Cashier ka yi welcome back din layukan”
“Okay Sir”
Amsa da sauri yana jin sanyi sanyi a ransa ya juya da sauri ya fice, fridge Ameer ya sake budewa ya dauki gorar ruwa ya fice daga office.
MALEEK POV.
Sun samu Abiey a Station din yana jiran isowarsu, da gangan ya bari aka kama Nimra saboda ta san ransa ya bace kuma ta kiyaye sake aikata irin kuskure a gaba, ta wani bangaren kuma yana ganin kamar bata da laifi domin gani yake Ummi ce ta shirya mata haka saboda ta samawa Ameer mafita. Office din CP din aka shiga da su, yadda aka kawata dakin ba dan tarin hotuna da awards da kuma littafai da suke gurin ba sai ka rabtse ba Office ba ne, sanyin Ac ta ko'ina ga wani madaidaicin tv da aka saka a gafe bayan na'urar sanyaya ruwan sanyi da zafi a suke gefe daya. Kusan kamar hira Maleek ya samu mahaifinsa na yi da CP din da suke ganinsa kamar dan'uwan Abiey saboda shakuwa da suka yi tun kamin a kawo shi Abuja a matsayin CP sun san juna shi da Abiey.
Nimra ta kasa kallon inda mahaifinta yake ma balle ta karasa ta zauna a inda CP yake nuna mata.
“Ka kyaleta a nan ai duk ita ta jawa mutane matsala”
CP yayi murmushi yana kallon yarinyar da zai iya kiranta da yarsa daman bata wuce sa'ar yarsa ba.
“Yaran ne sai hakuri, kullum cikin janyo magana suke, zauna... Wannan... Nimra tambaya zan miki”
Ta zauna daker har lokacin kuka take marar sauti, kamin CP ya fara magana Abiey ya kalli Maleek ya ce.
“Ummi ce ta maka umarnin amsa cewar kai ka karbi motarta?”
Maleek ya girgiza kai.
“Aa saboda ni din ne dai”
Abiey ya kalli CP daman tun kan a iso da su aka fada ma CP abun da Maleek yayi shi kuma ya fadawa Mahaifinsa.
“Shashanci ne, ba shi ya aikata abun nan, kawai yana kokarin kare yar'uwarsa ne, Maleek ba shi da matsalar shiga sha'anin da babu ruwansa ko kuma janyo magana, ita ma kuma yanzu ne ta zama haka da can ba haka take ba”
From A to Z Nimra ta bada labarin abun da ya faru ciki har da haduwarsu, da adadin kudin data ba shi da kuma Alert din da ta gani na kudin da aka cire. CP ya girgiza kai Abiey kuma ya tabe baki.
“This is serious issues to shi yaron yana ina yanzu”
“Ban san inda yake ba Wallahi”
Ta amsa tana kuka, sai ya mika mata takardar da biro.
“Rubuta mana number da kika ba shi a nan zamu binciko inda yake, idan kuma kin san inda zamu ganshi ki fada mana”
“Idan ma an fada muku ai ba kamashi zaka yi CP sai dai ka bugawa Mahaifinsa ka fada masa ya boye dansa”
Cewar Abiey CP ya kyalkyale da dariya.
“Alhaji Aliyu kenan, to ai rayuwar duk haka take tafiya dole kowa ya ci Alfarmar, kasan shi arziki ba karyar ba ne ko da baka mutuncin da mutum balle kuma ana yi, kai ma yanzu da aka turo min case din nan Abuja da bayanin yarka ai kiranka na yi a waya na fada maka, kuma da baka aminta ba da Police ba su shiga sun kamata ba, so abun ya zama na gida ne gaba daya, sa'arku daya daga kai har shi Mr Bashir din yarinyar bata mutu ba, kuma babu wani abu da aka gani a tare da ita idan ba cizon maciji ba kuma Alhamdulillah tana asibitin a yanzu haka karkashin kulawar likitoci”
Abiey ya sauke ajiyar zuciya.
“Ina ya dauko yarinyar kuma?”
“To wannan kuma shi kadai zai iya amsa mana, amman dai yarinyar wata kala ce tun daga yanayin hoton da na nuna maka idan ka kalleta zaka ga yadda tufafin jikinta ma suka banbanta da mu”
“Ka kira mahaifinsa ka fada masa abun da ďansa ya sake aikatawa”
“Kana hanyar zuwa na kira wayarsa ban samu ba, amman anjima zan sake gwadawa ko kuma na aika masa da sako”
Abiey ya mike tsaye sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin aljihunsa mai dan dama ya dora saman teburin CP.
“Zan tafi da ita gida idan ya dawo ya fadi inda ya dauko yarinyar zan dawo”
CP ma tsaye yayi da katon cikinsa.
“Kwana biyu kana ta zirya CID kuma be kamata ana ganinka a nan ba, indai ba abun ya fi karfin yadda nake tunani ba, to ba sai ka dawo ba zan iya rufe case din na san shi ma Mr Bashir haka zai bukata, kuma hakan zai fi tun da abun ya zama duk gida ne, idan ya fada mana inda yarinyar take zamu maida ita gurin iyayenta then case closed”
Abiey ya mika masa hannu suka gaisa.
