Sashe 18
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dayan ya amsa mata, sai ta yi baya baya alamar ba zata je ba, domin zuciyarta bata raya mata komai sai cewar ita ma kasheta za'ayi kamar yadda ta ga gawar saurayin da yayi mata magana jiya a fada matacce. Kai ta girgiza musu alamar ba zata je ba, su kam daman can musu da jayayya ba na su ba ne sai abun da Sarki ya fada, sai suka juya domin sanar da Sarkin yunkurin Waira na cewa ba zata je ba kamar yadda ta yi musu alama. Waira na ganin sun bace sai ta juya ta fara gudu zuwa bayan gari can gurin manyan duwatsun da Eid ya taba kaita, tana gudu tana kuka har ta isa, sai da ta isa ta boya bayan wani dutse tana tuno abun da ya faru jiya, sai ta sake fashewa da kuka, a rayuwarta babu abun da ta tsana kamar mutuwa, domin ta san duk wanda ya tafi be dawo ba, kuma ta san halin Sarki da tsananin hukunci kuma ba ya yafewa kowa musamman idan zalinci ne aka yi. Mikewa ta yi tsaye ta fara tafiya tana sauka ta gafen garin tun tana yi a hankali har ta fara sauri tana hadawa da gudun, duk da ita da kyamar ruwanta sai gata ta saka kafarta ta gafen da ruwan be da yawa ta tsallaka ta fara ratsa dajin dake gurin tana gudu, har da faduwa take ta tashi ta jefa kafarta can ta cire ta saka a nan bata damu da ciwon da ta ji a kafa ba ita dai burinta ta bar garin gaba daya....
EID POV.
Eid dake tsaye cikin fadar yana jiran Dakarun Sarki su dawo tare da Waira da Sarkin ya ce a zo da ita ko ta halin yaya bayan sun shaida masa abun da ta fada. Ya daga kafarsa da ya ji tana masa mugun zafi alamar jin ciwo ko taka wani abu, yana dubawa sai ya ga jini. A take hankalinsa yayi matukar tashi.
“Waira...”
Ya furta numfashinsa na karo da juna, juyawa yayi da sauri domin zuciyarsa na raya masa dakarun sun ji mata ciwo a kokarinsu na kawota, sai tukunyar layun mai cike da kayan tsafi dake fadar ta fado ta fashe, ba shi ba gaba daya yan fadar mikewa suka yi tsaye har Sarki suna kallon tukunyar domin fashewar tukunyar na nufin wani babban lamari. A take Sarkin ya saka a fara bincike abun da ya faru, tsohuwar dake gaban tukunyar ta mike tsaye da sauri ta fara guda da halshe da ya rabe biyu kamar macijiya, ko'ina na fuskarta wuri ne aka yi mata ado da shi ba kuma ado irin na kwalliya ba, ado ne na tsafi domin sai da aka tsafe wurin sannan ta saka su a fuskarta.
“Yau dandanon azabar rai ta tabbata ga mai butulcewa Sarki, mai gudu ya bar garin tsafi, mai yunkurin karya dokokin garin Garuk, yaryaryar...... Karkarkar.... Farfarfar Waira ta gudu kafarta ta taka wata kasar da ba ta garin nan ba, hancinta ya shaki iskar da ba ta garin Garuk ba, lelelelelelelelelelelelelelelele hasara ta tabbata ga tsatson Kusan....”
Tsohuwar na maganar Eid na jin zuciyarsa na rawa kamar zata fado tsabar tsoro da zuwan labarin ba ga tatatan, a take ya ji yawun bakinsa sun kafe kansa ya fara tsawa, kamin ya ji kamar bakinsa ta bugu wani abu, sai jini ya samu hanya. Hannu ya kai ya taba bakin ya duba sai ya ga jini, ya juya da sauri sai Sarki ya daka masa tsawa.
