Sashe 122
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi yayi ya nufi upstairs hakoransa basa rufuwa saboda farincikin da yake ciki, gaba daya a yau ji yake kamar an masa kyautar Waira. Ya shiga wanka yana murza sabulu a jikinsa yana rausayawa yadda zai rayu da Waira yake tunani, one day ace tare za su yi wanka, gata ta iya zuba shagwaba yadda zata narke masa a jiki tana kuka yake da raya a zuciyarsa. Ya fito wanka ya fada saman gado kamar wani karamin yaro ya saka tawul ya goge kansa. Ya gama shiryawa ya tsaya gaban madubi yana kallon kasan ya dauki wayarsa yana yi ma kansa selfie, a yanzu kam ya yarda son Waira ba kadan ya kama shi ba, domin soyayyarta na kokarin maida shi wani karamin yaro, shi da yake ganin ya fi karfin karamar yarinyar yar under 20yrs. A yanzu ya yarda soyayyar gaskiya bata bukatar ado, kuma babu ruwanta da kyau ko muni, haka ma babu ruwanta da talauci ko arziki matsayi ko asali, kamin son Waira ya kama shi babu irin dokokin da be gindayawa soyayyarsa ba amman a yanzu ya mantasu gaba daya babu ko sharadi daya da ya gindayawa kansa.
Ya shiga bangaren Daddy yana ta zuba kamshi kamar kullum, fuskarsa har annuri take saboda farinciki da yake ciki. Daddy ma kallo ďaya yayi masa ya fahimci haka, sai kuma ya jidadin daman baya son yin maganar da shi a cikin wani yanayi na bacin rai.
“Fuskarka sake kamar ka san Mummy ta maka favorite dinka”
“Kai kace ta yi min? Ko kuma ita ta yi da kanta”
Daddy ya daga hannunsa a kokarinsa na gyara hannun Egyptian Jallabiyar dake jikinsa saboda ya ji dadin cin abincin na dare da kyau.
“Ni na ce ta girka maka, saboda ina da special abu da zan fada maka kuma zan roka ka min, and i hope ba zaka ce min aa, na yanke shawara ne ba tare da saninka ba, sai dai ban yi hakan dan na bata maka ba, sai dan ina ganin zai taimaki rayuwarka, domin abu ne da na dade ina jira, kuma na ga kai kamar baya gabanka dan haka zan matukar farinciki idan ka amsa min, sai dai ban ce ka amsa a dole ba, domin ka san na fi kowa son abun da kake so, ina son farincikinka fiye da komai”
Ameer yaja kujera ya zauna gabansa ya soma faduwa zuciyarsa na raya masa kamar Daddy zai gabatar masa da wanda be zata ba ne a matsayin wanda zai aura, ba dan ya san wacece ba, sai dan ya fahimci kamar hakan din ne duba da kalaman da ke fitowa a bakin Daddy. A take yaji kamar an datse masa rabin jindadin da ya shigo da shi gidan, a kokarin na ganin ya kawar da tunani ko bukatar Daddy yayi yunkurin yin wani abu.
“Ina tunanin babu wani abun da zaka bukata ko ka gabatar min na ce maka aa ko da kuwa zai cutar da ni, balle kuma na san ba zaka so abun da zai cutar da ni ba, zan baka dama ka fara saboda ka gabatar da cewar kana son magana da ni tun a jiya da safe, amman nima ina da maganar da nake son na fada maka mai muhimmanci”
Daddy yayi masa alama da hannu.
“Go ahead you first..”
“No Daddy ai ka riga ni”
“No ina saurarenka ai kai ka fara”
“Amman ni ne babba dan haka na baka umarni ka fara fada min”
Ameer yayi murmushi, sannan ya dauki plate ya bude abincin ya fara zubawa.
“Daddy idan baka manta ba, last year da aka yi rigima da Maleek da kuma kanwarsa Nimra akan wata yarinya da aka gani bayan motarsa har na ce ban santa ba ka tuna?”