“Thank You, when you done with the case Maleek ko Mahmood zai kawo maka cash”
“Godiya nake, a sauka lafiya, Nimra sai a kiyaye gaba ko?”
Ya karasa yana kallon Nimra, sai ta daga masa kai ta juya ta bi bayan mahaifinta. Motarsa dabam direba ke janshi ita da Maleek suka shiga mota daya. Kasa kallon inda Maleek yake ta yi har suka isa gida daman ta san shi ba zai ce mata komai ba, ita kuma bata san abun da zata fada masa ba.
Su kadai suka isa gida, Maleek na faka mota Nimra ta fita ta rigashi shiga falon, kusan cin karo suka yi da Namra da fuskarta ke dauke da tashin hankali, tana ganin yar'uwarta ta rumgume ta da sauri domin bata san abun da yake faruwa ba sai da Mahmood ya kira a waya ya sanar mata a dole ta bar gurin aikinta ta dawo gida.
“Oh ya Rabbb Thank You, lafiya kike?”
“Lafiya kalau ina Ummi?”
“Tana ciki bachi take Mahmood yace min bata jindadi”
Maleek na jin hakan sai ya haura saman ya tura dakin mahaifiyarsa a hankali ya shiga, har kusa da gadonta ya isa ya daga blanket din da ta lulluba da shi ya kalli fuskarta ganin bachin take ya saka ya maida blanket din ya fito tare da ja mata kofar...
Kamar wadanda aka yi ma mutuwa haka suka wuni a gidan, sai dai Ummi ta dan samu sauki saboda ganin Nimra ta dawo lafiya ba tare da an tsareta ba, amman babu walwala a fuskokinsu, Namra da Mahmood sai tsinewa Ameer suke, Ummi ta kasa cewa komai likewise Nimra ma bata iya yaba masa ko aibantashi.
Bayan Sallah Isha'i Nimra na dakinta zaune Ummi ta shigo, ganin mahaifiyarta ya saka ta aje wayar dake hannunta ta share hawayenta.
“Kiransa kike yi?”
“Me zai saka na kira butulu Ummi? Mutumen dake son jefa rayuwata a cikin hatsari”
“Amman kin damu da shi”
Ta dauke kai daga barin kallon Ummi ta kasa cewa komai, Hajiya Zahra ta zauna kusa da ita kamin tace komai Nimra ta ce.
“Abiey na turawa sakon ban hakuri”
“Ba ni labarin yadda kuka hada har shakuwa ta shiga tsakaninku?”
Ummi ta tambaya ba tare da ta kalleta ba a lokacin da Nimra ta dago ta kalleta sai ta ga ba ita Ummi ke kallo ba. Ko ace wadannan abubuwan ba su faru ba ba zata iya boye mata komai ba, balle kuma yanzu da abubuwan suka zo mata a haka.
“Na hadu da shi a gurin da na saba zama ina hutawa tare da kawata, busar sarewar sa muka fara ji, sai na leka na duba shi...... ”
Daga haka ta fara labarta mata haduwarsu. Ummi ta maida hawayen dake son taruwa a idonta ta kalli Nimra.
“Nimra zaki iya bin umarnina?”
“Zan bi Ummi”
Ummi ta kama hannayenta ta rike.
“Ina son ki fita hanyar yaron nan, kar wata alaka ta sake shiga tsakaninku, ko kallonsa karki sake yi, matukar kina son mu zauna lafiya da ke a gidan nan, kuma kina kallon yadda mahaifinki ya dauki fushi idan har kina son faranta masa rai dole ne ki gujewa Ameer, kuma kin fi kowa sanin abun da yayi ma dan'uwanki saboda haka ko tunaninsa bana son na ga kina yi”
Kamar wanda aka yi shokin Nimra ta ji, sai dai hakan be hanata daukarwa mahaifiyarta alkawarin da bata da tabbacin ko zata iya cika mata shi.
“Toh Ummi, ba zan sake ba”
“Allah ya miki albarka”
“Ameen”
Ta amsa sannan ta bi Ummi da kallo har ta fice daga dakin.
AMEER POV.
Yana isowa gida Momy ta tarbe shi da zancen mahaifinsa yana son ganinsa.
“Lafiya?”
“Ban sani ba, amman ina kyautata zaton haka, ya kira wayar Office aka ce ka fito ya kira ni na fada masa ban same ka a gidan ba, kuma wayoyinka idan an kira duka a kashe”
“Alright”
Ya juya ya koma cikin motar zuciyarsa bata kawo masa komai ba sai lamarin Nimra. Kuma ya canka daidai domin yana isa Asibitin Daddy ya ce masa.
“Be honest with me, karka min karya”
Ya gyara zamansa yana kallon Daddy.
“Miya faru?”
“Miye tsakaninka da kanwar abokinka wanda kuka samu matsala?”
Kawai dan Daddy yace masa ya fadi gaskiya ne, kuma ya san idan yace masa to be honest yana nufin tsantsar gaskiyar.