Sashe 46
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta yatsina fuska ta tashi ta nufin dinning table, da kanta ta shiga hada ma kanta abubuwan da take son karyawa da su even though ba komai da komai da suka saba karyawa da shi Ummi da dafa tare da Hanne ba. Farfesun kayan cikin da plate din dankali da ruwan zafi sai kayan hada tea, sannan ta koma ta dauko bread for Waira domin Nimra bata damu da shan tea tare da bread ba, ta fi son ta zuna dankali enough ta saka masa miyar farfesu ta ci ta koshi ta dora da tea sama, sauran kam basa haka sai dai kowa ya ci farfesun da dabam wani lokacin ma basa ra'ayin cin komai sai kayan kwalama.
“Hanne akwai cake a bridge please ki dumama, ko zata iya ci”
“Toh ranki ya dade”
Ta koma kitchen ta dauki cake din kamar yadda Nimra ta bukata ta saka a oven. Nimra ta zaunar da Waira kasa ta matsa dayan gefen ta zauna ta fara hada tea Waira nata kallon yadda take zuba wani abun cikin wani tana juyawa kamin a gama kamshi mai dadi ya cika mata hanci, daman yawunta ya dade da tsinkewa ganin farfesun dake wani kamshi na dabam ba kamar na su ba. Sai da Nimra ta gama hada tea tsab tana kokarin karbar cake din da Hanne ke mika mata Maleek ya soma saukowa without making any sound daman baka jin saukarsa ko hawansa idan yana tafiya, yana sanye da material ash colar wanda yayi matukar yi masa kyau ya haska fatarsa da bakin gashin kansa sai dai rama ta samu muhalli a fuskarta kadan hakan kuma ya karawa goshinsa haske, kamar ance daga kai ki kalli stairs haka Waira ta yi tana ganin Maleek ne sai ta mike tsaye da sauri kafarta ta kifar da tea da da Nimra ta hada, ta taka bread din da Nimra ta aje mata a gabanta bata ko tsaya gurin Nimra ba sai ta nufi dinning ta kwanta kasa taja kafafuwanta ta shiga da jikinta karkashi ta boya. Maleek kam tsaye yayi yana kallonta ya san tsoronsa take kuma ya cancanci ta tsorata idan ta ganshi saboda marin da yayi mata ba kadan ba ne, shi kansa ya ji ba dadi a dazun da ta ganshi ta yi ihu yanzu kuma ta nemi gurin boya, be dace ya mareta ba from first place sai dai idonsa ya rufe a lokacin baya iya gane hakan sai a yanzu da ya aikata. Nimra ma kallonta take bayan ta mike tsaye domin kadan ya rage tea ya bata mata tufafi.
“Ikon Allah ke kuma haka kike?”
Namra ta fada tana leka karkashin table din da mamaki. Juyawa Maleek yayi ya koma dakinsa, daman ba a falon zai karya ba, idan be yi breakfast a bangaren mahaifinsa ba to ya kan sauko ya debi abun da zai iya ci ya koma sama ta karya ko kuma Ummi ta kai masa da kanta, domin baya cin abincin tare da yan'uwansa mata, kamar yadda baya zama a falon idan suna nan.
“Ya wuce fito Hajiya”
Namra ta fada tana mikewa tsaye ta dawo kan cushion da tea dinta tana sha. Nimra ta nufo table din ta leka karkashi sai ta hangota tana ta kuka jikinta na rawa. Hannu ta miko mata sai ta kama hannun hakan ya bata damar janyota a hankali har ta fito. Ta koma da ita gurin da suka zauna dazun daman tuni Hanne ta gyara gurin, dankali Nimra ta fara dauka ta mika mata, sai ta karba ta kai bakinta tana taunawa a hankali shi kam ba laifi zata iya cinsa duk kuwa da kasancewar ba wani dadinsa ta ji ba sai dai abu ne da aka soya da mai da sai gishi kuma ta saba cin gishiri a garinsu. Karamin plate Nimra ta cika mata da dankali ta aje mata gabanta, sannan ta dauki karamin bowl ta zuba mata fesfesun kayan cikin ta saka mata spoon ta aje mata. Waira na ganin mai nama sai ta aje dankalin hannunta ta dauki bowl din wani abun kallo ne a gareta domin a garinsu da akushi suke cin abincin sai kuma abun da aka yi da wood itace kenan, tabawa ta yi ta murza sai ta ji shi da sulbi, ta mika hannu ta taba plate din da aka zuba mata dankali shi ma ta jishi kamar wannan, ta daga spoon din da Nimra ta saka mata sama tana kallo ta matsa shi ta murza tana ta mamakin yadda ake iya cin abinci da shi gashi har wani haske yake kamar zinari.
