Sashe 76
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi ta hade yawu da tana jin bacin rai akan abun da Ameer ya aikata for the first time, miyasa zai fada mata hakan a lokacin da take cikin tashin hankalin rabuwa da shi? Kuma daman can ba sonta yake tsakani da Allah ba da akwai aure a tsakaninsu haka zai saka mata ya ki aureta ya bayan yayi breaking heart dinta?
“Ummi ina kaunarki sosai”
Ta fada tana kara jimke hannun Ummi tare da dagowa ta sai Ummi ta kai jikinta kadan ta rumgumeta, suna haka aka turo kofar dakin Abiey ya shigo fuskarsa dauke da damuwa sosai.
“Tun da muka kawo yarinyar asibiti kin ki barta ta huta, a gabanki dazun likitan ya fada mana cewar hutu take bukata, na san kuma idan kina dakin nan ke ba zaki huta ba ita ma ba zata huta ba”
Ummi ta daga jikin Nimra ta mike tsaye gaba daya tana kallonta da hawaye a idonta.
“Mutuwa kadai ta isa ta shiga tsakanin uwa da ya Abiey, idan bana kusa da ita damuwata karuwa take, kuma zamana a kusa da ita ita kuma kara mata damuwa yake”
“Dan Allah ki kwantar da hankalinki, ciwo ne fa kawai zata ji sauki ta tashi kamar ba ayi ba, yanzu da wanne zan ji tashin ha kalinki ko ciwonta?”
Ummi ta sauke kai kasa ba tare da ta sake cewa Abiey komai ba ta saki hannun Nimra ta juya ta fice daga dakin. Abiey ya zauna a kujerar data tashi yana kallon Nimra dake kallonsa oxygen a hancinta da bakinta. Ya dade yana kallonta sannan ya mike tsaye ba tare da yace da ita komai ya nufi kofa sai ta cire Oxygen din dake bakinta ta ce.
“Abiey ka yafe min dan Allah ka yi hakuri”
Ya juyo da sauri ya dawo ya zauna ya kai hannu ya shafa goshinta.
“Da ban yafe miki ba, ba zan so asibitin nan kuma har na shigo cikin nan ba, kin yi kuskure a matsayinki na ya kuma yar adam, ni kuma na yafe miki a matsayina na mahaifinki, Allah ya baki lafiya kuma yayi miki albarka”
“Ameen Abiey”
Ta fada tana jin sanyi a ranta.
“Abiey da gaske Ummi ita ta haifi Ameer”
Abiey yayi jimm kamar ba zai ce komai ba, be mamakin sanin da ta yi ba wata kila Ummi ce ta fada mata haka saboda ta warware mata tsakanin tsare da abawa, na haramcin aurenta da Ameer.
“Nimra kina a yanayin da be kamata mu yi doguwar magana da ke ba, hutu kike bukata a yanzu, idan kin samu lafiya sai mu yi magana kin ji”
“Abiey dan Allah ka fada min, ina son na sani, gaskiya ne ko?”
“Gaskiya ne Zahra ita ta haifi Ameer kuma jininta ne”
“Amman Abiey miyasa bata tare da shi? Mutanen da yake nunawa a matsayin iyayensa su waye su?”
“Idan kika samu lafiya zan fada miki komai da kaina, fata dai yanzu ki samu lafiya karki zurfafa tunani zai kara haifar miki da damuwa i love you you should know that”
Ya sumbanci goshinta hawayensa na diga a saman kanta, sai ta yi murmushi ta lumshe ido tana jin son mahaifin nata a ranta. Bata bude idon ba har ya fice daga dakin, yana tafe yana tunanin Ummi a ransa, tausayinta ya cika masa zuciya fiye da kullum, shi da yake a tsakanin rayuwar yarsa da rasata yana jin kamar ba zai iya jurewa idan ya rasa ta, saboda mugun son yayansa da yake da kuma shakuwa da yayi da su, balle kuma Ummi da ta rayu a tsaye shekara da shekaru babu danta a kusa da ita, alhalin yana raye a yanzu kam ya tabbatar ciwon nan yana tare da ita, ta wannan babin kan ya jinjina mata matuka. Ya isa gurin da su Ummi da Dr Zajnab, Yesmin da Juwairiyyya, Mahmood da Maleek suke zaune har da Namra. Ummi na ganinsa ta mike tsaye sai yayi mata alama da ta zauna.
