Sashe 48
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Kar wani yayi min wata magana akan Maleek, and i meant it, enough is enough na gaji kowa ya tafi gurin sha'aninsa, Mahmood je ka shirya mu kai yarinyar nan Asibiti, Namra wuce ki tafi gurin aikinki, and you Nimra ki sama mata tufafin da zata saka zan shiga na yi wanka”
Haka ta rabawa kowa aiki sannan ta shiga bandakin, kamar yadda ta umarta haka kowa yayi, ba ma kamar Mahmood da ya san condition dinta shi ya tsoron tashin hankalinta fiye da komai. A falo ya fito ya zauna yana jiran saukowarsu, Namra tuni ta wuce gurin aikinta Nimra kuma ta taimakawa Waira ta saka wando da riga domin su ne kadai suka yi mata a cikin tufafinta shi ma wandon dan yana gajere ne sai ya saukowa Waira saboda tsayinta be kai na Nimra ba. Ummi ta fito da shirinta suka wuce tare Mahmood da be samu tsayawa ya karya ba a ranar, daman Abiey tuni ya fice daga gidan bayan sun yi sallama da Maleek da ya dawo bangaren Ummi a dazun da abubuwa marar dadi suka faru. Sai ya rage Nimra ce kadai a gidan, hakan ya bata damar shiga bangaren Abiey ta shiga har dakinsa tana bincike inda yaks aje abubuwansa ta har ta samu sa'ar gano inda keys din motar ta yake ta dauko ta fito waje ta bude motar tana duba ko'ina. Har da addu'a take Allah ya sa ta sarewar saboda ta farantawa Ameer rai, can kasan kujera ta hango abu mai kamar akwaiti da sauri ta dauka tana budewa sai ta yi arba da abun da ba dan ta ganta a hannunsa yana busa ba da ba zata iya kiransa da sarewa kai tsaye ba, saboda ya sabon samfur ne. Da sauri ta fito motar ta rufe ta maida key din inda ta dauko shi ta dawo dakinta ta dauki hoton sarewar ta turawa Ameer sannan ta boye box din a karkashin gadonta.
AMEER POV.
Ya aje wayar yana murmushi ya cigaba da saka maballan rigarsa.
“Good Girl yanzu sai zancen haduwa zan yi wannan wasan da kyau”
After ya gama sakawa ya sake daukar wayar ya mayar mata da amsa.
‘Idan ba zaki iya zuwa can ba, then mu hadu a Galadimawa inda muka taba zuwa it's a safe place babu wanda zai gan ki kuma yanzu nan zan tafi sai kin iso’
Tana gama rubuta mata amsar ya kashe data shi ya saka wayar aljihu ya dauki abubuwa da ya san zai bukata ya fice daga dakin. Sai da ya zabi motar da ta yi masa sannan ya saka kanwarsa ta dauko nasa key motar a bangaren mahaifinsa ya karba ya hau ya kama hanyar Galadimawa. Ya isa in time saboda yayi abun da ya saba wato gudu da mota, ya ki ya kunna data shi balle ya ga abun da Nimra zata fada masa so yake ya cilasta ta baro gidansu zuwa inda yake bukatar ganinta so that ya san idan ya fara tasiri a zuciyarta ko akasin haka, yadda ta nuna masa ba zata iya zuwa gurin da suka saba haduwa da farko ba ya nuna tana tsoron yan'gidansu sun ganta kenan kamar yadda ta fada masa cewar idan mahaifinta ko wani ya gani bata san iya hukunci da za'ayi mata. Yana zaune cikin motarsa ya hango yarinyar da suka yi fada a gurin aikin mahaifinsa an sauke ta a wata motar da bata gurin aikin ba, 206 Saurayi a ciki yana sanye da kananan kaya kamar yadda Ameer ma ya saka kananan kayan, ita kuma tana sanye da rigar gurin aikin sai skirt ta dora after dress sai mayafin rigar da ta yafa tana rataye da jakarta daya hannunta na rike da bakar farar ledar dake dauke da rubutun kamfanin. Bude motar yayi ya fito ya nufi inda take tana tafiyarta a hankali.
“Miye a cikin ledar nan?”
Ta tsaya sai ta juyo ta kalleshi kamar ba zata ce komai ganin shi ne, sai kuma ta daure ta ce.