“Yau ta fara ganin plate ne?”
Tambayar Namra.
“I don't think so, jiya ba Ummi ta bata fruit a plate ba, sai dai wata kila bata samu natsuwar tsayawa ta kula da plate din ba sai yau”
Dukansu kallonta suke, har ta cire spoon din ta aje kasa ta saka hannunta tana dauko kayan cikin a hankali ta kai bakinta ta fara taunawa, ďanďannon farin maggi da kuma species da seasoning bata taba cin irinsa ba, wannan ya saka yana sauko a kanta ya kaiwa kwakwalwarta sako, sai ta ji kanta ya dauki wani ziza tana hadewa ya shiga cikinta sai hanjinta suka bata no a matsayin amsa domin sun ji bakon abun da ba za su iya dauka ba, a take ta dawo da naman ba shi kadai ya zo ba har da fruit din da ta ci da safe sai da ta amayar da shi tas a gurin. Namra ta jefar da cup din tea ta ita ma ta fara amai domin kazantar wani tana daga ta wani ne da zuciyarsa bata da nisan tashin.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
24
“Fita da ita waje please mun shiga uku, Nimra kin janyo mana fitina”
Cewar Namra tana fashewa da kuka domin rabonta ta ganin kazanta irin wannan ta amai har ta manta, and the most annoying thing is tana cin abinci Waira ta yi amai.
“Hanne ki fita da ita waje na ce, gaskiya ba zamu zauna da yarinyar nan gidan nan ba”
Ta fada a tsaye tana jin kamar ta fashe da kuka, Nimra kam kasa magana ta yi sai dai ta ji babu dadi kuma kazantar aman ya daga mata hankali. Hanne taja hannun Waira da sauri ta fitar da ita falon ta kaita can kusa da Garden ta tsayar rai a mace tana ta mata masifa domin ta san ita zata kwashi aman.
“Idan ba shegen kwadayi ba, kin ga abincin da ba irin na ku ba kuma sai kin ci, gashi nan yanzu kin janyo min aiki, Wallahi ba dan Hajiya ba da sai dai ki saka hannunki ki kwashe amanki da kanki mahaukaciyar yarinya kai”
Ta dangwari goshinta har sai dai Waira ta yi baya kamar zata fadi, ta ja tsaki ta juya ta koma tana jin kamar ta yi ma Waira duka. Waira ta saka haka hannunta ta share bakinta sannan ta duka ta zauna a gurin hawaye na sauko mata, gaba daya sai ta ji rayuwarta ta baya take marmari ta saba da can da acan ta yi amai sai dai Eid ya wanke mata baki ya zaunar da ita ba ya nuna mata kyama haka ba, ta kalli hannunta dake zugi ta fashe da kuka, can kuma ta mike tsaye ta nufi hanyar Garden din tana leken gurin da take ganin yayi mata yanayi da garinsu saboda itatuwan da suke gurin da shuke shuke, da sauri ta karasa tana jin kamar ace akwai wata hanya da za a bulle a gurin ta tsinci kanta a garinsu. Cikin Garden din ta shiga ta daga kanta sama tana kallon itatuwan sai gata tana murmushi da hawaye a lokaci daya, bayyana yadda ta yi marmarin hawan tsauni da icen bata lokaci ne, ta taka har gurin swimming pool tana kallon ruwan da aka tara a gurin sannan ta nufi gurin da tsuntsaye suke kebe tana kallonsu fuskarta fes kamar ba ita ce ke kuka dazun ba, dawowa ta yi gurin itacen ta kama dayan da hannun daya tana tunanin hawa saboda dayan ciwo yake mata, duk yadda zata yi ta hau icen sai ta kasa saboda hannu daya kawai take iya aiki da shi, a nan ta rumgume icen abarbar ta fashe da kuka ta taba kanta tana jin kamar ace beranta yana nan dake cire mata kewa, kamin ta sulale kasa ta zauna a hankali, ta cire ribbon din da kanwar Dr Shuraim Maimoon ta saka mata a kai gashinta ya watse ya sauko gaba daya a bayanta, sai ta kwatanta irin zagen da Mahmood yayi mata dazun ta zana mutane biyu, ta zana beranta da wani irin zane mai ban dariya ta zana zakara iya yadda ta ga ya iya, sannan ta nuna na farkon idonta na tara hawayen da suke daf da zubo mata
“Eid...”