“Waira ta tsallake iyaka, babu wanda zai je ya dawo da ita, babu wanda zai taro ta, wannan doka ce, ita zata dawo da kafarta”
Sai da suka fadi kasa kamar za su masa sujada domin girmama umarninsa da nuna tsantsanr biyaya a gareshi, ban da Eid dake tsaye yana kallonsa domin ya san hukuncin da Sarki ya shar'anta idan har ta bar garin kasheta za'ayi.
AMEER POV.
Ko da aka yi azahar ya bar garin Abuja, gudu yake kamar wanda baya son ransa, yana overtaking any how irin shi ya shiryawa mutuwa a yanzu saboda mahaifinsa ya bata masa rai. Sai da ya isa Kano sannan ya rage gudun da yake, ya shiga wani Shagon siyar da kaya dake bakin hanya, yana dubawa ko zai samu tufafin da za su masa, wani kallo tsana yake yi ma tufafin domin ba a'adarsa ba ce saka tufafi mai karamin kudi, duk wani abu da karamin mai arziki ko talaka zai iya sakawa sai ya ji cewar ba sa'arsa ba ne. Hakan nan dai ya daure ya siya kayan da suka ci kudin da ya kai 20k riga da wando, sannan ya fito ya shiga wani Babban shago ya siye biscuits da lemu sai ruwan da ya san za su ishe shi har ya isa inda zuciyarsa zata raya masa.
“Ina zan samu Carpet a nan?”
Ya tambaya daker domin mutane haushi suke ba shi, wani yayi masa kwatacen inda zai samu carpet dai ya nufi can ya siye karamin Carpet domin ba su da na sallah, shi kuma be ji zai iya sallah da na Nimra da ya gani a motar ba, domin be dan waye yayi sallah da shi ba.
Cikin garin Kano ya shiga ya sauka a wani babban Hotel da dollars yayi amfani ya kama daki, bayan ya bada key din motar Nimra da sunan a bada masu wankin mota na Hotel din su wanke masa ita saboda kyamar ta take tun da ya kamo hanya, duk kuwa da kasancewar be ga wani abun kazanta a ciki ba, sai dai taba sitiyarin da Nimra ta yi shi kuma ya bata yana jin kyamar kansa domin be san iya abun da ta taba ba kamin ta tuka motar bayan ita be sani ba ko wani ya tuka motar ma. Yana shiga tufafin jikinsa ya fara cirewa ya shiga be yarda ya taba tawul din dake Hotel din ba, shi dama be tana amfani da kayan kowa ba sai na shi, idan zai yi tafiya be san wahalar neman komai ba sai dai a hada masa, har Hotel ko gidan da zai zauna nema masa ake, haka ya shiga dakin wanka yadda zai kai hannunsa ya taba shower ma wani abun kallo ne, domin kyamar komai yake na Hotel saboda sanin da yayi kowa zai iya zuwa ya kama dakin ciki har da kare da akuya da tinkiya ko jaki.
“Miyasa Daddy zai min haka”
Ya fada yana jin duniyar ta juye masa gaba daya saman ya dawo kasa, kasan kuma ya koma sama, yamma ta zama kudi arewa ta zama yamma, ransa be kara baci ba sai da ya shiga wankan ya tuna be siyo soap ba, wani mugun tsaki yaja ya ji kamar ya fashe komai dake cikin bathroom din, a dole ruwa kawai ya watsa ya wanke jikinsa yayi alwala ya fito ya saka tufafin da ya siya ya bar nasa a gurin ya dauki kudin da rikonsu dole kawai suka zame masa da Atm ya saka aljihu sannan ya dauki wayar da Nimra ta bashi, Hotonta ne shimfide saman screen din wayar tana murmushi ta sha kwalliyar zamani har ta sauya kamanni. Samun kansa yayi da tsayawa kallon hoton sannan ya saka wayar aljihu ya dauki ledar biscuits dinsa da lemu ya fice daga dakin.