“Abinci ne?”
“Hmmm-uhmm wato kin yi sa'a ba a koreki ba bayan fadan da kika yi da ni, and now sata kike mana a gurin ko?”
Kalmar sata ta bata mata rai, sai dai mai nema baya fushi kamar yadda Kakarta ta fada mata dole ta hakurewa wani abun.
“Aa ni ban taba sata ba, mai gurin ya amince mana mu rika diba idan ya rage ko kuma idan mun san babu shi a gida”
“Oh Really i will ake him then, but before that bari na fada miki wani abu karki sake saka rigar kamfaninmu kina yawo da ita samari na dauki kala kala kuna iskancinku idan an gani sai ace a karkashin mahaifina kike aiki, and consider yourself a matsayin korrriya a gurin nan”
Ta daka masa tsawa domin kalmar iskanci da ya jefeta da shi ya bata mata rai.
“Sai me? Idan ka koreni rai ka acire min? Kuma ni ba yar iska ba ce ban san miye iskanci ban hada hanya da shi ba, amman kai ka sanshi saboda aikinka ne abun da kake yi ne, kuma ka bakar shegiyar shinkafar ku nan ka dauka ka tafi da ita”
Ta jefa masa shimkafar, har ta juya ta fara tafiya sai kuma ta dawo ta iso har inda yake ta kama hannunsa yaja kamar wani yaro haka ya rika binta har cikin unguwar ta shiga da shi har cikin gidan ta tsaya da shi kofar dakin ta bude kofar dakin.
“Ga gidan mu nan ka ga dakin da nake rayuwa nan, idan ka iya ka kore ni a nan din ma, sannan ka raba ni da duniyar gaba daya, sai na san ka kai tsohon shege, idan baka gode ni'imar Allah ba zaka godewa zabarsa, ba dai ka zabi wulakanta bayinsa ba saboda ya daukaka ya baka abun da bayinsa suke nema a karkashinka? Ka ji tsoron karshenka”
Wadanda suke cikin gidan suka fito suna kallonta da shi, Mamanta ma ta fito da sauri tare da kakarta dake lullube da zane zata fita bara.
“Miya faru Humaira?”
Mamarta ta tambaya sai Humaira ta fashe da kuka ta shige falon ta bar shi a gurin tsaye. Kakarta ta taso ka iso inda yake tana kallon fuskarsa da wani irin kallo kamar zata cinye shi.
“Jika na, ka yi hakuri idan wani abun Humaira ta yi maka, kai namiji ne, karfi da zuciya da fushi ba daya ba, a inda ta nuna maka a nan muke rayu, bata da kowa sai Allah marainiya ce ubanta ya rasu kuma da aikinku da dogara da shi take biyan makaranta tana mana hidima har ta yi ma kanta wani lokacin, mahaifiyarta bata sana'ar komai ni kuma kakarta bara kawai na iya, dan Allah karka koreta karka mata wani abun ka yi jinkan na kasa da kai, duk wanda ya nema a gurinka lallai dan ya san kana da shi ne, ka fi karfinmu nesa ba kusa ba, amman karka bari sherin shaida da zuciya su rinjaye ka, ka yi hakuri dan Allah...”
Ta duka har kasa tana bashi hakuri idonta dake cike da hawaye suna kallon fuskarsa, ba shi kadai take gani ba zubun fuskar da tsarin hallitar da tsayin take ganin kamar na ďanta ďa ďaya tilo da ya rasu, Kamar har ta so ta yi yayi sai dai wannan ya fi ďanta manyan ido da kyau da fadin kirji. Baya baya yayi ba tare da yace komai ba ya juya ya fice daga gidan cikin rashin kuzari, yana jin wani abu marar dadi a ransa.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
25
Cikin motarsa ya dawo ya zauna yana ta kallon mutanen dake wucewa, ya duba duba hannunsa daidai saitin inda ta rika wutsiyar hannun ta ja zuwa cikin gidansu. Isowar Nimra ya saka shi sauke gilashin motarsa yayi mata horn, sai ta fito motar Ummi ta nufo inda yake rike da Box din ta saka mask a fuskarta tare da katon bakin gilashi, bude motar ta yi ta shiga ta zauna ta cire mask din da glass.