Ta nuna na biyu.
“Sulen”
Ta nuna berata.
“Bulat”
Haka ta yi a gurin zanen zakaran shi ma ta fadi sunansa hawaye na sauko mata sosai su ne kadai mutanen da ta yi marmari domin su ne kadai take jin sanyinsu, ta taba zoben dake wuyanta ta rumgume kanta kuka sosai marar sauti. Duk abun da take Maleek na tsaye jikin Window dakinsa hannayensa zube a aljihu yana kallonta, kamin ya juyo ya fito daga dakin ya sauko downstairs gaba daya a daidai lokacin da Ummi ta shigo falon tare da Abiey domin Namra ta kai karar Waira gurin mahaifinta wai ba zata iya zama da ita gida daya tana musu ihu da kazanta ba.
“In that case sai a maida ta BQ ta zauna tare da Hanne”
Abiey ya fada domin yana goyon bayan abun da yayansa suke so. Ummi ta gigiza kai domin hukuncin be yi mata ba sam.
“Haba ya za'ayi yarinyar da muke son ta sake jiki mu fahimce ta ta fada mana danginta a maidata cikinsu zamu barta gurin Hanne ta zauna gashi ko lafiya bata da”
“Hanne akwai cake a bridge please ki dumama, ko zata iya ci”
“Toh ranki ya dade”
Ta koma kitchen ta dauki cake din kamar yadda Nimra ta bukata ta saka a oven. Nimra ta zaunar da Waira kasa ta matsa dayan gefen ta zauna ta fara hada tea Waira nata kallon yadda take zuba wani abun cikin wani tana juyawa kamin a gama kamshi mai dadi ya cika mata hanci, daman yawunta ya dade da tsinkewa ganin farfesun dake wani kamshi na dabam ba kamar na su ba. Sai da Nimra ta gama hada tea tsab tana kokarin karbar cake din da Hanne ke mika mata Maleek ya soma saukowa without making any sound daman baka jin saukarsa ko hawansa idan yana tafiya, yana sanye da material ash colar wanda yayi matukar yi masa kyau ya haska fatarsa da bakin gashin kansa sai dai rama ta samu muhalli a fuskarta kadan hakan kuma ya karawa goshinsa haske, kamar ance daga kai ki kalli stairs haka Waira ta yi tana ganin Maleek ne sai ta mike tsaye da sauri kafarta ta kifar da tea da da Nimra ta hada, ta taka bread din da Nimra ta aje mata a gabanta bata ko tsaya gurin Nimra ba sai ta nufi dinning ta kwanta kasa taja kafafuwanta ta shiga da jikinta karkashi ta boya. Maleek kam tsaye yayi yana kallonta ya san tsoronsa take kuma ya cancanci ta tsorata idan ta ganshi saboda marin da yayi mata ba kadan ba ne, shi kansa ya ji ba dadi a dazun da ta ganshi ta yi ihu yanzu kuma ta nemi gurin boya, be dace ya mareta ba from first place sai dai idonsa ya rufe a lokacin baya iya gane hakan sai a yanzu da ya aikata. Nimra ma kallonta take bayan ta mike tsaye domin kadan ya rage tea ya bata mata tufafi.