A dole gurin hutarwasu ya tsaya bayan ya fito Masallaci yayi sallah, sai da aka gama wanke motar aka goge sannan ya shiga, ya kama hanya, be bar garin Kano ba sai da ya siya Soap da yawa ya wasu abubuwan bukata ya zuba a motarsa, shagon da ya siye kayan ba su karbi dala ba sai ATM ya ba su suka cire kudinsu, sannan ya kama babbar hanyar fita daga Kano ba dan ya san garin da zai tafi ba. Yana tukin yana cin biscuits da lemun da ya siya, not his regular biscuits da lemu sai ya ji tas din wani iri ba irin wadanda ya saba ci ba, sai dai ba laifi wannan ma yana da dadi.
Hakan wata zuciya ke raya masa ya koma garin Kano ya shige gidan Hajiya Jamila yayi zama, sai kuma ya ji ba zai iya ba, a ganinsa ita ma ai saboda mahaifinsa ya santa, after that kuma zata iya fadawa mahaifinsa cewar yana gurinta, a yanzu be bukatar wani abun da ya shafi mahaifinsa. Driving kawai yake heading to Katsina ba dan yana da kowa a garin ba, ba dan kuma ya san kowa ba, Impact ba dan yana sha'awar zuwa garin ba sai dan ba shi da gurin zuwa.
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*
_Na Khadeeja Candy_
🔟
Namra ta matsa kusa da ita ta karbi wayar ta duba hoton, sai gata suna kallon kallo ita da Nimra, sai a yanzu Namra take tuna ta sha ganinsa a media amman how come ta ganshi a fili bata gane shi ba. Nimra ta yi baya ta zauna saman kujera ba tare da tace komai ba, Namra shiru ta yi gudun kar ta furta abun da zai saka jefa yar'uwarta cikin matsala, domin idan Ummi ko Abiey suka san cewar ta bashi motarta za su yi mata fada sosai.
Ummi da wani abu mai kama da kashi ya tsoki kahon zuciyarta saboda ambatar sunan Ameer da na mahaifinsa da Mahmood yayi ya saka ta kasa zama ta kuma kasa motsawa zuciyar sai ciwo take mata.
“Ummi”
Namra ta kira sunanta ganin yadda ta tsaya kamar hoto, da sauri ta kalli Namra irin kallon kamar bata cikin hayyacinta, wani abu take ji mai kamar kuka kuma ba kukan ba, ba zata iya kiran da damuwa ba, haka kuma ba almara ba ce, wata kila mamaki take na sunan da ya zo daya, wata kila kuma wani bangare na zuciyarta gaskiya yake fada mata cewar Ameer dinta ne. Ko shiyasa Abiey yace a bar magana sun yi solving matsalar da mahaifinsa.? Daker ta iya tara yawun bakinta ta jika makoshinta sannan ta juya ta cira kafarta da take jin kamar ta shekara bata taka ta ba, ta fara tafiya.
“Ummi lafiya”
Mahmood ya tambaya domin hankalinsa yana gurinta, Nimra kam nata hankalin yana can gurin wani tunanin na dabam.
“Na'am”
EID POV.
Eid dake tsaye cikin fadar yana jiran Dakarun Sarki su dawo tare da Waira da Sarkin ya ce a zo da ita ko ta halin yaya bayan sun shaida masa abun da ta fada. Ya daga kafarsa da ya ji tana masa mugun zafi alamar jin ciwo ko taka wani abu, yana dubawa sai ya ga jini. A take hankalinsa yayi matukar tashi.
“Waira...”
Ya furta numfashinsa na karo da juna, juyawa yayi da sauri domin zuciyarsa na raya masa dakarun sun ji mata ciwo a kokarinsu na kawota, sai tukunyar layun mai cike da kayan tsafi dake fadar ta fado ta fashe, ba shi ba gaba daya yan fadar mikewa suka yi tsaye har Sarki suna kallon tukunyar domin fashewar tukunyar na nufin wani babban lamari. A take Sarkin ya saka a fara bincike abun da ya faru, tsohuwar dake gaban tukunyar ta mike tsaye da sauri ta fara guda da halshe da ya rabe biyu kamar macijiya, ko'ina na fuskarta wuri ne aka yi mata ado da shi ba kuma ado irin na kwalliya ba, ado ne na tsafi domin sai da aka tsafe wurin sannan ta saka su a fuskarta.
