Sashe 65
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta fara lekowa ta karewa falon kallo ta ga babu kowa sai Ummi da Nimra sannan ta fito da sauri ta nufi gurin Ummi ta zauna a kasa dayan side din da Nimra take zaune tana kallon Nimra da idonta yake rufe tana zubar da hawaye.
“Kalli wacce ta rasa iyaye da yan'uwa da abokai da gari, ta rasa abinci da masu jin kalar yarenta ta bata mutu ba ta rayu tare da mu, sai ke ce zaki mutu dan kin rasa saurayi? Karki bari shaidan ya sharin zuciya su rinjaye ki Nimra”
Nimra ta bude ido ta kalli Waira take leken fuskarta, murmushi karfin hali Nimra ta yi mata sai Waira ta saka hannu ta fara share mata hawayenta, ta mika hannunta ta kama hannun Nimra ta rike ba dan komai ba sai dan ta san abun da yake faruwa, ta kwanatar da kanta a jikin Ummi kamar yadda na Nimra yake kwance. Ummi ta girgiza kai tunanin Ameer da kalamansa sun hanata sukuni, furucinsa na cewar saboda be san dadin uwa ba shi ke nuna be san muhimmancinta ba ya matukar tsaya mata a rai. Me aka fada masa? Uwarsa ta mutu? Shigowar Maleek ya saka ta share hawayenta ta kalleshi sa'insar da sukayi a dazun da Ameer take ta gani a idonta.
“Treatment zaka mata ka bata maganin da ya kamata”
“Ban taba mata treatment ba”
“Ka fara daga yau, kuma ban ce ka fada mata ko da kalma matar dadi ba balle har hannunka ya sake kaiwa a jikinta, Namra rikata ku tafi dakinta ki hada mata ruwa ta gasa jikinta zan hada mata wani abun ci a yanzu”
Ummi ta karasa tana kallon Namra wacce ta amsa mata da kai ta rika yar'uwarta suka mike tsaye. Waira ta bude ido da sauri tana kallon Nimra.
“Ta sanshi i know him... Waira ta san shi ta gane shi ta san shi”
Haka take ta fada da sauri tana nuna Nimra, daga Ummi har Maleek dake tsaye ba su fahimci abun da take nufi ba, Ummi kuma bata da lokacin tsayawa ta fahimceta a yanzu balle har ta gyara mata abun da take furtawa. Da ido Maleek ya harare a tunaninsa zata fara ba bada labarin abun da ya faru a school dinsu ne a yau, sai ta yi tsit kamar bata gurin.
“Bari na je na siyo magani”
Maleek ya fada sannan ya juya ya koma ta kofar falon da ya shigo. Waira ta bi Nimra da kallo har sai da suka haye sama gaba daya sannan ta dauke idonta ta dawo da su gurin Ummi.
“Ummi...”
Ummi ta kalleta wasu hawayen suna tarar mata a ido.
“Ummi miyasa Ummi ba zata bari Nimra ta aure shi ba”
“Saboda wani abubuwa da yawa tashi ki je ki cire uniform dinki”
Ta tashi ta nufi upstarts, sai kuma ta juyo.
“Ummi... Meyasa Ummi ba zata fadawa Abiey tana son mijin Nimra ba?”
Ummi bata bi ta kan maganar ba, domin tana cikin damuwa a yanzu.
“Na ce ki tafi ki canja uniform dinki”
Waira ta juya ta karasa hayewa sama, Ummi kuma ta cire hijabinta ta kwanta akan kujera tana ta addu'ar samun saukin zuciya. Waira na shiga dakinta wanka ne abun da ta fara yi sannan ta fito ta saka wando da riga ta sauko kasa bata samu kowa a falon ba sai motsin da take ji a kitchen, hakan ya saka ta nufi kitchen kai tsaye ta leka sai ga ta samu Ummi a tsaye.
“Ummi ta canja”
Ta fada tana shafa tufafin jikinta, Ummi ta juyo ta kalleta tana jin kamar zuciyarta zata tsage.
“Ummi. Meyasa Ummi ba fada fadawa Abiey bata da lafiya?”
“Lafiyata kalau tafi falo ki zauna zan hada miki tea yanzu ke da Nimra”
A maimakon ta juya ta fita kamar yadda Ummi ta bukata sai ta rugo da gudu ta rumgume Ummi ta fashe da kuka.
