Sashe 37
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
“Ba dai Maimoon ba kam Shuraim ta cinye min ƴa ana kwana, ko kuma ta mutu ace ita ta kasheta? Aa lalala ni ai lamarinta a yanzu ya ba ni tsoro, bana jin zata kwana a gidan nan ma ka maida ita inda ka daukota can gurin police din su sai su sama mata inda zata kwanta”
Bude baki yayi zai yi magana sai mahaifinsa ya goyawa Hajiya baya.
“Gaskiya, karka aikata irin kuskuren dana aikata wanda nake nadama har yanzu, garin taimako ka jefa kanka da mu a matsala, ko kuma ita yarinyar ma gaba daya”
“Bata yarda da kowa yanzu Abba kai ma ka gani kuma idan nace zan maidata fitina ce”
“Bata yarda da kowa idan za a kaita abujar kai zaka kaita ne? Ji min wata maganar banza? Karka janyo mana masifa Shuraim dan Allah ka maida yarinyar nan gurin tun ranka be bace ba”
Waira ta dago ta kalli Shuraim tana iya fahimtar fada ake masa, wata kila kuma duk saboda ita ne.
“Hajiya mun riga mun yi magana da su, sun ce da safe za su zo su dauke ta sai kuma yanzu na maida musu ita? Idan na kaita a can wani abun ya sameta still ba mu fita daga zargi ba”
“Kara ta mutu a hannunsu, duk abun da zai sameta ya sameta a can, ba nan ba, ka tashi ka kai yarinyar nan na ce maka Shuraim”
Ta daka mashi tsawar data saka shi sa hannu biyu ya dafe kansa da hannu biyu. Waira ta sakarwa Hajiya Hajara ido daman tun da suka dannenta suka mata wanka take tsoronsu balle kuma yanzu da take yi ma Shuraim fada har ya rike kansa.
“Shikenan zan mai da ita”
“Yanzu kuma ba sai anjima ba, daman can ban da karanbani dauko ta ba, haka kawai daga yarinya tana kuka sai ka ce sai ka zo mana da ita”
Tausayinsa sai ya kama Waira ta san duk saboda ita ake masa fada, ba zata fadi abun da suke cewa ba, amman ta san akanta ne suke masa fadan, shi ma tausayinta yaji hakam ya hana shi yi mata allurar da ya siyo sai ya bude maganin kawai ya balla ya saka mata a baki, sai ta bude bakin a hankali saboda yarda da ta yi da shi ba zai cutar da ita ba ya saka mata maganin ta fara sotsawa jin yana da daci ba a yadda ta yi tsammani ba ya saka ta yi yunkurin zubarwa sai ya girgiza mata kai.
“Maimoon kawo ruwa”
Ya kwalawa kanwarsa kira, sai gata da kofin ruwan data debo a tap ta mika masa ya karba ya kai mata a baki, abun ka da wanda be saba ba da zo hade maganin sai ya tsaya mata a makoshi ta kasa hadewa ta dawo da shi a hannunta, sai ya karba ya balla wani ya bata ta kora mata da ruwa a dole ta hade da sauri haka yayi ta mata har ta anye sannan ya rika hannunta suka mike tsaye. Ya nufi gurin da ta zubar da kayanta ya dauka ya mika mata ta rike da hannun da baya ciwo, shi kuma ya rike wuciyar hannun ya jata suka fice daga falon, binshi kawai take kamar wata igiya har ya isa gurin motar da suka shigo dazun, a tsoro ya kamata jikinta ya fara rawa a taken hawayen na jini suka fara mata zuba, shi kanshi yayi mamakin ganin hawayen jini a idonta. Bude motar yayi ya dauko tissue ya goge mata hawayen, hakan nan ya ji yana sha'awar rumgumarta saboda ya kwantar mata da hankali, ba dan yau kadai ba har da gobe dan ya san da mota za aje da ita Abuja. Rumgume ta yayi yana shafa bayanta alamar rarrashi, yanayinsa sai yayi mata kamar na Eid da baya son kukanta. Bata san lokacin data kankameshi ba ta fashe da wani irin kuka mai karfi, jikinta na bata rabuwa zai yi da ita, bata san yaushe zata sake ganinsa ba, haka kuma bata san hannun da zata fada ba, bata san waye zai fahimce kamar shi ba. Dagota yayi ya duba idonta a yanzu din ma hawayen jinin ne, ya dauko wani tissue ya goge mata sannan ya bude mata front seat, wani irin dauke numfashi ta yi ta kalleshi, sai ya dafa kafadarta zai shigar da ita sai ta rufe ido gam jikinta ya fara rawa, hannunsa ya saka ya bude mata idon tana kallonsa sai ya girgiza mata kai, bata fasa hawayen ba, shi kuma be fasa goge mata ba har ya zaunar da ita cikin motar, sai ta ki yarda ta zauna a inda ya zaunar da ita ta sulale kasa ta matse kanta ta zauna a inda ya kamata ce kafafuwanta ne a gurin. A hankali ya rufe motar saboda kar ya daga mata hankali ya zagoyo ta dayan side din ya shiga ya saka maganinta da tufafinta a back seat ya kunan motar a hankali ya fara tukawa kadan kadan har ya fice daga gidan. Ganin ta ki daina hawayen kuma ta kasa rufe idon ta kasa daina kallonsa ya saka yayi mata murmushi ya mika hannunsa ya rike hannunta.