“Matukar kika ce zaki tare a dakin can to mota zan saka ki mu tafi gida yanzu nan, domin na ga alamar ba zaki barta ta samu hutu ba”
Ummi ta koma ta zauna suna kallonta.
“Ba a barin marar lafiya shi kadai ai”
“Toh ga Dr nan sai ta tafi gurinta ta zauna, ke kuma sai ki tashi mu tafi gida saboda babu kowa a cikin gidan an kwashe duk kun zo nan kun tare, kamar ni ne ba ni da lafiya”
Duk sai da suka yi murmushi da ba su shirya masa ba har Ummi dake cikin damuwa.
“Abiey idan kai ne baka da lafiya ai har masu gadin gidan sai sun tare a nan”
Maleek ya fada yana daga zaune a dayan carpet din da aka shimfida. Abiey yayi murmushi ya ce.
“Balle ma ba zan yi ba, sai dai Umminku”
“Ummin ma muna sonta Abiey”
Namra ta fada, sai duk suka saka dariya kamar babu damuwa a ransu. Sun dan taba hira sannan ya wuce tare da Maleek Juwairiyyya, aka bar Namra daman tace ba zata tafi ba, sai Yesmin dake lake da Mamarta wato tsohuwar likita Dr Zainab inda suka tare a dakin Nimra, harabar ta zama daga Mahmood sai Ummi da Abbie ya hana ta shiga ciki da Namra wacce ganin halin da yar'uwar haihuwarta take ciki yake daga mata hankali.
Abiey na gaba zaune Maleek na tuka motar Juwairiyyya na baya tana taba wayarta, titi kawai Abiey yake kallo amman hankalinsa yana wani gurin har suka isa gida. Masu gadin suka bude musu gate, kamin Maleek yaja motar su shiga ciki Police din da tarbi Humaira ya iso gurin motar Maleek na ganin hakan ya saukewa Abiey gilashinsa domin ta side dinsa ya tsaya.
“Ranka ya dade, dazun na so na baku wayar da yarinyar nan ta bari da wasika amman ban samu dama ba saboda kun fita hankali a tashe”
“Wace yarinya?”
Abiey ya tambaya domin shi be san abun da ke faruwa ba ma.
“Yarinyar da ta so dazun akan cewar ita kawar Nimra ce tana son ta ganta wai wayar Nimra ma tana hannunta, toh na zo na kira wayarka a tambayi Nimra ko ta san da zuwanta ko kuma akwai wanda ya santa a gidan, gudun kar mu barta ta shiga wani abu ya faru bayan dokar da ka saka mana cewar kar mu sake barin Nimra ta fita, toh fitowar da aka yi da ita cikin rashin lafiya sai yarinyar ta saki wayar da takardar hannunta ta gudu, mun bita sai dai ba mu samu nasarar kamata ba saboda ta shiga wata motar kuma mai tukin yaja da gudu sun tafi, sai dai muna son fadada bincike idan ka ba mu dama”
Abiey ya mika hannu ya karbi wayar da takardar with curious face. Maleek ma da mamakin guduwar ya ja motar suka shiga compound din gidan, Juwairiyyya ce ta fara fita, Abiey ya warwar takardar ya fara karantawa bayan ya gama duba wayar da ya tabbatar ta yarsa ce.
‘I'm sorry Nimra, ban dauka abun zai kai ga haka ba, ina tunanin kiran wayata da kika ba zai gamsar da ke ba kamar ganin wannan sakon nawa a rubuce, na rubuto ne saboda na kara tabbatar miki kuma na jadda miki cewar ni ban tana jin kaunarki ko digo daya a zuciyata ba, na san zaki min kallon maci amana, amman yayanki ya fara ai ni kawai fansa na dauka, kuma ki gode Allah ban taba mu'amala dake ba, wata kila da sai abun yafi taba ki, i wish you all the best, i kila da wanda zai nuna miki so kuma wanda zaki fada sonsa a nan gaba
Ameer’
Sunansa ne daga karshe tare da sa hannunsa, Abiey na gama karantawa ya mikewa Maleek yana jin wata sabuwar tsanar Ameer a ransa. Maleek ya karba ya karanta.