“Ai ban manta ba go ahead”
“A zahirin gaskiya, na boye maka ne kawai kamar yadda na fada maka a baya, na san yarinyar lokacin da fushin zuciya ya dauke ni na tafi Katsina na shiga wani kauye da ban san kowa ba, kuma a al'adar mutanen garin idan bako ya zo suna aurar masa yar garin kamin su ba shi damar zama a cikin garinsu, to nima haka ne ya faru da ni, suka aura min yarinyar nan Waira sannan suka ba ni damar zama a garin, sai dai ko kamin safiya ta waye na fahimci al'adunsu da addininsu ya sha banban da nawa, kuma ba zasu yarda su bar ni na yi kalar addininsu ba, dan haka na gudu da yarinyar na baro garin ba tare da saninsu ba, da na zo da ita sai na barta a dajin ta nan maciji ya cijeta, kuma at that time na yi zaton ta mutu dan haka na nadeta na sakata a bayan motar na barta a nan ya dawo gida, saboda a wacan lokacin ban san yadda zan gabatar da ita a matsayin matata ba, kuma ni ban ma dauki wacan auren a matsayin aure ba, sannan ina ganin sigarta da tawa ma ba kala daya ba, but Now Daddy want to correct my mistakes ina son duk wanda na batawa na faranta masa kuma na roki yafiyarsa, now am already na karbi Waira a matsayin mata, kuma zan sakata a gaba muje har garin iyayenta saboda sanin asalinta, na san wannan magana ce babba amman na boye maka ne saboda zuciya tana raya min bad things a wacan lokacin amman yanzu Alhamdulillah komai ya canja and i loved her”
Kusan ya kwashe kafafuwan Daddy na cewa ya aureta tun a can, wani irin mamaki da ban al'ajabi ne ya bayyana a fuska Daddy ya sarkafe hannunsa da juna yatsunsa suka shiga cikin juna ya rasa ta ina zai kama zaren zancen.
Abiey ya aje cin abincin dare da yake ci, ya kalli Ummi fuskarsa da shauki irin na wanda ke dauke da labari mai dadi. Ita ma dubansa take zaman jiran ya gama cin abinci take ta gabatar masa da kudin Ameer.
“Ina da labari mai dadi da zan fada miki, amman ba zan fada ba sai kin ba ni goro”
With surprise din da ya bayyana yanzu a fuskarta take sake duba Abiey.
“It seems like, we both have a good news to share, nima ina da labari mai faranta zuciya da zan baka”
Abiey ya girgaza kai yana fadada murmushin dake fuskarsa ya ce.
“Nawa ya fi naki dadin sauraro da kuma saka farincikinki, domin wani abu ne wanda ni da ke da duk wani makusanci yake jira, ba ma kamar ke da kika tashi hankalinki akansa”
Ta zurfafa a tunani wai ko zata hango albishir din da Abiey yake mata, amman ta kasa ganin komai, ta san bata gabatar masa sa zancen Namra ba na neman a bawa Shuraim dama ya turo magabanta sa, balle tace Abiey zai amince ne ba tare da jan wani dogon zance ba, haka ma ba shi da good understanding da Ameer balle ta ce Ameer ya fara sanar masa ne kamin ita.
“Na gane, Mr Bashir ya fada maka abun da Ameer ya fada min yau”
Abiey ya dauki spoon din ya cigaba da cin abincinsa wannan karon dariya yake.
“Baki canka daidai ba, Mr Bashir tun a lokacin da kike kokarin ganin Ameer ya san gaskiya rabon da na yi waya ko magana da shi, kuma wannan albishir din ba abu ne da ya shafi ďanki Ameer ba, wannan na ďana ne Maleek”
Cike da son sani Ummi ta kara matsawa kusa da mijinta ta rike spoon din da yake cin abincin ta saka cikin plate ta maida plate din gefe.
