← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 170

Sashe 8

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka suka yi ta gardama akan kwallo da yan kwallo kai ka rantse da Allah su kadai a gidan domin muryarsu kawai ake jin tana tashi a bangaren, ba su ba ba Mahaifinsu ba domin tsohon dan kwallon kwando ne, ya san in and out na wasanin da yawa na duniya. A take laulayi da dan bacin ran da Maleek yake ji ya washe fess daman haka yake so ya zauna yayi ayi hirar abun da ya shafi maza tare da maza yan'uwansa, ya kan ji sakewa da sukunin zuciya da nishadi kamar kar a rabu, mahaifinsa kuma ya fi kowa fahimtar abun da yake so wannan ya saka yake kokarin faranta ransa.

AMEER POV.

“Me ya hada ka da Balarabe?”

Ya aje spoon din da yake cin abinci da shi ya kalli Momy ko be tambaya ba ya san ita ta fada, domin ita kadai ta san abin da ya faru kare da karau a gaban idonta aka yi komai.

“Tambayarka na ke”

Daddy ya fada rai a bace, sai kanensa suka kalli Ameer, ba za su ce basu saba gani ba sai dai ya zama kamar bakon abu ne a gurinsu Daddy yayi ma Ameer fada ko ya nuna masa bacin ransa akan wani abun ko da kuwa ran nasa be masa dadi ba.

“Aiki na saka shi yayi min shirme”

“Shi ne zaka daga hannu ka mari babban mutum kamar Malam Balarabe?”

Ameer ya masa kallon mamaki domin a gurinsa ba wani abun ba ne.

“Daddy a karkashinmu yake”

“Shi ya baka damar ka wulakanta shi?”

Daddy ya kalli Safna.

“Je ki kira Malam Balarabe”

Safna ta mike tsaye domin cika umarnin mahaifinta, Ameer ya bita ta kallo kamin ya juyo ya kalli mahaifinsa kamar yayi magana sai kuma ya saka hannu ya dauki spoon dinsa ya cigaba da cin abincin, Baba Balarabe ya shigo bakinsa kumshe da sallama, Daddy da Momy suka amsa masa ban da Ameer dake kara jin haushinsa har a yanzu.

“Ranka ya dade gani”

Daddy ya kalli Ameer fuska babu alamun wasa ya ce.

“Ba shi hakuri”

Not just him even Momy da kanensa sai da suka kalli Daddy with shock balle kuma da aka bawa umarnin.

“Hakuri Daddy for what?”

“For marinsa da ka yi”

Baba Balarabe yayi fararat ya ce.

“Babu komai Alhaji, ai komai ya wuce tun jiya, hakurin da ka ba ni ma ya wadatar”

Daddy ya daga masa.

“Babu ruwanka a wannan maganar, Ameer umarni nake baka ka bashi hakuri na ce”

Wasu takwayen numfashi ne suka fito da gudu daga cikin Ameer suka fita ta hancinsa suka suka shiga da gudu kai kace wani yakin duniya ake a jikinsa, ba komai ba sai bacin rai. Baya son ya kunyata Daddy a dole ya bude bakin da halshe ke hadewa da hakori ya ce.

“Ka yi hakuri”

Daddy ya daka masa tsawa rai a bace.

“Say his name and ask for his forgiveness”

Ameer ya kalli Daddy yana jin kamar ba a taba wulakanta shi a duniya ba irin yau.

“Ka yi hakuri Balarabe”

“Baba Balarabe”

Daddy ya maimaita.

“I'm sorry Baba Balarabe”

“In Hausa”

“Ka yi hakuri Baba Balarabe”

Ya fada muryarsa na rawa irin rawar bacin rai da bakincikin an saka shi bawa wanda yake gani kaskantacce hakuri. Daddy ya kara dowara da na shi.

“Ka yi hakuri Malam Balarabe”

“Babu komai na gode da karamci Alhaji Allah ya kara kusanci da ma'aiki”

Baba Balarabe ya fada cikin farinciki domin a gurinsa Daddy ya gama masa komai tun da ya mutunta shi duk da kasancewar a karkashinsa yake. Sai da Baba Balarabe ya fice sannan Daddy ya kalli Ameer da ya matse spoon din hannunsa hannunsa nata rawa kamar mai jin sanyi.

“Karka sake dagawa wanda ya haife murna balle har ka saka hannu ka mareshi, saboda yana neman abun da zai ci a gidanku ba shi yake nufin Allah baya son shi ba, kuma ba shi zai baka damar wulakanta shi ba, na baka dama ka ji dadi rayuwa ka yi yadda kake so saboda ina kaunarka, na barka dukiyata ka wataya ka yi yadda kake so saboda kar wani ya fika jindadi ko gata, ban yi haka saboda ka wulakanta na kasa da kai ba, ban yi haka saboda na nuna maka akwai banbanci tsakaninka da talaka ba, ban yi haka dan ka wulakanta mutumen da sai Allah ya tsayar da ni ya tambaye ni akan me na bar ďana ya wulakantasu ba, duniyar da ta tashi ka gani ban tara ta dan ta gurbata tarbiyarka ba”

Yadda ko wane harafi da lafazi yake fitowa daga bakin Daddy ya sanar da iyalansa bacin ransa akan abun da ďan da yake kauna fiye da komai a duniya ya aikata. Ameer ya saki spoon din ya mike tsaye ya fice daga harabar da suke karyar kumallon yana jin yadda duniyarsa gaba daya take tafasa tana fitarta da bakin hayakin kara mai matukar yaji da kaifi saboda bacin rai, da za a fasa zuciyarsa a yanzu wata kila da an tararda goraba da garwashin wuta a ciki. Bedroom dinsa ya shiga, duk wani abu da yake a kasa sai da yayi ball da shi yana ta buga kafarsa a kafa yana cizon baki kamar zai fasa Iips din.