“Waira tana son Ummi”
Ummi ta shafa bayanta..
“Ya isa, bana son jin kuka kowa a yanzu je ki zauna zan kawo miki tea kamin mai lessons dinki ya zo kin ji? Ni ma ina sonki”
Ba dan ta so ba ta bar jikin Ummi ta fito falo ta zauna ta takure guri daya kamar bakuwa, tana kallon Maleek ya shigo ya haura sama zuwa dakin Nimra, aka sake bude kofar Dr ta shigo tare da Jabir hankalinta a tashe.
“Ina Zahra take?”
Ummi na jin muryar Dr Zainab ta fito daga kitchen din ta nufota ta rumgume tana jin wani sanyi sanyi a ranta. Jabir kuma ya nufi Waira dake ta sharar kwalla.
“Waya taba ki?”
“Ummi zata mutu...”
Yayi saurin rufe mata baki, a zatonsa kuka da ta ga Ummi tana yi ne ya saka ta tsorata har take furta haka.
“Subhanallah, ki dina fadar hakan ba abubuwa ne akwai suka faru kuma komai zai wuce kinji?”
Ta girgiza kai ta fara magana da karfi cikin kuka.
“Ummi tana kuka, Ummi tana da ciwo Ummi zata mutu, Ummi ba zata fada ba, Ummi tana son mijin Nimra, Ummi ta haifi Mijin Nimra”
Ta ta saka dayan hannunta ta share hawayen fahimci abun da take nufi bata iya fadar da kyau ba hakan ya saka ta kalli Ummi dake kallonta ta ce
“Ummi talk, tell them ki fada musu”
Kusan kowa kallonta yake daga Maleek dake saukowa rike da syringe a hannunsa har Mahmood da ya turo kofar falon ya shigo da zimmar sanar mata mai lessons dinta ya zo, balle kuma Ummi data tsorota da abun da Waira take fada, Jabir kuma be fahimci zancen da kyau ba as well as Maleek sai dai kalmar Ummi zata mutu ta daga musu hankali, Dr Zainab ma bata fahimcin yaren nata ba.
“Me take fada ne? Ni ban fahimta ba”
Jabir ya tambaya yana kallon Ummi.
“Ummi tana da ciwo mai mutuwa Ummi zata mutu Waira tana son Ummi”
Ta sake fada tare da fashewa da wani irin kuka mai karfi, a wannan karon Mahmood ya fahimcin inda ta dosa, Maleek kuma ya shiga hudu sai idonsa suna akan mahaifiyarsa.
“Waira ki tafi dakinki yanzu nan?”
Ummi ta fada, sai Mahmood yayi karaf ya ce.
“Mai lessons dinta ya zo yanzu nan”
“Okay wuce ki dauko jakarki ki tafi gurin lessons dinki”
Ta sauka daga kan couch din ta nufi upstarts haka ta raba gefen Maleek da ya gagara saukowa ta wuce dakinta ta dauko jakarta ta sauko ta fice daga falon.
“Me yarinyar na yi take fada ne Zahra?”
Dr Zainab ta tambaya.
“Shirmenta ne mana, da ma kin tafi gurin Abiey kun tattauna zai fi”
Maleek ya sauko ya nufi kofa ya fice daga zuwa gurin motarsa ya bude ya dauko wata ledar sannan ya dawo ciki ya haura zuwa dakin Nimra zuciyarsa da tunani kala kala. Dr Zainab ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Abiey, Jabir da Mahmood kuma suka zauna a falon Mahmood na labarta masa abun da ya faru a game da Nimra da kuma rashin mutun Ameer da ya sani. Ummi kuma ta koma kitchen din ta cigaba da abun da take tana tunanin inda Waira ta samu wannan labarin, hausawa suka ce sawun giwa ya batar da na rakumi, gaba daya sai tunaninta ya koma gurin Waira.
WAIRA POV.
A inda suka saba zama su yi lessons ta zauna akan kujerar da aka siya mata da karamin tebur din da take dora littafan karatunta, dattijon da zai yi shekara 50 yana ta zuba mata karatu amman hankalinta baya guri, tunaninta ya tafi akan dalilin Ummi na boyewa kowa ciwonta da kuma burinta akan Ameer, a yanzu kuma ta rasa gane dalilinta na kin son auren Nimra da wanda take so, domin ta ga komai a madafar iliminta sai dai illar ce ta kasa gani har yanzu.