“Na karya dokar da Abiey ya saka min, kuma na karya alkawarin da na yi ma Ummi”
Ya kalleta a lokacin da hankalinsa da kuma tunaninsa suka dawo kanta.
“Wace doka?”
“Na yi ma Ummi alkawarin ba zan sake haduwa da kai ba, ita ta bukaci haka kuma na yi mata, Abiey kuma yace ko sunanka kar ya sake jin a gurin mu, yanzu kuma na fito ba tare da sanin kowa ba na zo nan”
Ya taba baki.
“Just”
Ta kalleshi.
“Just ne kawai?”
“Yeah don't tell me this is the first time da kika yi breaking rules din gidanku, yanzu fa an waye ba komai zaka aikata ka bar iyayenka su sani ba like this”
Ya kwanta jikin kujerar da take ya sumbanci gefen bakinta.
“You can't tell them same one kissed you”
Ya rika hannunta ya murza a hankali.
“And you can't tell them someone hold your hand, akwai abubuwa da yawa ba zamu fadawa iyayeba amman muna aikatawa, an waye yanzu Nimra muna wani zamani ne da muka fi iyayenmu wayo da iya sirranta abu”
Rawa jikinta yake, ba rawa ta tsoro ko fargaba ba, rawa irin da macen da namiji be taba rika hannunta ba ya fara a yanzu, wani abun take jin mai kamar faduwar gaba tana ji tana gani numfashinta na son sarkewa, so take ya janye hannunta daga rikon da yayi mata domin har yanzu murza mata yatsun yake amman ta kasa. Kiss din da yayi mata ma ta aje shi a wani ma'auni na dabam. Ta kasa kallonsa sai yawo take da idonta a titi.
“Ga... Ga.. Sarew... War...”
Ta samu kuzarin mika mishi bayan ta yaki zuciyarta. Be saki hanninta ba sai ya saka dayan hannunsa ya karba yana hadawa da hannunta ya rike, sai kuma ya daga hannunta ya sumbanta.
“Na gode sosai sarewar tana da muhimmanci a gareni”
Wannan karon ka ta samu kuzarin fisge duka hannayenta.
“Wannan be dace ba Ameer haramun be”
Dariya ya saka mata yana mata kallon mamaki.
Haka ta rabawa kowa aiki sannan ta shiga bandakin, kamar yadda ta umarta haka kowa yayi, ba ma kamar Mahmood da ya san condition dinta shi ya tsoron tashin hankalinta fiye da komai. A falo ya fito ya zauna yana jiran saukowarsu, Namra tuni ta wuce gurin aikinta Nimra kuma ta taimakawa Waira ta saka wando da riga domin su ne kadai suka yi mata a cikin tufafinta shi ma wandon dan yana gajere ne sai ya saukowa Waira saboda tsayinta be kai na Nimra ba. Ummi ta fito da shirinta suka wuce tare Mahmood da be samu tsayawa ya karya ba a ranar, daman Abiey tuni ya fice daga gidan bayan sun yi sallama da Maleek da ya dawo bangaren Ummi a dazun da abubuwa marar dadi suka faru. Sai ya rage Nimra ce kadai a gidan, hakan ya bata damar shiga bangaren Abiey ta shiga har dakinsa tana bincike inda yaks aje abubuwansa ta har ta samu sa'ar gano inda keys din motar ta yake ta dauko ta fito waje ta bude motar tana duba ko'ina. Har da addu'a take Allah ya sa ta sarewar saboda ta farantawa Ameer rai, can kasan kujera ta hango abu mai kamar akwaiti da sauri ta dauka tana budewa sai ta yi arba da abun da ba dan ta ganta a hannunsa yana busa ba da ba zata iya kiransa da sarewa kai tsaye ba, saboda ya sabon samfur ne. Da sauri ta fito motar ta rufe ta maida key din inda ta dauko shi ta dawo dakinta ta dauki hoton sarewar ta turawa Ameer sannan ta boye box din a karkashin gadonta.
AMEER POV.
Ya aje wayar yana murmushi ya cigaba da saka maballan rigarsa.
“Good Girl yanzu sai zancen haduwa zan yi wannan wasan da kyau”
After ya gama sakawa ya sake daukar wayar ya mayar mata da amsa.
