Sashe 114
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuwan wani tunanin ya tsayar da halshen Hajiya daga sarrafa kalmar da zata fito daga bakinta, sai ta yanke maganar tana kallon Ameer da yayi baya ya jingina da kofa, shi ma kallon Hajiyar yake cikin wani yanayi na tashin hankali. Ummi ta juya ta kalli Ameer da Hajiya ke kallo sannan ta juyo ta kalli Hajiya, sai wani sabon kuka ya kwankwaso mata kofa hawaye suka ce mata salamatu alaiki. Hajiya kam kallon Ameer kawai take babu dauke ido, surarta da zubin halittarsa suke tuna mata da ďanta Deen, yayinda wani bangare na zuciyarta ke raya mata abun da hankali da tunani ba zai dauka ba, balle har ta yarda. Ssi da Ummi ta yi da gaske sannan ta iya tsayar da kukanta, ta mikewa tsaye tana fadin.
“Hajiya Allah ya kara lafiya, zamu tafi daman na ce ya kawo ni ne na duba ki kawai”
“Ummi zauna”
Kamar saukar aradu haka ta ji maganar da Ameer yayi mata ta dira a kunnenta ta yi cikin kanta. Bata da kuzarin musa mass duk da kasancewar shi ne ďa ita kuma uwa, sai ta koma ta zauna gabanta ns bugawa da karfi, idonta kuma ta kafe shi gurin Ameer.
“Akwai abun da ya kamata ki warware ko ba haka ba? Zuciyata na hararon min wani abu, ni da Hajiyar da Humairah duk kin saka mana shakku. Warware maganar dake cikinki, fada min wani abun da ban sani ba, ba ni labarin yadda kika san tsohuwar nan”
Ummi na fargaba da tunanin kalmomin da zata hada ta fadi maganar ta sigar da Ameer da kuma Hajiya za su fahimceta. Ta tsinkayo Hajiya na karanta masa alakarsu.
“Ni uwar mijinta ce ta farko, mutumen da ta aura kamin ta auri mahaifinka, ni ce na haife shi, Bahijja da ka ji tana ambata ita ce kanwarsa, su biyu kawai Allah ya ba ni, sai kuma yanzu da na samu yan jikoki, wannan Humairah da ka sani yar Bahijja ce matar da ka ji tana tambaya, ita mahaifiyarka har ta haihu da Deen amman Allah be kawo abun da ta haifa da rai ba, shi ya tafi kuma shi ma abun da ta haifa ya tafi, ba dan ma mace ta haifa ba, Wallahi da na ce kai ďansa ne domin kamar ta yi yawa har ta bace, duk na kalleka sai na tuna da ďana...”
Ta kai karshe maganar, su kuma hawaye suka fara gudana a idon Ameer. Ummi na ganin haka ta mike tsaye da sauri tana kiran sunanshi.
“Ameer”
Sai ta sauke kansa kasa, duk yadda ya so gushewa ganin laifin Ummi ko daga mata kafa yayi mata uzuri a wannan babin sai abun ya gagara.
“Hajiya, ni ne ďan da kike zaton ya mutu, ba mace ba ce namiji ne, kuma ban mutu ba ina raye ni jikanki ne, ni ďan da aka haifawa ďanki ne”
Wani abu mai kama da mafarki kamar zahiri ne ya baibaiye Hajiya, ba dan hankalinta da yake tare da ita ba, da kuma kaifin tunani da Allah ya bata na gane komai ba tare da rikicewa ba, tabbas da babu abun da zai hana ba zata rikice a lokacin ba. Sai dai duk da haka sai ta ji kamar ba daidai ta ji abun da Ameer yake fada ba, dan haka ta sake fadar.
“Kasan abun da kake fadi ďan nan? Wacan jika da aka haifa min mace ce kuma bata zo da rai ba, kuma kuma an ba mu gawarta mu muka rufeta da kanmu, ko dai baka gane bayanin ba?”