“Me kake tunani idan ta karanta wannan sakon? Yaron nan so yake kawai ya kasheta”
“Ta sani ai, Ummi ta fada mana haka dazun kamin ka zo, kuma tace shi yayi silar da aka kaita asibiti, daman na fada mata ai bata yarda ba ne, amman ni na san waye Ameer, ba zai taba sonta ba ko dan tana kanwata, sai dai yayi amfani da ita ya cin ma wata manufa”
Abiey yaja dogon tsaki ya bude motar ya fita ya nufi sashensa. Maleek ya juya gafensa da zimmar bude gambun motar ya hango Waira dake tsaye nesa da motar rike da dan zomonta tana kallon motarsu, jiran take waye zai fito mazaunin direban ko Ummi ce, domin ita kadai take son gani. Samun kansa yayi da tsayawa kallonsa kasancewar bakin gilashi ne na waje baya iya ganin na ciki, sai dai na ciki ya ga na waje, idonta yayi sumtum kamar an dafa shi saboda kukan da ta ci na tafiyar Shuraim. Ganin kamar ba za a fito ya saka ta laraso gurin motar ta saka hannunta daya ta dafa zata leka ciki sai ya sauke gilashin motar, ta kalleshi ya kalleta ido cikin ido, ba tare da tace komai ba ta juya.
“Waira”
Ya kira sunanta da tattausan lafazi, ta juyo tana kallonsa sai ta fashe da kuka.
“Toh me na ce miki kuma na kuka?”
“Ka ce Waira”
Ta fada tana kuka hawaye na mata zuba kamar bata san zafinsu ba. Hannu ya mika ya ciro tissue a motar Abiey ya mika mata bata tare da ya ce komai ba, sai ta saka hannu ta karba ta share hawayen, sannan ta juya ta koma gurin da ake mata lessons dinta. Sai a sannan ya bude mota ya sauko ya shiga cikin gidan. A kujerarta ta zauna tana share hawayenta har lokacin. Dattijon dake mata darasin ya ce.
“Kin tafi ki gani ko Ummi ce?”
“Ta daga kai”
“Ummi tana can asibiti gurin Nimra”
“Me ya same ta?”
Ta tambaya cike da son sani, domin ita dai tun da Maleek yayi mata tsawa dazun saboda tafiyar su Shuraim sai ta boya a kitchen tana kuka duk abun da ya faru bata sani ba.
“Saboda rabata da aka yi da wanda take so”
“Amman miyasa Ummi ba zata bari ta aureshi ba”
“Baki san Ummi ta haife shi?”
“Na sani”
“Na gani ai”
“Ta ina?”
“Ummi ina kaunarki sosai”
Ta fada tana kara jimke hannun Ummi tare da dagowa ta sai Ummi ta kai jikinta kadan ta rumgumeta, suna haka aka turo kofar dakin Abiey ya shigo fuskarsa dauke da damuwa sosai.
“Tun da muka kawo yarinyar asibiti kin ki barta ta huta, a gabanki dazun likitan ya fada mana cewar hutu take bukata, na san kuma idan kina dakin nan ke ba zaki huta ba ita ma ba zata huta ba”
Ummi ta daga jikin Nimra ta mike tsaye gaba daya tana kallonta da hawaye a idonta.
“Mutuwa kadai ta isa ta shiga tsakanin uwa da ya Abiey, idan bana kusa da ita damuwata karuwa take, kuma zamana a kusa da ita ita kuma kara mata damuwa yake”
“Dan Allah ki kwantar da hankalinki, ciwo ne fa kawai zata ji sauki ta tashi kamar ba ayi ba, yanzu da wanne zan ji tashin ha kalinki ko ciwonta?”
Ummi ta sauke kai kasa ba tare da ta sake cewa Abiey komai ba ta saki hannun Nimra ta juya ta fice daga dakin. Abiey ya zauna a kujerar data tashi yana kallon Nimra dake kallonsa oxygen a hancinta da bakinta. Ya dade yana kallonta sannan ya mike tsaye ba tare da yace da ita komai ya nufi kofa sai ta cire Oxygen din dake bakinta ta ce.
“Abiey ka yafe min dan Allah ka yi hakuri”
Ya juyo da sauri ya dawo ya zauna ya kai hannu ya shafa goshinta.
“Da ban yafe miki ba, ba zan so asibitin nan kuma har na shigo cikin nan ba, kin yi kuskure a matsayinki na ya kuma yar adam, ni kuma na yafe miki a matsayina na mahaifinki, Allah ya baki lafiya kuma yayi miki albarka”
“Ameen Abiey”
Ta fada tana jin sanyi a ranta.