“Yau dandanon azabar rai ta tabbata ga mai butulcewa Sarki, mai gudu ya bar garin tsafi, mai yunkurin karya dokokin garin Garuk, yaryaryar...... Karkarkar.... Farfarfar Waira ta gudu kafarta ta taka wata kasar da ba ta garin nan ba, hancinta ya shaki iskar da ba ta garin Garuk ba, lelelelelelelelelelelelelelelele hasara ta tabbata ga tsatson Kusan....”
Tsohuwar na maganar Eid na jin zuciyarsa na rawa kamar zata fado tsabar tsoro da zuwan labarin ba ga tatatan, a take ya ji yawun bakinsa sun kafe kansa ya fara tsawa, kamin ya ji kamar bakinsa ta bugu wani abu, sai jini ya samu hanya. Hannu ya kai ya taba bakin ya duba sai ya ga jini, ya juya da sauri sai Sarki ya daka masa tsawa.
“Waira ta tsallake iyaka, babu wanda zai je ya dawo da ita, babu wanda zai taro ta, wannan doka ce, ita zata dawo da kafarta”
Sai da suka fadi kasa kamar za su masa sujada domin girmama umarninsa da nuna tsantsanr biyaya a gareshi, ban da Eid dake tsaye yana kallonsa domin ya san hukuncin da Sarki ya shar'anta idan har ta bar garin kasheta za'ayi.
AMEER POV.
Ko da aka yi azahar ya bar garin Abuja, gudu yake kamar wanda baya son ransa, yana overtaking any how irin shi ya shiryawa mutuwa a yanzu saboda mahaifinsa ya bata masa rai. Sai da ya isa Kano sannan ya rage gudun da yake, ya shiga wani Shagon siyar da kaya dake bakin hanya, yana dubawa ko zai samu tufafin da za su masa, wani kallo tsana yake yi ma tufafin domin ba a'adarsa ba ce saka tufafi mai karamin kudi, duk wani abu da karamin mai arziki ko talaka zai iya sakawa sai ya ji cewar ba sa'arsa ba ne. Hakan nan dai ya daure ya siya kayan da suka ci kudin da ya kai 20k riga da wando, sannan ya fito ya shiga wani Babban shago ya siye biscuits da lemu sai ruwan da ya san za su ishe shi har ya isa inda zuciyarsa zata raya masa.
“Ina zan samu Carpet a nan?”
Ya tambaya daker domin mutane haushi suke ba shi, wani yayi masa kwatacen inda zai samu carpet dai ya nufi can ya siye karamin Carpet domin ba su da na sallah, shi kuma be ji zai iya sallah da na Nimra da ya gani a motar ba, domin be dan waye yayi sallah da shi ba.
Cikin garin Kano ya shiga ya sauka a wani babban Hotel da dollars yayi amfani ya kama daki, bayan ya bada key din motar Nimra da sunan a bada masu wankin mota na Hotel din su wanke masa ita saboda kyamar ta take tun da ya kamo hanya, duk kuwa da kasancewar be ga wani abun kazanta a ciki ba, sai dai taba sitiyarin da Nimra ta yi shi kuma ya bata yana jin kyamar kansa domin be san iya abun da ta taba ba kamin ta tuka motar bayan ita be sani ba ko wani ya tuka motar ma. Yana shiga tufafin jikinsa ya fara cirewa ya shiga be yarda ya taba tawul din dake Hotel din ba, shi dama be tana amfani da kayan kowa ba sai na shi, idan zai yi tafiya be san wahalar neman komai ba sai dai a hada masa, har Hotel ko gidan da zai zauna nema masa ake, haka ya shiga dakin wanka yadda zai kai hannunsa ya taba shower ma wani abun kallo ne, domin kyamar komai yake na Hotel saboda sanin da yayi kowa zai iya zuwa ya kama dakin ciki har da kare da akuya da tinkiya ko jaki.
