Sashe 105
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maleek be ce komai ba daman kuma ba zai ce ba, ya ayyana a ransa sai ya doketa a yau ba Hanne ba ko da kuwa Ummi ce a falon. Yana isa ya fisgota jikin Hanne ya jefar da ita kan kujera ya nufi gurin da Kristen yake ya ya cire wayar da zai iya cirewa ya nufo Waira, a maimakon ta tashi ta gudu stairs ko waje sai kawai ta yi zaune a gurin sai kuka take tana jarfar da hannu. Yana auna mata daya ta daka tsalle ta kwala wani uban kara tana murza jikinta, bata san wata rana da take da wayo da aka daketa da wani abun dukaba tun tana garinsu, sai daia yi mata hukunci idan ta yi wani abu, shi ma kuma ba sosai ba, bata taba sanin zafin jikinta ba irin yau. Mahmood ne ya sauko da gudu stairs saboda ihun da take, kamar zai same ya fadi haka ya iso gurin ya fisge bulalar da Maleek yake shauda mata.
“Meye haka me ta yi?”
Ta tashi da sauri ta boya a bayan Mahmood tana kuka sosai kamar ranta zai fita. Maleek can't tell laifin da ta yi dan haka ya fice daga falon yana hakki kamar shi aka daka ba shi yayi dokan ba. Mahmood ya kalli Hanne da mamakin abun da Maleek yayi ya ce.
“Me ta yi?”
“Toh Wallahi ni ma ba zan iya fada ba, dazun dai gaban Hajiya aka yi komai, balle na ce ko ta yi laifi, wata kila ko dan ta shigo da kudi ne yayi mata wannan dukan”
“Kudi?”
Ta nuna masa inda ta zubar da kudi, Mahmood ya nufi kudin ya dauka yana dubawa.
“Waya baki dollars haka Waira?”
Kofa kawai take iya nunawa, kuka ya ci karfinta ta yadda bata iya furta komai. Kofar Mahmood ya nufa ya leka waje be ga kowa ba ya dawo cikin falon.
“Babu kowa kin san wanda ya bata kudi”
Ya mikawa hanne tambayar kamin ta amsa Ummi ta shigo falon Yesmin na bayanta rike da warmers. Da sauri ta karasa gurin Waira dake kuka ta rikata. Waira kamar makira tana ganin Ummi sai ta zube a jikinta ta kara fashewa da kuka. Sosai ran Ummi ya bace bayan Mahmood ya fada mata abun da ya faru, sai ta hau masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
“To me zai saka ya dake ta?”
“Waya sani, Mahmood kira shi mana”
Mahmood ya dan daga gira yana kallon yadda ran Ummi ya bace, rabon da ya ga bacin ranta irin haka an jima. Upstarts ya nufa ya tura kofar dakin Maleek, sai da ya karewa dakin kallon be ga kowa ba, motsin da yaji na ruwa a bathroom ya tabbatar masa da yana ciki.
“Alhaji fito ka taba Waira Ummi na nemanka kasa”
Mahmood na rufe baki sai ga Maleek ya fito daure da tawul, gudun ya batawa Ummi lokaci ya saka shi saka short tare da jallabiya ya sauko kasa, be karasa saukowa ba yaja ya tsaya jikim stairs yana kallon Ummi wadda ta bude nasa sabon shafin ihu.
“Tun da kake a gidan nan ka taba ganin na taba yarinyar nan? Ka taba ganin na saka hannu na daketa? Akan me kai saka zaneta? Tun farkon zuwanta gidan nan ka tsinka mata mari ba tare da hakki ba”
“Wacan marin mistake ne”
Ya amsa yana jin kamar ya karasa ya kara mata dukan domin har yanzu zuciyarsa bata daina tafasa da abun da Waira ta yi ba. Da mugun fusata Ummi ta ce
“Wannan kuma intentionally ko?”