“Waira?”
Ta kalleshi da idanuwanta masu kamar na mage.
“Lafiya kike yau?”
Ta girgiza kai domin ya saba fahimtarta tun kamin ta fada masa komai, ita kuma bata boye masa damuwarta a duk zuwan da yake gidan, wannan ya saka take jindadin zuwansa fiye da zuwa makaranta da ake takura mata. Ya bar jikin allon ya dawo kusa da ita ta tsaya.
“Fada min meya faru yau kuma?”
“Ummi tana son Mijin Nimra, kuma Ummi tana da ciwo, kuma ciwon zai kasheta ta mutu kamar Waira, amman ba ta fada ba, Ya Maleek ya daki Nimra kuma Nimra tana son... ”
Ta kasa karawa domin bata rike sunansa ba saboda haka bata san yadda ta kwatanta shi ko ta kira shi ba, Dattijon yayi murmushi ya dauko kujerar ya dawo kusa da ita ta zauna.
“Ki daina damuwa da matsalar wasu, ke ma kina cikin taki matsalar ai, ki daina kuka haka nan kukanki yana saka ni jin babu dadi”
“Toh”
Ta amsa tana kallonsa idonta na sake cika da wasu hawayen. Ya saka hannunsa aljihu ya dauko apple ya mika mata sai ta karba ta rike, a can idan suna darasi take cin apple kullum idan ya bata yau kuma da take cikin kuka da bacin rai sai ta kasa ci ta rike Apple din kawai a hannu, mikewa yayi tsaye ya nufi jakarsa ya bude ya dauko farin zomo ya nufota da shi ya dora mata saman jiki sai ta saki apple din da sauri ta rike zomon.
“Neman wannan zomon ya saka ban zo jiya gurin darasinki ba, ina fatar kina son shi”
“Sosai sosai”
Ta rumgume shi a jikinta tana jin kamar beranta ne na baya data rasa.
“Thank You”
Murmushi da farincikin da ya gani a fuskarta wanda ya kawarda bakinciki da bacin ran da take ciki ne yafi komai faranta masa rai kuma daman abun da yake son gani kenan. Ta mike tsaye ta aje zomon zata rumgume shi sai yaja baya da sauri.
“Aa aa aa, dauki jakarki ki shiga ciki darasi ya kare sai gobe idan na dawo”
“Kalli wacce ta rasa iyaye da yan'uwa da abokai da gari, ta rasa abinci da masu jin kalar yarenta ta bata mutu ba ta rayu tare da mu, sai ke ce zaki mutu dan kin rasa saurayi? Karki bari shaidan ya sharin zuciya su rinjaye ki Nimra”
Nimra ta bude ido ta kalli Waira take leken fuskarta, murmushi karfin hali Nimra ta yi mata sai Waira ta saka hannu ta fara share mata hawayenta, ta mika hannunta ta kama hannun Nimra ta rike ba dan komai ba sai dan ta san abun da yake faruwa, ta kwanatar da kanta a jikin Ummi kamar yadda na Nimra yake kwance. Ummi ta girgiza kai tunanin Ameer da kalamansa sun hanata sukuni, furucinsa na cewar saboda be san dadin uwa ba shi ke nuna be san muhimmancinta ba ya matukar tsaya mata a rai. Me aka fada masa? Uwarsa ta mutu? Shigowar Maleek ya saka ta share hawayenta ta kalleshi sa'insar da sukayi a dazun da Ameer take ta gani a idonta.
“Treatment zaka mata ka bata maganin da ya kamata”
“Ban taba mata treatment ba”
“Ka fara daga yau, kuma ban ce ka fada mata ko da kalma matar dadi ba balle har hannunka ya sake kaiwa a jikinta, Namra rikata ku tafi dakinta ki hada mata ruwa ta gasa jikinta zan hada mata wani abun ci a yanzu”
Ummi ta karasa tana kallon Namra wacce ta amsa mata da kai ta rika yar'uwarta suka mike tsaye. Waira ta bude ido da sauri tana kallon Nimra.
“Ta sanshi i know him... Waira ta san shi ta gane shi ta san shi”
Haka take ta fada da sauri tana nuna Nimra, daga Ummi har Maleek dake tsaye ba su fahimci abun da take nufi ba, Ummi kuma bata da lokacin tsayawa ta fahimceta a yanzu balle har ta gyara mata abun da take furtawa. Da ido Maleek ya harare a tunaninsa zata fara ba bada labarin abun da ya faru a school dinsu ne a yau, sai ta yi tsit kamar bata gurin.