“Abiey da gaske Ummi ita ta haifi Ameer”
Abiey yayi jimm kamar ba zai ce komai ba, be mamakin sanin da ta yi ba wata kila Ummi ce ta fada mata haka saboda ta warware mata tsakanin tsare da abawa, na haramcin aurenta da Ameer.
“Nimra kina a yanayin da be kamata mu yi doguwar magana da ke ba, hutu kike bukata a yanzu, idan kin samu lafiya sai mu yi magana kin ji”
“Abiey dan Allah ka fada min, ina son na sani, gaskiya ne ko?”
“Gaskiya ne Zahra ita ta haifi Ameer kuma jininta ne”
“Amman Abiey miyasa bata tare da shi? Mutanen da yake nunawa a matsayin iyayensa su waye su?”
“Idan kika samu lafiya zan fada miki komai da kaina, fata dai yanzu ki samu lafiya karki zurfafa tunani zai kara haifar miki da damuwa i love you you should know that”
Ya sumbanci goshinta hawayensa na diga a saman kanta, sai ta yi murmushi ta lumshe ido tana jin son mahaifin nata a ranta. Bata bude idon ba har ya fice daga dakin, yana tafe yana tunanin Ummi a ransa, tausayinta ya cika masa zuciya fiye da kullum, shi da yake a tsakanin rayuwar yarsa da rasata yana jin kamar ba zai iya jurewa idan ya rasa ta, saboda mugun son yayansa da yake da kuma shakuwa da yayi da su, balle kuma Ummi da ta rayu a tsaye shekara da shekaru babu danta a kusa da ita, alhalin yana raye a yanzu kam ya tabbatar ciwon nan yana tare da ita, ta wannan babin kan ya jinjina mata matuka. Ya isa gurin da su Ummi da Dr Zajnab, Yesmin da Juwairiyyya, Mahmood da Maleek suke zaune har da Namra. Ummi na ganinsa ta mike tsaye sai yayi mata alama da ta zauna.
“Matukar kika ce zaki tare a dakin can to mota zan saka ki mu tafi gida yanzu nan, domin na ga alamar ba zaki barta ta samu hutu ba”
Ummi ta koma ta zauna suna kallonta.
“Ba a barin marar lafiya shi kadai ai”
“Toh ga Dr nan sai ta tafi gurinta ta zauna, ke kuma sai ki tashi mu tafi gida saboda babu kowa a cikin gidan an kwashe duk kun zo nan kun tare, kamar ni ne ba ni da lafiya”
Duk sai da suka yi murmushi da ba su shirya masa ba har Ummi dake cikin damuwa.
“Abiey idan kai ne baka da lafiya ai har masu gadin gidan sai sun tare a nan”
Maleek ya fada yana daga zaune a dayan carpet din da aka shimfida. Abiey yayi murmushi ya ce.
“Balle ma ba zan yi ba, sai dai Umminku”
“Ummin ma muna sonta Abiey”
Namra ta fada, sai duk suka saka dariya kamar babu damuwa a ransu. Sun dan taba hira sannan ya wuce tare da Maleek Juwairiyyya, aka bar Namra daman tace ba zata tafi ba, sai Yesmin dake lake da Mamarta wato tsohuwar likita Dr Zainab inda suka tare a dakin Nimra, harabar ta zama daga Mahmood sai Ummi da Abbie ya hana ta shiga ciki da Namra wacce ganin halin da yar'uwar haihuwarta take ciki yake daga mata hankali.
Abiey na gaba zaune Maleek na tuka motar Juwairiyyya na baya tana taba wayarta, titi kawai Abiey yake kallo amman hankalinsa yana wani gurin har suka isa gida. Masu gadin suka bude musu gate, kamin Maleek yaja motar su shiga ciki Police din da tarbi Humaira ya iso gurin motar Maleek na ganin hakan ya saukewa Abiey gilashinsa domin ta side dinsa ya tsaya.
“Ranka ya dade, dazun na so na baku wayar da yarinyar nan ta bari da wasika amman ban samu dama ba saboda kun fita hankali a tashe”
“Wace yarinya?”
Abiey ya tambaya domin shi be san abun da ke faruwa ba ma.