‘Idan ba zaki iya zuwa can ba, then mu hadu a Galadimawa inda muka taba zuwa it's a safe place babu wanda zai gan ki kuma yanzu nan zan tafi sai kin iso’
Tana gama rubuta mata amsar ya kashe data shi ya saka wayar aljihu ya dauki abubuwa da ya san zai bukata ya fice daga dakin. Sai da ya zabi motar da ta yi masa sannan ya saka kanwarsa ta dauko nasa key motar a bangaren mahaifinsa ya karba ya hau ya kama hanyar Galadimawa. Ya isa in time saboda yayi abun da ya saba wato gudu da mota, ya ki ya kunna data shi balle ya ga abun da Nimra zata fada masa so yake ya cilasta ta baro gidansu zuwa inda yake bukatar ganinta so that ya san idan ya fara tasiri a zuciyarta ko akasin haka, yadda ta nuna masa ba zata iya zuwa gurin da suka saba haduwa da farko ba ya nuna tana tsoron yan'gidansu sun ganta kenan kamar yadda ta fada masa cewar idan mahaifinta ko wani ya gani bata san iya hukunci da za'ayi mata. Yana zaune cikin motarsa ya hango yarinyar da suka yi fada a gurin aikin mahaifinsa an sauke ta a wata motar da bata gurin aikin ba, 206 Saurayi a ciki yana sanye da kananan kaya kamar yadda Ameer ma ya saka kananan kayan, ita kuma tana sanye da rigar gurin aikin sai skirt ta dora after dress sai mayafin rigar da ta yafa tana rataye da jakarta daya hannunta na rike da bakar farar ledar dake dauke da rubutun kamfanin. Bude motar yayi ya fito ya nufi inda take tana tafiyarta a hankali.
“Miye a cikin ledar nan?”
Ta tsaya sai ta juyo ta kalleshi kamar ba zata ce komai ganin shi ne, sai kuma ta daure ta ce.
“Abinci ne?”
“Hmmm-uhmm wato kin yi sa'a ba a koreki ba bayan fadan da kika yi da ni, and now sata kike mana a gurin ko?”
Kalmar sata ta bata mata rai, sai dai mai nema baya fushi kamar yadda Kakarta ta fada mata dole ta hakurewa wani abun.
“Aa ni ban taba sata ba, mai gurin ya amince mana mu rika diba idan ya rage ko kuma idan mun san babu shi a gida”
“Oh Really i will ake him then, but before that bari na fada miki wani abu karki sake saka rigar kamfaninmu kina yawo da ita samari na dauki kala kala kuna iskancinku idan an gani sai ace a karkashin mahaifina kike aiki, and consider yourself a matsayin korrriya a gurin nan”
Ta daka masa tsawa domin kalmar iskanci da ya jefeta da shi ya bata mata rai.
“Sai me? Idan ka koreni rai ka acire min? Kuma ni ba yar iska ba ce ban san miye iskanci ban hada hanya da shi ba, amman kai ka sanshi saboda aikinka ne abun da kake yi ne, kuma ka bakar shegiyar shinkafar ku nan ka dauka ka tafi da ita”
Ta jefa masa shimkafar, har ta juya ta fara tafiya sai kuma ta dawo ta iso har inda yake ta kama hannunsa yaja kamar wani yaro haka ya rika binta har cikin unguwar ta shiga da shi har cikin gidan ta tsaya da shi kofar dakin ta bude kofar dakin.
“Ga gidan mu nan ka ga dakin da nake rayuwa nan, idan ka iya ka kore ni a nan din ma, sannan ka raba ni da duniyar gaba daya, sai na san ka kai tsohon shege, idan baka gode ni'imar Allah ba zaka godewa zabarsa, ba dai ka zabi wulakanta bayinsa ba saboda ya daukaka ya baka abun da bayinsa suke nema a karkashinka? Ka ji tsoron karshenka”
Wadanda suke cikin gidan suka fito suna kallonta da shi, Mamanta ma ta fito da sauri tare da kakarta dake lullube da zane zata fita bara.
“Miya faru Humaira?”