“Ikon Allah ke kuma haka kike?”
Namra ta fada tana leka karkashin table din da mamaki. Juyawa Maleek yayi ya koma dakinsa, daman ba a falon zai karya ba, idan be yi breakfast a bangaren mahaifinsa ba to ya kan sauko ya debi abun da zai iya ci ya koma sama ta karya ko kuma Ummi ta kai masa da kanta, domin baya cin abincin tare da yan'uwansa mata, kamar yadda baya zama a falon idan suna nan.
“Ya wuce fito Hajiya”
Namra ta fada tana mikewa tsaye ta dawo kan cushion da tea dinta tana sha. Nimra ta nufo table din ta leka karkashi sai ta hangota tana ta kuka jikinta na rawa. Hannu ta miko mata sai ta kama hannun hakan ya bata damar janyota a hankali har ta fito. Ta koma da ita gurin da suka zauna dazun daman tuni Hanne ta gyara gurin, dankali Nimra ta fara dauka ta mika mata, sai ta karba ta kai bakinta tana taunawa a hankali shi kam ba laifi zata iya cinsa duk kuwa da kasancewar ba wani dadinsa ta ji ba sai dai abu ne da aka soya da mai da sai gishi kuma ta saba cin gishiri a garinsu. Karamin plate Nimra ta cika mata da dankali ta aje mata gabanta, sannan ta dauki karamin bowl ta zuba mata fesfesun kayan cikin ta saka mata spoon ta aje mata. Waira na ganin mai nama sai ta aje dankalin hannunta ta dauki bowl din wani abun kallo ne a gareta domin a garinsu da akushi suke cin abincin sai kuma abun da aka yi da wood itace kenan, tabawa ta yi ta murza sai ta ji shi da sulbi, ta mika hannu ta taba plate din da aka zuba mata dankali shi ma ta jishi kamar wannan, ta daga spoon din da Nimra ta saka mata sama tana kallo ta matsa shi ta murza tana ta mamakin yadda ake iya cin abinci da shi gashi har wani haske yake kamar zinari.
“Yau ta fara ganin plate ne?”
Tambayar Namra.
“I don't think so, jiya ba Ummi ta bata fruit a plate ba, sai dai wata kila bata samu natsuwar tsayawa ta kula da plate din ba sai yau”
Dukansu kallonta suke, har ta cire spoon din ta aje kasa ta saka hannunta tana dauko kayan cikin a hankali ta kai bakinta ta fara taunawa, ďanďannon farin maggi da kuma species da seasoning bata taba cin irinsa ba, wannan ya saka yana sauko a kanta ya kaiwa kwakwalwarta sako, sai ta ji kanta ya dauki wani ziza tana hadewa ya shiga cikinta sai hanjinta suka bata no a matsayin amsa domin sun ji bakon abun da ba za su iya dauka ba, a take ta dawo da naman ba shi kadai ya zo ba har da fruit din da ta ci da safe sai da ta amayar da shi tas a gurin. Namra ta jefar da cup din tea ta ita ma ta fara amai domin kazantar wani tana daga ta wani ne da zuciyarsa bata da nisan tashin.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
24
“Fita da ita waje please mun shiga uku, Nimra kin janyo mana fitina”
Cewar Namra tana fashewa da kuka domin rabonta ta ganin kazanta irin wannan ta amai har ta manta, and the most annoying thing is tana cin abinci Waira ta yi amai.