“Yarinyar da ta so dazun akan cewar ita kawar Nimra ce tana son ta ganta wai wayar Nimra ma tana hannunta, toh na zo na kira wayarka a tambayi Nimra ko ta san da zuwanta ko kuma akwai wanda ya santa a gidan, gudun kar mu barta ta shiga wani abu ya faru bayan dokar da ka saka mana cewar kar mu sake barin Nimra ta fita, toh fitowar da aka yi da ita cikin rashin lafiya sai yarinyar ta saki wayar da takardar hannunta ta gudu, mun bita sai dai ba mu samu nasarar kamata ba saboda ta shiga wata motar kuma mai tukin yaja da gudu sun tafi, sai dai muna son fadada bincike idan ka ba mu dama”
Abiey ya mika hannu ya karbi wayar da takardar with curious face. Maleek ma da mamakin guduwar ya ja motar suka shiga compound din gidan, Juwairiyyya ce ta fara fita, Abiey ya warwar takardar ya fara karantawa bayan ya gama duba wayar da ya tabbatar ta yarsa ce.
‘I'm sorry Nimra, ban dauka abun zai kai ga haka ba, ina tunanin kiran wayata da kika ba zai gamsar da ke ba kamar ganin wannan sakon nawa a rubuce, na rubuto ne saboda na kara tabbatar miki kuma na jadda miki cewar ni ban tana jin kaunarki ko digo daya a zuciyata ba, na san zaki min kallon maci amana, amman yayanki ya fara ai ni kawai fansa na dauka, kuma ki gode Allah ban taba mu'amala dake ba, wata kila da sai abun yafi taba ki, i wish you all the best, i kila da wanda zai nuna miki so kuma wanda zaki fada sonsa a nan gaba
Ameer’
Sunansa ne daga karshe tare da sa hannunsa, Abiey na gama karantawa ya mikewa Maleek yana jin wata sabuwar tsanar Ameer a ransa. Maleek ya karba ya karanta.
“Me kake tunani idan ta karanta wannan sakon? Yaron nan so yake kawai ya kasheta”
“Ta sani ai, Ummi ta fada mana haka dazun kamin ka zo, kuma tace shi yayi silar da aka kaita asibiti, daman na fada mata ai bata yarda ba ne, amman ni na san waye Ameer, ba zai taba sonta ba ko dan tana kanwata, sai dai yayi amfani da ita ya cin ma wata manufa”
Abiey yaja dogon tsaki ya bude motar ya fita ya nufi sashensa. Maleek ya juya gafensa da zimmar bude gambun motar ya hango Waira dake tsaye nesa da motar rike da dan zomonta tana kallon motarsu, jiran take waye zai fito mazaunin direban ko Ummi ce, domin ita kadai take son gani. Samun kansa yayi da tsayawa kallonsa kasancewar bakin gilashi ne na waje baya iya ganin na ciki, sai dai na ciki ya ga na waje, idonta yayi sumtum kamar an dafa shi saboda kukan da ta ci na tafiyar Shuraim. Ganin kamar ba za a fito ya saka ta laraso gurin motar ta saka hannunta daya ta dafa zata leka ciki sai ya sauke gilashin motar, ta kalleshi ya kalleta ido cikin ido, ba tare da tace komai ba ta juya.
“Waira”
Ya kira sunanta da tattausan lafazi, ta juyo tana kallonsa sai ta fashe da kuka.
“Toh me na ce miki kuma na kuka?”
“Ka ce Waira”
Ta fada tana kuka hawaye na mata zuba kamar bata san zafinsu ba. Hannu ya mika ya ciro tissue a motar Abiey ya mika mata bata tare da ya ce komai ba, sai ta saka hannu ta karba ta share hawayen, sannan ta juya ta koma gurin da ake mata lessons dinta. Sai a sannan ya bude mota ya sauko ya shiga cikin gidan. A kujerarta ta zauna tana share hawayenta har lokacin. Dattijon dake mata darasin ya ce.
“Kin tafi ki gani ko Ummi ce?”
“Ta daga kai”
“Ummi tana can asibiti gurin Nimra”
“Me ya same ta?”
Ta tambaya cike da son sani, domin ita dai tun da Maleek yayi mata tsawa dazun saboda tafiyar su Shuraim sai ta boya a kitchen tana kuka duk abun da ya faru bata sani ba.
“Saboda rabata da aka yi da wanda take so”
“Amman miyasa Ummi ba zata bari ta aureshi ba”
“Baki san Ummi ta haife shi?”
“Na sani”
“Na gani ai”
“Ta ina?”