“Ke ce dai abun zai miki wahalar fahimta a yanzu, wata gaskiya ce da zaki ganta kamar karya, wata kalar gaskiya ce mai wuyar karba, Ummi kin cutar da mu, ina jin kamar abun da kika fada be isa ya saka ki aikata abun da kika aikata ba, why Ummi why”
Wannan karon da kuka Ameer yake tambayarta, sannan ya karasa gurin Hajiya ya kai hannunsa ya taba kafarta mai lafiya, ya daga zanenta zuwa guiwarta ya shafa kafar ya kalli fuskarta mamaki da rashin yadda da karyar da suke kokarin mayar mata a matsayin gaskiya ya saka ta sakin baki da ido tana kallonsu, can kuma ta kalli Humairah ta ce.
“Humaira ke kin gane abun da kike nufi”
Hunairah da tun da ta fahimci abun da yake nan take kuka, ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana kara rushewa da wani sabon kukan.
“Dan Allah ku min bayani, kaina ya kasa dauka na kasa fahimta abun da kuke nufi”
Ummi ta koma ta zauna a kujerarta, yayinda Ameer ya kwantar da kansa a kafarta mai lafiyar hawaye dake fita a idonta suna zuba a kafar, ba tare da damuwa da tsabtar Hajiya ko kazantar ba, yau ya manta cewar kafar almajira mai yin bara a titi, mai zama a gidan da yake jin kyama da kazanta take rayuwa, shaukin son sanin mahaifinsa da kuma ganin kakarsa ya mantar da shi komai. Be taba tunanin haka ake ji idan aka hadu da uba ko dangi uba na kusa ba sai yau, lallai yau ya yarda shi ba ďan Mr Bashir ba ne, domin be taba jin shaukin da sarkewar zuciya dan gani ko tarayya da wani a cikin family Mr Bashir ma, amman gashi a yau yana yi, zuciyarsa har wani fisga take how he wish ace Mahaifinsa ma yana raye.
“Hajiya, ban yi zaton abun zai bayyana ta haka ba, ban yi zaton ta haka abun zai zo ba, ban san ta ina zan fara miki bayani ki fahimta ba, Ameer ji...ka... Kan...ki... Ne.... Ne.... Dan.... Da.... Na.... Na... Na... Na... Na....”
Sai numfashinta ya sarke da halshenta ta kasa karasa sentences din dake gaba.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un..... Ta ya? Ba yar ta mutu ba? Wa muka binne kenan?”
“Wadda kuka binne ba jikarku ba ce, ba ni na haifeta ba, ni ďa na haifa ba mace ba”
“Yanzu kuma kin kara rikita ni, toh da kika haife shi ina kika boye shi? A ina kika aje shi har ya girma? Idan ma gaskiya ne me zai saka ki aikata hakan?”
“Gaskiya ne Hajiya, Wallahi wannan yaron ďan Deen ne, jininsa ne ďan da na haifa ne”
Hajiya ta kalli Ameer tana bata fuska irin na tsofin dake kokarin ganin sun ci karfin kuka, amman ina sai da ta yi sai dai bata bari sautin kukan ya fito ba.
“Me yasa kika boye shi? Kamaninshi sak na Zaharardeen tun ranar da na fara ganinsa na ga kama yake da Deen, amman zuciyata bata raya min cewar shi jinina ba ne, me yasa kika boye shi? Me zaki yi tabbatar min da yaron nan jika ne? Ta ina zam gamsu?”
Ta inda Ummi ta ji zata iya, ta fara fede mata biri da wutsiya, ita kuka Humairah kuka Hajiya kuka Ameer hawaye.
Hajiya tayi kuri da ido sai hawaye take bayan gama kukan. Ummi ta share majina ta kalli Hajiya da yanayin da take ciki ta ce.
“Hajiya ki ce wani abu mana”
Hajiya ta kalleta ta kalli Ameer sai ta sauke dauke idonta.