“Fada min wani abu ne mai faranta zuciya da ya shafi Maleek? Kuma ka ce abun da na dade ina jira ne”
“Kwarai kuwa”
Ya furta sannan ya dauki ruwa ya sha yana murmushin dake bayyana farincikin dake zuciyarsa ya ce.
“Madam sai fa kin ba ni goro”
“Shikenan zan girka maka abinci mai dadi gobe”
“Abinci kin fi kowa sanin be dame ni ba, kawai ki ce zaki min tukuicin zama ba tare da kin yi wani aikin ko da daukar cup ne ba har na tsawon wata daya”
Ummi ta san abu ne mai wahala ta iya haka, domin tana son taba aiki musamman ta tasan mijinta baya son cin abincin a waje sai dole, ta fi kowa sanin bukatarsa na son ta daina yin komai saboda ta samu hutu yadda ya dace. Sai dai ƙaguwa da ta yi na son jin albishir din ya saka ta amince.
“Na yarda”
Abiey ya mika mata hannu.
“Deal... ”
Sai ta yi dariya ta girgiza kai.
“Kai dai ba zaka taba girma ba”
“Girma saboda me? Dama ace akwai yara sai na san na girma amman daga ni sai ke a daki ki dauko min zancen girma, ai ni yadda kika san yaro dan shekara goma sha bakwai haka nake jin kaina ke kuma yar sha ďaya”
Ummi ta fashe da dariya sosai kamar ba ita ba.
“See har na manta when last ki min irin dariyar nan, shikenan kin maida ni tsoron karfi da yaji, alhalin zan iya auro yar Shida ko bakwai sa'ar Waira”
“Ko dai Wairar kake so? Daman ku maza komai kankantar mace ko tsufanta burgeku take, to an riga ka dai sai hakuri”
“Aa ni ido be taba kaiwa can ba, amman idon ďana Maleek ya kai gurinta, shi dai ya ga ruwan dake masa wanka, daman kuma na dade da fahimtar haka, kawai dai na saka masa ido ne na ga iya gudun ruwansa, na dade da fahimtarsa, ke baki ga haka ba? Yadda ya sauko ya canja rayuwa tun daga zuwanta gidan nan har zuwa yau?”
Kamar hoto haka Ummi ta tsaya kallon Abiey, gaba daya sai ta ji kamar an cire mata lakka jikinta babu karfi har na numfashi, duk wani farinciki da hanzari da take da shi na son fadawa Abiey abun da Ameer ya gabatar mata sai ya kau, rudani da tunani ya cika kwakwalwarta. Daman Maleek ya fada masa yana son Waira tun da dadewa ko kuma yanzu ne ya fada masa saboda ta fada masa Ameer ya ce yana sonta.
“Are you not happy?”
Ya shiga bangaren Daddy yana ta zuba kamshi kamar kullum, fuskarsa har annuri take saboda farinciki da yake ciki. Daddy ma kallo ďaya yayi masa ya fahimci haka, sai kuma ya jidadin daman baya son yin maganar da shi a cikin wani yanayi na bacin rai.
“Fuskarka sake kamar ka san Mummy ta maka favorite dinka”
“Kai kace ta yi min? Ko kuma ita ta yi da kanta”
Daddy ya daga hannunsa a kokarinsa na gyara hannun Egyptian Jallabiyar dake jikinsa saboda ya ji dadin cin abincin na dare da kyau.
“Ni na ce ta girka maka, saboda ina da special abu da zan fada maka kuma zan roka ka min, and i hope ba zaka ce min aa, na yanke shawara ne ba tare da saninka ba, sai dai ban yi hakan dan na bata maka ba, sai dan ina ganin zai taimaki rayuwarka, domin abu ne da na dade ina jira, kuma na ga kai kamar baya gabanka dan haka zan matukar farinciki idan ka amsa min, sai dai ban ce ka amsa a dole ba, domin ka san na fi kowa son abun da kake so, ina son farincikinka fiye da komai”
Ameer yaja kujera ya zauna gabansa ya soma faduwa zuciyarsa na raya masa kamar Daddy zai gabatar masa da wanda be zata ba ne a matsayin wanda zai aura, ba dan ya san wacece ba, sai dan ya fahimci kamar hakan din ne duba da kalaman da ke fitowa a bakin Daddy. A take yaji kamar an datse masa rabin jindadin da ya shigo da shi gidan, a kokarin na ganin ya kawar da tunani ko bukatar Daddy yayi yunkurin yin wani abu.