“Ummi baki ganin abun da take yi? Mu fa musulmai ne, kina kallom yadda take a jikin Ameer amman baki ce mata komai ba, ta raka shi baki hanata ba, ta dawo da kudi a hannunta duk be miki ciwo ba sai dukan da na yi mata? Haba Ummi, ko dan abun da yayi Nimra ai ya kamata ce an saita yarinyar nan a hanya domin ita na lura sam bata da hankali kuma bata san ciwon kanta ba”
“Idan ya bata kudi, wata kila ya bata ne dan ra'ayin kansa, bana tunanin Waira zata roke shi kudi, kana ganin yawan kudin ma kasan ba rokonsa ta yi ba, saboda ita ya zo gidan nan yau, saboda ita ya sha abun da na zuba masa, idan ba a gode mata ba be kamata a saka mata da duka ba, saboda ita ďana zai dawo gareni”
“Hakan na nufin ke kika bashi damar yaje ya dauke ta a school kenan? Abun da kike kokarin ginawa a tsakaninsu is very wrong Ummi”
Ummi ta mike tsaye.
“Ni mahaifiyarka ce, this should be the last time da zaka ce I'm wrong, ni ban gina wani abu a tsakaninsu ba, duk wata alaka ko shakuwa da soyayya da ka gani a tsakanin Waira da Ameer su suka gina abarsu, ba ni da masaniya akan zai je ya dauketa a makaranta karka sake zargina, kuma karka sake saka hannu ka doki Waira, an yi n karshe”
Daker ya samu saukar da numfashin da ya hau masa saman zuciya. Sannan ya juya ba tare da ya sake cewa komai ba ya shige dakinsa.
After two weeks later...
Yana tafe Fiyya na bayansa rike da basket din da Mummy ta zuba masa kulolin abincin da za a kawo asibitin. Shi ya fara tura kofar ya shiga ya rike mata kofar ta shiga sannan ya rufe. Fiyya ce ta fara karasawa gurin gadon ta aje musu abincin tana yi ma Tsohuwar ya jiki tare da isar musu da gaisuwar Mummy, domin ita bayan kwana biyu take zuwa ta duba su, kanensa kuma time time idan zai so ko direba zai kawo abinci, Ameer kan kullum idan zai je aiki ko ya dawo sai ya shigo asibitin duba tsohuwar, domin jin yake kamar nauyinta a yanzu yana kansa.
“Ya jikin?”
Ya tambaya yana kallon Tsohuwar dake rike da ayaba tana ci.
“Jiki Alhamdulillah ďan nan, Allah yayi albarka kana ta fama da dawainiya”
Humaira ta mike tsaye ta bashi kujera, sai dai ta san ba zai zauna ba, domin ba gwada zama a dakin ba duk zuwan da yake.
“Kullum zai kin kin ba ni kujera, kuma kin san ba zama nake ba”
Ta yi murmushi.
“Ina jin ba dadi ne ace ina zaune kana tsaye”
“Kuma kullum sai na tararda ke a nan ke kike jinyarta bayan ga mahaifiyarki, ba kasafai nake tararda ita, Allah yass dai kina zuwa aiki”
“Duk lokacin da zaka zo kana sa'a da ina nan ne shiyasa, aiki kuma na daina zuwa ai tun a wacan lokacin”
Ya daga mata kai.
“You got lucky na canja if da yanzu na koreki”
Dariya Fiyya ta yi kamar yadda Humaira ma ta yi dariyar.
“Baka bukatar ka koreni ai, ni na kore kaina?”
“Why?”
Ta daga kafadunta.
“Kawai dai”
Be sace cewa komai ba, ya kalli agogon hannunsa.
“Kuna bukatar wani abu?”
“Aa bama bukatar komai a yanzu”
Shigowar da Dr yayi ne ya katse hanzarinsa daga yi musu sallama ya fice. Likitan dake cikin shiga ta kayan likitoci ya iso gurin ya mikawa Ameer hannu suka gaisa.
“An fada maka sakona”
Ameer ya kalli Humaira wadda ta dago tana kallon Likitan.
“Yanzu nake kokarin yi masa bayani”
Likitan yayi murmushi.
“Kin manta kenan?”
“Aa na tuna yanzu da na ganka”
Ta fuskanci Ameer dake jiran abun da zata fada masa.