“Dan Allah Hajiya ki yi magana ko da tsunuwa zaki furta min na cancanta, kuma na shirya tarbonta da Ameen, amman ni ban aikata hakan a nufin na cutawa kowa a cikinku ba, ban aikata haka ba saboda na son zuciya ba”
“Toh me zan ce Zahra?”
“Ki fadi duk abun da kike son fada Hajiya, na cancanta, na shirya neman afuwarki sai dai ban yo zaton abun zai zo mana ta wannan sigar ba, tunanina da zatona kuna kano har yanzu, ina ta kokarin shirya zuwa kano na kai Ameer a gurinki na nuna masa ku da sauran dangi kuma na roki yafiyarku”
“Zaharadeen be miki komai ba sai alheri Zahra, talaka ne, amman tufafinki baya bari ki wanke, sai dai ya wanke miki ya goge, ko da ya aureki baki iya girki ba, amman haka yake zaune da ke, sai dai ya siyo muku abinci ko ya girka, kamin ki fadi kina son wani abu ya aikata miki, kowa yace be zon Zahra Deen be son shi, saboda ke babu halin da be shiga ba, akan me zaki saka masa da wannan? Me ya miki? Cewar dole ce ta saka kika aikata saboda kina tsoron rasa rayuwarsa shin kin kai ni ni uwarsa ne? Ba gashi kin yi aure kin cigaba da rayuwa ba? Ni ko fa? Ba ni da mai maye min gurbinsa, duk na tuna cewar Deen ya tafi be bar min jika ba sai na yi kamar na yi hauka, zuciyarki bata raya miki ina bukatar ba ki kawo min shi ko sau daya na gani? Malam ya har ya bar duniya be san yana da jika ba, ya zaki yi da hakkinsa? Wace Wahala ce taki Malam be sha ba, amman sai ki saka masa da wannan? Saboda muna talakawa ne ko kuma saboda kina ganin ba mu da hakki ne? Shim kaunar Deen ne baki yi har yanzu ko kuma son zuciya ne kawai irin an ďan adam?”
Gefen mayafi Ummi ta saka ta share hawayenta tana jin wani gwarin guiwar magana yana tunkarota.
“Hajiya zaki iya tuna, wani lokaci da Deen ya tirsasa Dr Zainab yayar Abiey yin karya ta yi min kazafi cewar ina dauke da cutar HIV? Saboda kawai a fasa aurena da Abiey? Kuma yayi nasara Ammy da yan'uwanta suka ce ba zai aureni ba? Mutumen da na fara so aka saka mana ranar aure? Kuma ba a fadi haka ba sai a ranar da za a daura min aure? Bayan tara mutane da shela? Zaki iya tunawa?”
“Ramuwa kika yi kenan? Amman shi Deen ai ya aikata miki haka ne saboda yana kaunarki, tun da kuka taso yaron nan yake kaunar, kawai saboda ya san ba za'a yarda ya aureki ba ne ya saka shi aikata haka, kuma a cikin wasiyar da ya bar miki ai ya fada komai”
Ummi ta daga kai
“Kwarai ya fada min saboda yana sona ne, saboda yana tsoron rasa ni ne? Saboda yana son rayuwa da ni ne? Saboda idan babu ni a rayuwarsa zai iya shiga wani hali, komai yana cikin kaina ban manta ba”
Ta mike tsaye.
“Hajiya Allah ya kara lafiya, zamu tafi daman na ce ya kawo ni ne na duba ki kawai”
“Ummi zauna”
Kamar saukar aradu haka ta ji maganar da Ameer yayi mata ta dira a kunnenta ta yi cikin kanta. Bata da kuzarin musa mass duk da kasancewar shi ne ďa ita kuma uwa, sai ta koma ta zauna gabanta ns bugawa da karfi, idonta kuma ta kafe shi gurin Ameer.