“Ina tunanin babu wani abun da zaka bukata ko ka gabatar min na ce maka aa ko da kuwa zai cutar da ni, balle kuma na san ba zaka so abun da zai cutar da ni ba, zan baka dama ka fara saboda ka gabatar da cewar kana son magana da ni tun a jiya da safe, amman nima ina da maganar da nake son na fada maka mai muhimmanci”
Daddy yayi masa alama da hannu.
“Go ahead you first..”
“No Daddy ai ka riga ni”
“No ina saurarenka ai kai ka fara”
“Amman ni ne babba dan haka na baka umarni ka fara fada min”
Ameer yayi murmushi, sannan ya dauki plate ya bude abincin ya fara zubawa.
“Daddy idan baka manta ba, last year da aka yi rigima da Maleek da kuma kanwarsa Nimra akan wata yarinya da aka gani bayan motarsa har na ce ban santa ba ka tuna?”
“Ai ban manta ba go ahead”
“A zahirin gaskiya, na boye maka ne kawai kamar yadda na fada maka a baya, na san yarinyar lokacin da fushin zuciya ya dauke ni na tafi Katsina na shiga wani kauye da ban san kowa ba, kuma a al'adar mutanen garin idan bako ya zo suna aurar masa yar garin kamin su ba shi damar zama a cikin garinsu, to nima haka ne ya faru da ni, suka aura min yarinyar nan Waira sannan suka ba ni damar zama a garin, sai dai ko kamin safiya ta waye na fahimci al'adunsu da addininsu ya sha banban da nawa, kuma ba zasu yarda su bar ni na yi kalar addininsu ba, dan haka na gudu da yarinyar na baro garin ba tare da saninsu ba, da na zo da ita sai na barta a dajin ta nan maciji ya cijeta, kuma at that time na yi zaton ta mutu dan haka na nadeta na sakata a bayan motar na barta a nan ya dawo gida, saboda a wacan lokacin ban san yadda zan gabatar da ita a matsayin matata ba, kuma ni ban ma dauki wacan auren a matsayin aure ba, sannan ina ganin sigarta da tawa ma ba kala daya ba, but Now Daddy want to correct my mistakes ina son duk wanda na batawa na faranta masa kuma na roki yafiyarsa, now am already na karbi Waira a matsayin mata, kuma zan sakata a gaba muje har garin iyayenta saboda sanin asalinta, na san wannan magana ce babba amman na boye maka ne saboda zuciya tana raya min bad things a wacan lokacin amman yanzu Alhamdulillah komai ya canja and i loved her”
Kusan ya kwashe kafafuwan Daddy na cewa ya aureta tun a can, wani irin mamaki da ban al'ajabi ne ya bayyana a fuska Daddy ya sarkafe hannunsa da juna yatsunsa suka shiga cikin juna ya rasa ta ina zai kama zaren zancen.
Abiey ya aje cin abincin dare da yake ci, ya kalli Ummi fuskarsa da shauki irin na wanda ke dauke da labari mai dadi. Ita ma dubansa take zaman jiran ya gama cin abinci take ta gabatar masa da kudin Ameer.
“Ina da labari mai dadi da zan fada miki, amman ba zan fada ba sai kin ba ni goro”
With surprise din da ya bayyana yanzu a fuskarta take sake duba Abiey.
“It seems like, we both have a good news to share, nima ina da labari mai faranta zuciya da zan baka”
Abiey ya girgaza kai yana fadada murmushin dake fuskarsa ya ce.