“Duk saboda kai Maleek aka min wannan abun”

Ya nufi gurin da ya saba aje keys dinsa ya dauka ya fice. Kamar wanda baya son rayuwarsa haka yake tukin yana sauka daga kan titi sai kuma ya hau, sa'arsa daya babu motoci sosai a titin unguwarsu. Gurin daya yada zango a jiya a nan ya sake yada zango a yau din ma, sai dai a yau cikin motarsa yake zaune bayan ya bude murfin motar yana ta kallin itatuwan dake gurin, tunanin abun da zai yi rama wulakanci da Maleek yayi masa amman ya sake ta ina zai rama idan ya kulla wannan ya kwance wacan.

“Sannu dai”

Ya ji an fada bayan mintuna uku da wucewar wata mota ta gabansa ta dawo baya ta faka bayansa, dagowa yayi ya kalli kyakkyawar budurwar da idanuwanta suka taba arba da ita, kunnensa na kokarin turawa kwakwalwarsa daddadar muryarta domin tuna inda ta taba jin muryar.

“Sannu dai”

Ya samu kansa da amsawa duk da kasancewar yana cikin bacin rai.

“Kamar kai ne mutumen jiya mai bura ko?”

Yayi murmushi da be san ta inda ya fito masa ba ya fito daga cikin motar.

“Shi ne”

“Yau ba busar ko kana cikin damuwa ne?”

Ya kalleta da mamaki a fuskarsa.

“Kina nazartar halayyar dan'adan ne?”

Ta yi murmushin daya kara mata kyau.

“Ina zaune tare da mahaifiyata, ina yawan fahimtar damuwarta, hakam ya bude min kofar fahimtar damuwar wasu”

Ya dan tabe baki try to smile sai kuma ya boye shi.

“Wani ne ya bata min rai, ina ta kokarin ganin na rama that's why I'm here”

“Miyasa ba zaka yafe masa ba?”

“Be cancanci yafiya ba, ya wulakanta ni kuma ya saka mahaifina ya wulakanta irin wulakancin da ban tana mafarki ba, yayi min abun da na fi tsana a duniya”

“Who's that stupid guy?”

“Wani sakarene da zan koya masa hankali soon”

“In that case kai ma ka yi bincika wani abin da ya fi tsana, so that ya dandana dacin da ka ji, sai dai ban ci ka wuce iya yadda yayi maka ba, zaka iya bincikar abin da baya so sai ka yi masa shi ka ga na zuza kenan”

Ta fada da murmushi a fuskarta sannan ta nufi motarta.

“Kar na yi latti bye, sai wata rana idan Allah ya sake hada mu but next time karka yarda mu hadu na ganka da bacin ran nan kuma karka ce min baka rama ba”

Kallonta kawai Ameer yake cike da burgewa har ta shige motarta ta barshi a gurin tsaye.

“You're right yarinya, na fi kowa sanin abin da ya fi tsana kanki na ja kin kawo shawara, nice to meet you”

Ya fada da murmushi a fuskarsa kamar ba shi ne ya gama fushi a yanzu ba.

______________
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*

_Na Khadeeja Candy_

5️⃣

“Ko wace dakika da mintuna idan suka wuce basa dawowa, rashin dawowar yana nufin rasa abubuwa da dama ciki har da lokaci idan baka yi amfani da shi a lokacin da ya dace ba, kyaunku ba zai tabbatar har a bada ba, ku yi aure a lokacin da maza suke ganinku suna yaba surarku har suna sha'awar aurenku, idan lokaci ya wuce za ku neme su ku rasa a lokacin ido zai rufe wata kila ku fadawa wanda be dace da aurenku ba, ba ni da buri a yanzu kamar ganin aurenku”

Ta sauke hannunta daga fuskar Nimra tana murmushi.

“Zamu yi aure Ummi, ni kin riga da kin san inda da wanda nake so kuma da zarar ya dawo daga Umra zan masa magana ya turo, sai dai ki yi ma Namra wa'azi ta rika sauraren masu zuwa gurinta, domin ita ce mai girman kai”

Namra dake ta danne danne da complete ta dago a fusace tana kallon kanwarta, wato Husainarta.

“Okay haka kike zama gurin Ummi kina min munafurci ko? Kina ruwanki da rayuwata? Maybe I'm not ready now ko kuma dukan masu zuwan basu min ba”

Ummi ta lankwasa kai tana kallon yarta.

“Na fa san halinki Namra, taya za a ce duk samarin dake nuna suna sonki babu wanda yayi miki?”

“Ummi I'm serious gaba dayansu ni ba su min ba”

“Ba ki sake jiki da su taya za'ayi ki san wadanda suka miki? Da wandanda basa miki?”

Cewar Nimra, domin ita ce mai far'a da saurin sabo ga son mutane, yadda take friendly da kowa sai ka dauka tana kaunar duk namijin da ta yi arba da shi ne.

“Nimra this is my life, can you please mind your own business? Ni fa ba irinki ba ce kowa far'a kowa dariya har wanda be kamata ace yana sonka ba ya zo yana maka maganar soyayya”

“Ummi See? Kin ga abun da nake fada miki ko? Fadin rai ba zai bar ta ta kula samari ba”

Namra ta dauki fillon kujera ta jefawa Nimra, Hajiya Zahra ta yi saurin saka hannunta ta tare.
Chapter 8 · 0% Book details