“Yace gobe za a kwance daurin da aka yi mata, a duba, idan yayi haka ake so, idan kuma be yi ba sai an sake wani”
Tana fadar idonta na cika da kwalla.
“Sarkin kuka daga magana sai hawaye, haka jiya kika min fa”
Likitan ya fada yana kallonta.
“Bana son tashin hankali, ba mu da yawa a dangi kusa, bana son na sake rasa kowa”
“Ba saki rasata ba, aiki ne kawai kuma ni ba cinye ta zan yi ba, I'm not zombie”
Ta yi murmushi tana share hawayen idonta.
“Ni ban ce ba”
“Da dai yafi”
Duk abun da ake Ameer be ce uffan ba, sai kallon tsohuwar dake cin ayarba hankali kwace yake kamar ba ita ake fadar za a sakewa aiki ba.
“Ita hankalinta a kwance ma yake naki ne a tashe”
Likitan ya fada yana kallon Humairah
“Toh abun da Allah ya kawo ba sai hakuri ba, gwagwarmaya wace kala ce ba mu gani ba?”
Ameer yayi murmushi yana kallonta, karfin halinta da imani ya burge shi.
“Allah ya kara lafiya”
Ya fada sannan yayi ma Fiyya alama da su tafi da ido, Fiyya ta yi musu sallama suka fice. Likitan ya juya ya kalli Ameer har sai da ya fice sannan ya maida dubansa gurin Humairah.
“Am ya sunanki ma?”
“Humairah..”
“Haka ashe na rike sunan”
Ta yi murmushi tare da sauke kai kasa, sai ya dauki file din da ya shigo dashi bayan ya gama duba Tsohuwar ya fice. Zaunawa Humairah ta yi tana fadin.
“Yau Mama bata zo da wuri ba, gashi ina son na shiga makaranta kar na yi latti”
“Ki zuba min abinci da aka kawo sai ki tafi, ai zata zo wata kila ta tsaya wanke tsumman da tafi da su jiya ne”
“Maybe”
Ta dauki plate din ta bude coolar jalof din shimkafa ce da aka yi mata ado da doya ta sha kayan kamshi da vegetables ga kuma mai har yayi yawa. Rabin plate ta zuba mata ta dora mata a saman gadon ta matsa mata da ruwa kusa.
“Ba zaki ci abincin ba?”
“Sai na dawo zan ci”
“Toh Allah ya kiyaye hanya, yau ba su bada kudin da suka saba fadawa ba”
“Yau da gobe ai sai Allah Hajiya, wata kila sun fara gajiya ne ko kuma sun manta”
“Meye haka me ta yi?”
Ta tashi da sauri ta boya a bayan Mahmood tana kuka sosai kamar ranta zai fita. Maleek can't tell laifin da ta yi dan haka ya fice daga falon yana hakki kamar shi aka daka ba shi yayi dokan ba. Mahmood ya kalli Hanne da mamakin abun da Maleek yayi ya ce.
“Me ta yi?”
“Toh Wallahi ni ma ba zan iya fada ba, dazun dai gaban Hajiya aka yi komai, balle na ce ko ta yi laifi, wata kila ko dan ta shigo da kudi ne yayi mata wannan dukan”
“Kudi?”
Ta nuna masa inda ta zubar da kudi, Mahmood ya nufi kudin ya dauka yana dubawa.
“Waya baki dollars haka Waira?”
Kofa kawai take iya nunawa, kuka ya ci karfinta ta yadda bata iya furta komai. Kofar Mahmood ya nufa ya leka waje be ga kowa ba ya dawo cikin falon.
“Babu kowa kin san wanda ya bata kudi”
Ya mikawa hanne tambayar kamin ta amsa Ummi ta shigo falon Yesmin na bayanta rike da warmers. Da sauri ta karasa gurin Waira dake kuka ta rikata. Waira kamar makira tana ganin Ummi sai ta zube a jikinta ta kara fashewa da kuka. Sosai ran Ummi ya bace bayan Mahmood ya fada mata abun da ya faru, sai ta hau masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
“To me zai saka ya dake ta?”