“Nawa ya fi naki dadin sauraro da kuma saka farincikinki, domin wani abu ne wanda ni da ke da duk wani makusanci yake jira, ba ma kamar ke da kika tashi hankalinki akansa”
Ta zurfafa a tunani wai ko zata hango albishir din da Abiey yake mata, amman ta kasa ganin komai, ta san bata gabatar masa sa zancen Namra ba na neman a bawa Shuraim dama ya turo magabanta sa, balle tace Abiey zai amince ne ba tare da jan wani dogon zance ba, haka ma ba shi da good understanding da Ameer balle ta ce Ameer ya fara sanar masa ne kamin ita.
“Na gane, Mr Bashir ya fada maka abun da Ameer ya fada min yau”
Abiey ya dauki spoon din ya cigaba da cin abincinsa wannan karon dariya yake.
“Baki canka daidai ba, Mr Bashir tun a lokacin da kike kokarin ganin Ameer ya san gaskiya rabon da na yi waya ko magana da shi, kuma wannan albishir din ba abu ne da ya shafi ďanki Ameer ba, wannan na ďana ne Maleek”
Cike da son sani Ummi ta kara matsawa kusa da mijinta ta rike spoon din da yake cin abincin ta saka cikin plate ta maida plate din gefe.
“Fada min wani abu ne mai faranta zuciya da ya shafi Maleek? Kuma ka ce abun da na dade ina jira ne”
“Kwarai kuwa”
Ya furta sannan ya dauki ruwa ya sha yana murmushin dake bayyana farincikin dake zuciyarsa ya ce.
“Madam sai fa kin ba ni goro”
“Shikenan zan girka maka abinci mai dadi gobe”
“Abinci kin fi kowa sanin be dame ni ba, kawai ki ce zaki min tukuicin zama ba tare da kin yi wani aikin ko da daukar cup ne ba har na tsawon wata daya”
Ummi ta san abu ne mai wahala ta iya haka, domin tana son taba aiki musamman ta tasan mijinta baya son cin abincin a waje sai dole, ta fi kowa sanin bukatarsa na son ta daina yin komai saboda ta samu hutu yadda ya dace. Sai dai ƙaguwa da ta yi na son jin albishir din ya saka ta amince.
“Na yarda”
Abiey ya mika mata hannu.
“Deal... ”
Sai ta yi dariya ta girgiza kai.
“Kai dai ba zaka taba girma ba”
“Girma saboda me? Dama ace akwai yara sai na san na girma amman daga ni sai ke a daki ki dauko min zancen girma, ai ni yadda kika san yaro dan shekara goma sha bakwai haka nake jin kaina ke kuma yar sha ďaya”
Ummi ta fashe da dariya sosai kamar ba ita ba.
“See har na manta when last ki min irin dariyar nan, shikenan kin maida ni tsoron karfi da yaji, alhalin zan iya auro yar Shida ko bakwai sa'ar Waira”
“Ko dai Wairar kake so? Daman ku maza komai kankantar mace ko tsufanta burgeku take, to an riga ka dai sai hakuri”
“Aa ni ido be taba kaiwa can ba, amman idon ďana Maleek ya kai gurinta, shi dai ya ga ruwan dake masa wanka, daman kuma na dade da fahimtar haka, kawai dai na saka masa ido ne na ga iya gudun ruwansa, na dade da fahimtarsa, ke baki ga haka ba? Yadda ya sauko ya canja rayuwa tun daga zuwanta gidan nan har zuwa yau?”
Kamar hoto haka Ummi ta tsaya kallon Abiey, gaba daya sai ta ji kamar an cire mata lakka jikinta babu karfi har na numfashi, duk wani farinciki da hanzari da take da shi na son fadawa Abiey abun da Ameer ya gabatar mata sai ya kau, rudani da tunani ya cika kwakwalwarta. Daman Maleek ya fada masa yana son Waira tun da dadewa ko kuma yanzu ne ya fada masa saboda ta fada masa Ameer ya ce yana sonta.
“Are you not happy?”