“Hanne ki fita da ita waje na ce, gaskiya ba zamu zauna da yarinyar nan gidan nan ba”
Ta fada a tsaye tana jin kamar ta fashe da kuka, Nimra kam kasa magana ta yi sai dai ta ji babu dadi kuma kazantar aman ya daga mata hankali. Hanne taja hannun Waira da sauri ta fitar da ita falon ta kaita can kusa da Garden ta tsayar rai a mace tana ta mata masifa domin ta san ita zata kwashi aman.
“Idan ba shegen kwadayi ba, kin ga abincin da ba irin na ku ba kuma sai kin ci, gashi nan yanzu kin janyo min aiki, Wallahi ba dan Hajiya ba da sai dai ki saka hannunki ki kwashe amanki da kanki mahaukaciyar yarinya kai”
Ta dangwari goshinta har sai dai Waira ta yi baya kamar zata fadi, ta ja tsaki ta juya ta koma tana jin kamar ta yi ma Waira duka. Waira ta saka haka hannunta ta share bakinta sannan ta duka ta zauna a gurin hawaye na sauko mata, gaba daya sai ta ji rayuwarta ta baya take marmari ta saba da can da acan ta yi amai sai dai Eid ya wanke mata baki ya zaunar da ita ba ya nuna mata kyama haka ba, ta kalli hannunta dake zugi ta fashe da kuka, can kuma ta mike tsaye ta nufi hanyar Garden din tana leken gurin da take ganin yayi mata yanayi da garinsu saboda itatuwan da suke gurin da shuke shuke, da sauri ta karasa tana jin kamar ace akwai wata hanya da za a bulle a gurin ta tsinci kanta a garinsu. Cikin Garden din ta shiga ta daga kanta sama tana kallon itatuwan sai gata tana murmushi da hawaye a lokaci daya, bayyana yadda ta yi marmarin hawan tsauni da icen bata lokaci ne, ta taka har gurin swimming pool tana kallon ruwan da aka tara a gurin sannan ta nufi gurin da tsuntsaye suke kebe tana kallonsu fuskarta fes kamar ba ita ce ke kuka dazun ba, dawowa ta yi gurin itacen ta kama dayan da hannun daya tana tunanin hawa saboda dayan ciwo yake mata, duk yadda zata yi ta hau icen sai ta kasa saboda hannu daya kawai take iya aiki da shi, a nan ta rumgume icen abarbar ta fashe da kuka ta taba kanta tana jin kamar ace beranta yana nan dake cire mata kewa, kamin ta sulale kasa ta zauna a hankali, ta cire ribbon din da kanwar Dr Shuraim Maimoon ta saka mata a kai gashinta ya watse ya sauko gaba daya a bayanta, sai ta kwatanta irin zagen da Mahmood yayi mata dazun ta zana mutane biyu, ta zana beranta da wani irin zane mai ban dariya ta zana zakara iya yadda ta ga ya iya, sannan ta nuna na farkon idonta na tara hawayen da suke daf da zubo mata
“Eid...”
Ta nuna na biyu.
“Sulen”
Ta nuna berata.
“Bulat”
Haka ta yi a gurin zanen zakaran shi ma ta fadi sunansa hawaye na sauko mata sosai su ne kadai mutanen da ta yi marmari domin su ne kadai take jin sanyinsu, ta taba zoben dake wuyanta ta rumgume kanta kuka sosai marar sauti. Duk abun da take Maleek na tsaye jikin Window dakinsa hannayensa zube a aljihu yana kallonta, kamin ya juyo ya fito daga dakin ya sauko downstairs gaba daya a daidai lokacin da Ummi ta shigo falon tare da Abiey domin Namra ta kai karar Waira gurin mahaifinta wai ba zata iya zama da ita gida daya tana musu ihu da kazanta ba.
“In that case sai a maida ta BQ ta zauna tare da Hanne”
Abiey ya fada domin yana goyon bayan abun da yayansa suke so. Ummi ta gigiza kai domin hukuncin be yi mata ba sam.
“Haba ya za'ayi yarinyar da muke son ta sake jiki mu fahimce ta ta fada mana danginta a maidata cikinsu zamu barta gurin Hanne ta zauna gashi ko lafiya bata da”