Bude baki yayi zai yi magana sai mahaifinsa ya goyawa Hajiya baya.
“Gaskiya, karka aikata irin kuskuren dana aikata wanda nake nadama har yanzu, garin taimako ka jefa kanka da mu a matsala, ko kuma ita yarinyar ma gaba daya”
“Bata yarda da kowa yanzu Abba kai ma ka gani kuma idan nace zan maidata fitina ce”
“Bata yarda da kowa idan za a kaita abujar kai zaka kaita ne? Ji min wata maganar banza? Karka janyo mana masifa Shuraim dan Allah ka maida yarinyar nan gurin tun ranka be bace ba”
Waira ta dago ta kalli Shuraim tana iya fahimtar fada ake masa, wata kila kuma duk saboda ita ne.
“Hajiya mun riga mun yi magana da su, sun ce da safe za su zo su dauke ta sai kuma yanzu na maida musu ita? Idan na kaita a can wani abun ya sameta still ba mu fita daga zargi ba”
“Kara ta mutu a hannunsu, duk abun da zai sameta ya sameta a can, ba nan ba, ka tashi ka kai yarinyar nan na ce maka Shuraim”
Ta daka mashi tsawar data saka shi sa hannu biyu ya dafe kansa da hannu biyu. Waira ta sakarwa Hajiya Hajara ido daman tun da suka dannenta suka mata wanka take tsoronsu balle kuma yanzu da take yi ma Shuraim fada har ya rike kansa.
“Shikenan zan mai da ita”
“Yanzu kuma ba sai anjima ba, daman can ban da karanbani dauko ta ba, haka kawai daga yarinya tana kuka sai ka ce sai ka zo mana da ita”
Tausayinsa sai ya kama Waira ta san duk saboda ita ake masa fada, ba zata fadi abun da suke cewa ba, amman ta san akanta ne suke masa fadan, shi ma tausayinta yaji hakam ya hana shi yi mata allurar da ya siyo sai ya bude maganin kawai ya balla ya saka mata a baki, sai ta bude bakin a hankali saboda yarda da ta yi da shi ba zai cutar da ita ba ya saka mata maganin ta fara sotsawa jin yana da daci ba a yadda ta yi tsammani ba ya saka ta yi yunkurin zubarwa sai ya girgiza mata kai.
“Maimoon kawo ruwa”
Ya kwalawa kanwarsa kira, sai gata da kofin ruwan data debo a tap ta mika masa ya karba ya kai mata a baki, abun ka da wanda be saba ba da zo hade maganin sai ya tsaya mata a makoshi ta kasa hadewa ta dawo da shi a hannunta, sai ya karba ya balla wani ya bata ta kora mata da ruwa a dole ta hade da sauri haka yayi ta mata har ta anye sannan ya rika hannunta suka mike tsaye. Ya nufi gurin da ta zubar da kayanta ya dauka ya mika mata ta rike da hannun da baya ciwo, shi kuma ya rike wuciyar hannun ya jata suka fice daga falon, binshi kawai take kamar wata igiya har ya isa gurin motar da suka shigo dazun, a tsoro ya kamata jikinta ya fara rawa a taken hawayen na jini suka fara mata zuba, shi kanshi yayi mamakin ganin hawayen jini a idonta. Bude motar yayi ya dauko tissue ya goge mata hawayen, hakan nan ya ji yana sha'awar rumgumarta saboda ya kwantar mata da hankali, ba dan yau kadai ba har da gobe dan ya san da mota za aje da ita Abuja. Rumgume ta yayi yana shafa bayanta alamar rarrashi, yanayinsa sai yayi mata kamar na Eid da baya son kukanta. Bata san lokacin data kankameshi ba ta fashe da wani irin kuka mai karfi, jikinta na bata rabuwa zai yi da ita, bata san yaushe zata sake ganinsa ba, haka kuma bata san hannun da zata fada ba, bata san waye zai fahimce kamar shi ba. Dagota yayi ya duba idonta a yanzu din ma hawayen jinin ne, ya dauko wani tissue ya goge mata sannan ya bude mata front seat, wani irin dauke numfashi ta yi ta kalleshi, sai ya dafa kafadarta zai shigar da ita sai ta rufe ido gam jikinta ya fara rawa, hannunsa ya saka ya bude mata idon tana kallonsa sai ya girgiza mata kai, bata fasa hawayen ba, shi kuma be fasa goge mata ba har ya zaunar da ita cikin motar, sai ta ki yarda ta zauna a inda ya zaunar da ita ta sulale kasa ta matse kanta ta zauna a inda ya kamata ce kafafuwanta ne a gurin. A hankali ya rufe motar saboda kar ya daga mata hankali ya zagoyo ta dayan side din ya shiga ya saka maganinta da tufafinta a back seat ya kunan motar a hankali ya fara tukawa kadan kadan har ya fice daga gidan. Ganin ta ki daina hawayen kuma ta kasa rufe idon ta kasa daina kallonsa ya saka yayi mata murmushi ya mika hannunsa ya rike hannunta.