“Waya sani, Mahmood kira shi mana”
Mahmood ya dan daga gira yana kallon yadda ran Ummi ya bace, rabon da ya ga bacin ranta irin haka an jima. Upstarts ya nufa ya tura kofar dakin Maleek, sai da ya karewa dakin kallon be ga kowa ba, motsin da yaji na ruwa a bathroom ya tabbatar masa da yana ciki.
“Alhaji fito ka taba Waira Ummi na nemanka kasa”
Mahmood na rufe baki sai ga Maleek ya fito daure da tawul, gudun ya batawa Ummi lokaci ya saka shi saka short tare da jallabiya ya sauko kasa, be karasa saukowa ba yaja ya tsaya jikim stairs yana kallon Ummi wadda ta bude nasa sabon shafin ihu.
“Tun da kake a gidan nan ka taba ganin na taba yarinyar nan? Ka taba ganin na saka hannu na daketa? Akan me kai saka zaneta? Tun farkon zuwanta gidan nan ka tsinka mata mari ba tare da hakki ba”
“Wacan marin mistake ne”
Ya amsa yana jin kamar ya karasa ya kara mata dukan domin har yanzu zuciyarsa bata daina tafasa da abun da Waira ta yi ba. Da mugun fusata Ummi ta ce
“Wannan kuma intentionally ko?”
“Ummi baki ganin abun da take yi? Mu fa musulmai ne, kina kallom yadda take a jikin Ameer amman baki ce mata komai ba, ta raka shi baki hanata ba, ta dawo da kudi a hannunta duk be miki ciwo ba sai dukan da na yi mata? Haba Ummi, ko dan abun da yayi Nimra ai ya kamata ce an saita yarinyar nan a hanya domin ita na lura sam bata da hankali kuma bata san ciwon kanta ba”
“Idan ya bata kudi, wata kila ya bata ne dan ra'ayin kansa, bana tunanin Waira zata roke shi kudi, kana ganin yawan kudin ma kasan ba rokonsa ta yi ba, saboda ita ya zo gidan nan yau, saboda ita ya sha abun da na zuba masa, idan ba a gode mata ba be kamata a saka mata da duka ba, saboda ita ďana zai dawo gareni”
“Hakan na nufin ke kika bashi damar yaje ya dauke ta a school kenan? Abun da kike kokarin ginawa a tsakaninsu is very wrong Ummi”
Ummi ta mike tsaye.
“Ni mahaifiyarka ce, this should be the last time da zaka ce I'm wrong, ni ban gina wani abu a tsakaninsu ba, duk wata alaka ko shakuwa da soyayya da ka gani a tsakanin Waira da Ameer su suka gina abarsu, ba ni da masaniya akan zai je ya dauketa a makaranta karka sake zargina, kuma karka sake saka hannu ka doki Waira, an yi n karshe”
Daker ya samu saukar da numfashin da ya hau masa saman zuciya. Sannan ya juya ba tare da ya sake cewa komai ba ya shige dakinsa.
After two weeks later...
Yana tafe Fiyya na bayansa rike da basket din da Mummy ta zuba masa kulolin abincin da za a kawo asibitin. Shi ya fara tura kofar ya shiga ya rike mata kofar ta shiga sannan ya rufe. Fiyya ce ta fara karasawa gurin gadon ta aje musu abincin tana yi ma Tsohuwar ya jiki tare da isar musu da gaisuwar Mummy, domin ita bayan kwana biyu take zuwa ta duba su, kanensa kuma time time idan zai so ko direba zai kawo abinci, Ameer kan kullum idan zai je aiki ko ya dawo sai ya shigo asibitin duba tsohuwar, domin jin yake kamar nauyinta a yanzu yana kansa.
“Ya jikin?”
Ya tambaya yana kallon Tsohuwar dake rike da ayaba tana ci.
“Jiki Alhamdulillah ďan nan, Allah yayi albarka kana ta fama da dawainiya”
Humaira ta mike tsaye ta bashi kujera, sai dai ta san ba zai zauna ba, domin ba gwada zama a dakin ba duk zuwan da yake.