“Bari na je na siyo magani”
Maleek ya fada sannan ya juya ya koma ta kofar falon da ya shigo. Waira ta bi Nimra da kallo har sai da suka haye sama gaba daya sannan ta dauke idonta ta dawo da su gurin Ummi.
“Ummi...”
Ummi ta kalleta wasu hawayen suna tarar mata a ido.
“Ummi miyasa Ummi ba zata bari Nimra ta aure shi ba”
“Saboda wani abubuwa da yawa tashi ki je ki cire uniform dinki”
Ta tashi ta nufi upstarts, sai kuma ta juyo.
“Ummi... Meyasa Ummi ba zata fadawa Abiey tana son mijin Nimra ba?”
Ummi bata bi ta kan maganar ba, domin tana cikin damuwa a yanzu.
“Na ce ki tafi ki canja uniform dinki”
Waira ta juya ta karasa hayewa sama, Ummi kuma ta cire hijabinta ta kwanta akan kujera tana ta addu'ar samun saukin zuciya. Waira na shiga dakinta wanka ne abun da ta fara yi sannan ta fito ta saka wando da riga ta sauko kasa bata samu kowa a falon ba sai motsin da take ji a kitchen, hakan ya saka ta nufi kitchen kai tsaye ta leka sai ga ta samu Ummi a tsaye.
“Ummi ta canja”
Ta fada tana shafa tufafin jikinta, Ummi ta juyo ta kalleta tana jin kamar zuciyarta zata tsage.
“Ummi. Meyasa Ummi ba fada fadawa Abiey bata da lafiya?”
“Lafiyata kalau tafi falo ki zauna zan hada miki tea yanzu ke da Nimra”
A maimakon ta juya ta fita kamar yadda Ummi ta bukata sai ta rugo da gudu ta rumgume Ummi ta fashe da kuka.
“Waira tana son Ummi”
Ummi ta shafa bayanta..
“Ya isa, bana son jin kuka kowa a yanzu je ki zauna zan kawo miki tea kamin mai lessons dinki ya zo kin ji? Ni ma ina sonki”
Ba dan ta so ba ta bar jikin Ummi ta fito falo ta zauna ta takure guri daya kamar bakuwa, tana kallon Maleek ya shigo ya haura sama zuwa dakin Nimra, aka sake bude kofar Dr ta shigo tare da Jabir hankalinta a tashe.
“Ina Zahra take?”
Ummi na jin muryar Dr Zainab ta fito daga kitchen din ta nufota ta rumgume tana jin wani sanyi sanyi a ranta. Jabir kuma ya nufi Waira dake ta sharar kwalla.
“Waya taba ki?”
“Ummi zata mutu...”
Yayi saurin rufe mata baki, a zatonsa kuka da ta ga Ummi tana yi ne ya saka ta tsorata har take furta haka.
“Subhanallah, ki dina fadar hakan ba abubuwa ne akwai suka faru kuma komai zai wuce kinji?”
Ta girgiza kai ta fara magana da karfi cikin kuka.
“Ummi tana kuka, Ummi tana da ciwo Ummi zata mutu, Ummi ba zata fada ba, Ummi tana son mijin Nimra, Ummi ta haifi Mijin Nimra”
Ta ta saka dayan hannunta ta share hawayen fahimci abun da take nufi bata iya fadar da kyau ba hakan ya saka ta kalli Ummi dake kallonta ta ce
“Ummi talk, tell them ki fada musu”
Kusan kowa kallonta yake daga Maleek dake saukowa rike da syringe a hannunsa har Mahmood da ya turo kofar falon ya shigo da zimmar sanar mata mai lessons dinta ya zo, balle kuma Ummi data tsorota da abun da Waira take fada, Jabir kuma be fahimci zancen da kyau ba as well as Maleek sai dai kalmar Ummi zata mutu ta daga musu hankali, Dr Zainab ma bata fahimcin yaren nata ba.
“Me take fada ne? Ni ban fahimta ba”
Jabir ya tambaya yana kallon Ummi.