Mamarta ta tambaya sai Humaira ta fashe da kuka ta shige falon ta bar shi a gurin tsaye. Kakarta ta taso ka iso inda yake tana kallon fuskarsa da wani irin kallo kamar zata cinye shi.
“Jika na, ka yi hakuri idan wani abun Humaira ta yi maka, kai namiji ne, karfi da zuciya da fushi ba daya ba, a inda ta nuna maka a nan muke rayu, bata da kowa sai Allah marainiya ce ubanta ya rasu kuma da aikinku da dogara da shi take biyan makaranta tana mana hidima har ta yi ma kanta wani lokacin, mahaifiyarta bata sana'ar komai ni kuma kakarta bara kawai na iya, dan Allah karka koreta karka mata wani abun ka yi jinkan na kasa da kai, duk wanda ya nema a gurinka lallai dan ya san kana da shi ne, ka fi karfinmu nesa ba kusa ba, amman karka bari sherin shaida da zuciya su rinjaye ka, ka yi hakuri dan Allah...”
Ta duka har kasa tana bashi hakuri idonta dake cike da hawaye suna kallon fuskarsa, ba shi kadai take gani ba zubun fuskar da tsarin hallitar da tsayin take ganin kamar na ďanta ďa ďaya tilo da ya rasu, Kamar har ta so ta yi yayi sai dai wannan ya fi ďanta manyan ido da kyau da fadin kirji. Baya baya yayi ba tare da yace komai ba ya juya ya fice daga gidan cikin rashin kuzari, yana jin wani abu marar dadi a ransa.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
25
Cikin motarsa ya dawo ya zauna yana ta kallon mutanen dake wucewa, ya duba duba hannunsa daidai saitin inda ta rika wutsiyar hannun ta ja zuwa cikin gidansu. Isowar Nimra ya saka shi sauke gilashin motarsa yayi mata horn, sai ta fito motar Ummi ta nufo inda yake rike da Box din ta saka mask a fuskarta tare da katon bakin gilashi, bude motar ta yi ta shiga ta zauna ta cire mask din da glass.
“Na karya dokar da Abiey ya saka min, kuma na karya alkawarin da na yi ma Ummi”
Ya kalleta a lokacin da hankalinsa da kuma tunaninsa suka dawo kanta.
“Wace doka?”
“Na yi ma Ummi alkawarin ba zan sake haduwa da kai ba, ita ta bukaci haka kuma na yi mata, Abiey kuma yace ko sunanka kar ya sake jin a gurin mu, yanzu kuma na fito ba tare da sanin kowa ba na zo nan”
Ya taba baki.
“Just”
Ta kalleshi.
“Just ne kawai?”
“Yeah don't tell me this is the first time da kika yi breaking rules din gidanku, yanzu fa an waye ba komai zaka aikata ka bar iyayenka su sani ba like this”
Ya kwanta jikin kujerar da take ya sumbanci gefen bakinta.
“You can't tell them same one kissed you”
Ya rika hannunta ya murza a hankali.
“And you can't tell them someone hold your hand, akwai abubuwa da yawa ba zamu fadawa iyayeba amman muna aikatawa, an waye yanzu Nimra muna wani zamani ne da muka fi iyayenmu wayo da iya sirranta abu”
Rawa jikinta yake, ba rawa ta tsoro ko fargaba ba, rawa irin da macen da namiji be taba rika hannunta ba ya fara a yanzu, wani abun take jin mai kamar faduwar gaba tana ji tana gani numfashinta na son sarkewa, so take ya janye hannunta daga rikon da yayi mata domin har yanzu murza mata yatsun yake amman ta kasa. Kiss din da yayi mata ma ta aje shi a wani ma'auni na dabam. Ta kasa kallonsa sai yawo take da idonta a titi.
“Ga... Ga.. Sarew... War...”
Ta samu kuzarin mika mishi bayan ta yaki zuciyarta. Be saki hanninta ba sai ya saka dayan hannunsa ya karba yana hadawa da hannunta ya rike, sai kuma ya daga hannunta ya sumbanta.
“Na gode sosai sarewar tana da muhimmanci a gareni”
Wannan karon ka ta samu kuzarin fisge duka hannayenta.
“Wannan be dace ba Ameer haramun be”
Dariya ya saka mata yana mata kallon mamaki.