“Miyasa Daddy zai min haka”
Ya fada yana jin duniyar ta juye masa gaba daya saman ya dawo kasa, kasan kuma ya koma sama, yamma ta zama kudi arewa ta zama yamma, ransa be kara baci ba sai da ya shiga wankan ya tuna be siyo soap ba, wani mugun tsaki yaja ya ji kamar ya fashe komai dake cikin bathroom din, a dole ruwa kawai ya watsa ya wanke jikinsa yayi alwala ya fito ya saka tufafin da ya siya ya bar nasa a gurin ya dauki kudin da rikonsu dole kawai suka zame masa da Atm ya saka aljihu sannan ya dauki wayar da Nimra ta bashi, Hotonta ne shimfide saman screen din wayar tana murmushi ta sha kwalliyar zamani har ta sauya kamanni. Samun kansa yayi da tsayawa kallon hoton sannan ya saka wayar aljihu ya dauki ledar biscuits dinsa da lemu ya fice daga dakin.
A dole gurin hutarwasu ya tsaya bayan ya fito Masallaci yayi sallah, sai da aka gama wanke motar aka goge sannan ya shiga, ya kama hanya, be bar garin Kano ba sai da ya siya Soap da yawa ya wasu abubuwan bukata ya zuba a motarsa, shagon da ya siye kayan ba su karbi dala ba sai ATM ya ba su suka cire kudinsu, sannan ya kama babbar hanyar fita daga Kano ba dan ya san garin da zai tafi ba. Yana tukin yana cin biscuits da lemun da ya siya, not his regular biscuits da lemu sai ya ji tas din wani iri ba irin wadanda ya saba ci ba, sai dai ba laifi wannan ma yana da dadi.
Hakan wata zuciya ke raya masa ya koma garin Kano ya shige gidan Hajiya Jamila yayi zama, sai kuma ya ji ba zai iya ba, a ganinsa ita ma ai saboda mahaifinsa ya santa, after that kuma zata iya fadawa mahaifinsa cewar yana gurinta, a yanzu be bukatar wani abun da ya shafi mahaifinsa. Driving kawai yake heading to Katsina ba dan yana da kowa a garin ba, ba dan kuma ya san kowa ba, Impact ba dan yana sha'awar zuwa garin ba sai dan ba shi da gurin zuwa.
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*
_Na Khadeeja Candy_
🔟
Namra ta matsa kusa da ita ta karbi wayar ta duba hoton, sai gata suna kallon kallo ita da Nimra, sai a yanzu Namra take tuna ta sha ganinsa a media amman how come ta ganshi a fili bata gane shi ba. Nimra ta yi baya ta zauna saman kujera ba tare da tace komai ba, Namra shiru ta yi gudun kar ta furta abun da zai saka jefa yar'uwarta cikin matsala, domin idan Ummi ko Abiey suka san cewar ta bashi motarta za su yi mata fada sosai.
Ummi da wani abu mai kama da kashi ya tsoki kahon zuciyarta saboda ambatar sunan Ameer da na mahaifinsa da Mahmood yayi ya saka ta kasa zama ta kuma kasa motsawa zuciyar sai ciwo take mata.
“Ummi”
Namra ta kira sunanta ganin yadda ta tsaya kamar hoto, da sauri ta kalli Namra irin kallon kamar bata cikin hayyacinta, wani abu take ji mai kamar kuka kuma ba kukan ba, ba zata iya kiran da damuwa ba, haka kuma ba almara ba ce, wata kila mamaki take na sunan da ya zo daya, wata kila kuma wani bangare na zuciyarta gaskiya yake fada mata cewar Ameer dinta ne. Ko shiyasa Abiey yace a bar magana sun yi solving matsalar da mahaifinsa.? Daker ta iya tara yawun bakinta ta jika makoshinta sannan ta juya ta cira kafarta da take jin kamar ta shekara bata taka ta ba, ta fara tafiya.
“Ummi lafiya”
Mahmood ya tambaya domin hankalinsa yana gurinta, Nimra kam nata hankalin yana can gurin wani tunanin na dabam.
“Na'am”