“Ummi tana da ciwo mai mutuwa Ummi zata mutu Waira tana son Ummi”
Ta sake fada tare da fashewa da wani irin kuka mai karfi, a wannan karon Mahmood ya fahimcin inda ta dosa, Maleek kuma ya shiga hudu sai idonsa suna akan mahaifiyarsa.
“Waira ki tafi dakinki yanzu nan?”
Ummi ta fada, sai Mahmood yayi karaf ya ce.
“Mai lessons dinta ya zo yanzu nan”
“Okay wuce ki dauko jakarki ki tafi gurin lessons dinki”
Ta sauka daga kan couch din ta nufi upstarts haka ta raba gefen Maleek da ya gagara saukowa ta wuce dakinta ta dauko jakarta ta sauko ta fice daga falon.
“Me yarinyar na yi take fada ne Zahra?”
Dr Zainab ta tambaya.
“Shirmenta ne mana, da ma kin tafi gurin Abiey kun tattauna zai fi”
Maleek ya sauko ya nufi kofa ya fice daga zuwa gurin motarsa ya bude ya dauko wata ledar sannan ya dawo ciki ya haura zuwa dakin Nimra zuciyarsa da tunani kala kala. Dr Zainab ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Abiey, Jabir da Mahmood kuma suka zauna a falon Mahmood na labarta masa abun da ya faru a game da Nimra da kuma rashin mutun Ameer da ya sani. Ummi kuma ta koma kitchen din ta cigaba da abun da take tana tunanin inda Waira ta samu wannan labarin, hausawa suka ce sawun giwa ya batar da na rakumi, gaba daya sai tunaninta ya koma gurin Waira.
WAIRA POV.
A inda suka saba zama su yi lessons ta zauna akan kujerar da aka siya mata da karamin tebur din da take dora littafan karatunta, dattijon da zai yi shekara 50 yana ta zuba mata karatu amman hankalinta baya guri, tunaninta ya tafi akan dalilin Ummi na boyewa kowa ciwonta da kuma burinta akan Ameer, a yanzu kuma ta rasa gane dalilinta na kin son auren Nimra da wanda take so, domin ta ga komai a madafar iliminta sai dai illar ce ta kasa gani har yanzu.
“Waira?”
Ta kalleshi da idanuwanta masu kamar na mage.
“Lafiya kike yau?”
Ta girgiza kai domin ya saba fahimtarta tun kamin ta fada masa komai, ita kuma bata boye masa damuwarta a duk zuwan da yake gidan, wannan ya saka take jindadin zuwansa fiye da zuwa makaranta da ake takura mata. Ya bar jikin allon ya dawo kusa da ita ta tsaya.
“Fada min meya faru yau kuma?”
“Ummi tana son Mijin Nimra, kuma Ummi tana da ciwo, kuma ciwon zai kasheta ta mutu kamar Waira, amman ba ta fada ba, Ya Maleek ya daki Nimra kuma Nimra tana son... ”
Ta kasa karawa domin bata rike sunansa ba saboda haka bata san yadda ta kwatanta shi ko ta kira shi ba, Dattijon yayi murmushi ya dauko kujerar ya dawo kusa da ita ta zauna.
“Ki daina damuwa da matsalar wasu, ke ma kina cikin taki matsalar ai, ki daina kuka haka nan kukanki yana saka ni jin babu dadi”
“Toh”
Ta amsa tana kallonsa idonta na sake cika da wasu hawayen. Ya saka hannunsa aljihu ya dauko apple ya mika mata sai ta karba ta rike, a can idan suna darasi take cin apple kullum idan ya bata yau kuma da take cikin kuka da bacin rai sai ta kasa ci ta rike Apple din kawai a hannu, mikewa yayi tsaye ya nufi jakarsa ya bude ya dauko farin zomo ya nufota da shi ya dora mata saman jiki sai ta saki apple din da sauri ta rike zomon.
“Neman wannan zomon ya saka ban zo jiya gurin darasinki ba, ina fatar kina son shi”
“Sosai sosai”
Ta rumgume shi a jikinta tana jin kamar beranta ne na baya data rasa.
“Thank You”
Murmushi da farincikin da ya gani a fuskarta wanda ya kawarda bakinciki da bacin ran da take ciki ne yafi komai faranta masa rai kuma daman abun da yake son gani kenan. Ta mike tsaye ta aje zomon zata rumgume shi sai yaja baya da sauri.
“Aa aa aa, dauki jakarki ki shiga ciki darasi ya kare sai gobe idan na dawo”