“Kullum zai kin kin ba ni kujera, kuma kin san ba zama nake ba”
Ta yi murmushi.
“Ina jin ba dadi ne ace ina zaune kana tsaye”
“Kuma kullum sai na tararda ke a nan ke kike jinyarta bayan ga mahaifiyarki, ba kasafai nake tararda ita, Allah yass dai kina zuwa aiki”
“Duk lokacin da zaka zo kana sa'a da ina nan ne shiyasa, aiki kuma na daina zuwa ai tun a wacan lokacin”
Ya daga mata kai.
“You got lucky na canja if da yanzu na koreki”
Dariya Fiyya ta yi kamar yadda Humaira ma ta yi dariyar.
“Baka bukatar ka koreni ai, ni na kore kaina?”
“Why?”
Ta daga kafadunta.
“Kawai dai”
Be sace cewa komai ba, ya kalli agogon hannunsa.
“Kuna bukatar wani abu?”
“Aa bama bukatar komai a yanzu”
Shigowar da Dr yayi ne ya katse hanzarinsa daga yi musu sallama ya fice. Likitan dake cikin shiga ta kayan likitoci ya iso gurin ya mikawa Ameer hannu suka gaisa.
“An fada maka sakona”
Ameer ya kalli Humaira wadda ta dago tana kallon Likitan.
“Yanzu nake kokarin yi masa bayani”
Likitan yayi murmushi.
“Kin manta kenan?”
“Aa na tuna yanzu da na ganka”
Ta fuskanci Ameer dake jiran abun da zata fada masa.
“Yace gobe za a kwance daurin da aka yi mata, a duba, idan yayi haka ake so, idan kuma be yi ba sai an sake wani”
Tana fadar idonta na cika da kwalla.
“Sarkin kuka daga magana sai hawaye, haka jiya kika min fa”
Likitan ya fada yana kallonta.
“Bana son tashin hankali, ba mu da yawa a dangi kusa, bana son na sake rasa kowa”
“Ba saki rasata ba, aiki ne kawai kuma ni ba cinye ta zan yi ba, I'm not zombie”
Ta yi murmushi tana share hawayen idonta.
“Ni ban ce ba”
“Da dai yafi”
Duk abun da ake Ameer be ce uffan ba, sai kallon tsohuwar dake cin ayarba hankali kwace yake kamar ba ita ake fadar za a sakewa aiki ba.
“Ita hankalinta a kwance ma yake naki ne a tashe”
Likitan ya fada yana kallon Humairah
“Toh abun da Allah ya kawo ba sai hakuri ba, gwagwarmaya wace kala ce ba mu gani ba?”
Ameer yayi murmushi yana kallonta, karfin halinta da imani ya burge shi.
“Allah ya kara lafiya”
Ya fada sannan yayi ma Fiyya alama da su tafi da ido, Fiyya ta yi musu sallama suka fice. Likitan ya juya ya kalli Ameer har sai da ya fice sannan ya maida dubansa gurin Humairah.
“Am ya sunanki ma?”
“Humairah..”
“Haka ashe na rike sunan”
Ta yi murmushi tare da sauke kai kasa, sai ya dauki file din da ya shigo dashi bayan ya gama duba Tsohuwar ya fice. Zaunawa Humairah ta yi tana fadin.
“Yau Mama bata zo da wuri ba, gashi ina son na shiga makaranta kar na yi latti”
“Ki zuba min abinci da aka kawo sai ki tafi, ai zata zo wata kila ta tsaya wanke tsumman da tafi da su jiya ne”
“Maybe”
Ta dauki plate din ta bude coolar jalof din shimkafa ce da aka yi mata ado da doya ta sha kayan kamshi da vegetables ga kuma mai har yayi yawa. Rabin plate ta zuba mata ta dora mata a saman gadon ta matsa mata da ruwa kusa.
“Ba zaki ci abincin ba?”
“Sai na dawo zan ci”
“Toh Allah ya kiyaye hanya, yau ba su bada kudin da suka saba fadawa ba”
“Yau da gobe ai sai Allah Hajiya, wata kila sun fara gajiya ne ko kuma sun manta”