“Akwai abun da ya kamata ki warware ko ba haka ba? Zuciyata na hararon min wani abu, ni da Hajiyar da Humairah duk kin saka mana shakku. Warware maganar dake cikinki, fada min wani abun da ban sani ba, ba ni labarin yadda kika san tsohuwar nan”
Ummi na fargaba da tunanin kalmomin da zata hada ta fadi maganar ta sigar da Ameer da kuma Hajiya za su fahimceta. Ta tsinkayo Hajiya na karanta masa alakarsu.
“Ni uwar mijinta ce ta farko, mutumen da ta aura kamin ta auri mahaifinka, ni ce na haife shi, Bahijja da ka ji tana ambata ita ce kanwarsa, su biyu kawai Allah ya ba ni, sai kuma yanzu da na samu yan jikoki, wannan Humairah da ka sani yar Bahijja ce matar da ka ji tana tambaya, ita mahaifiyarka har ta haihu da Deen amman Allah be kawo abun da ta haifa da rai ba, shi ya tafi kuma shi ma abun da ta haifa ya tafi, ba dan ma mace ta haifa ba, Wallahi da na ce kai ďansa ne domin kamar ta yi yawa har ta bace, duk na kalleka sai na tuna da ďana...”
Ta kai karshe maganar, su kuma hawaye suka fara gudana a idon Ameer. Ummi na ganin haka ta mike tsaye da sauri tana kiran sunanshi.
“Ameer”
Sai ta sauke kansa kasa, duk yadda ya so gushewa ganin laifin Ummi ko daga mata kafa yayi mata uzuri a wannan babin sai abun ya gagara.
“Hajiya, ni ne ďan da kike zaton ya mutu, ba mace ba ce namiji ne, kuma ban mutu ba ina raye ni jikanki ne, ni ďan da aka haifawa ďanki ne”
Wani abu mai kama da mafarki kamar zahiri ne ya baibaiye Hajiya, ba dan hankalinta da yake tare da ita ba, da kuma kaifin tunani da Allah ya bata na gane komai ba tare da rikicewa ba, tabbas da babu abun da zai hana ba zata rikice a lokacin ba. Sai dai duk da haka sai ta ji kamar ba daidai ta ji abun da Ameer yake fada ba, dan haka ta sake fadar.
“Kasan abun da kake fadi ďan nan? Wacan jika da aka haifa min mace ce kuma bata zo da rai ba, kuma kuma an ba mu gawarta mu muka rufeta da kanmu, ko dai baka gane bayanin ba?”
“Ke ce dai abun zai miki wahalar fahimta a yanzu, wata gaskiya ce da zaki ganta kamar karya, wata kalar gaskiya ce mai wuyar karba, Ummi kin cutar da mu, ina jin kamar abun da kika fada be isa ya saka ki aikata abun da kika aikata ba, why Ummi why”
Wannan karon da kuka Ameer yake tambayarta, sannan ya karasa gurin Hajiya ya kai hannunsa ya taba kafarta mai lafiya, ya daga zanenta zuwa guiwarta ya shafa kafar ya kalli fuskarta mamaki da rashin yadda da karyar da suke kokarin mayar mata a matsayin gaskiya ya saka ta sakin baki da ido tana kallonsu, can kuma ta kalli Humairah ta ce.
“Humaira ke kin gane abun da kike nufi”
Hunairah da tun da ta fahimci abun da yake nan take kuka, ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana kara rushewa da wani sabon kukan.
“Dan Allah ku min bayani, kaina ya kasa dauka na kasa fahimta abun da kuke nufi”
Ummi ta koma ta zauna a kujerarta, yayinda Ameer ya kwantar da kansa a kafarta mai lafiyar hawaye dake fita a idonta suna zuba a kafar, ba tare da damuwa da tsabtar Hajiya ko kazantar ba, yau ya manta cewar kafar almajira mai yin bara a titi, mai zama a gidan da yake jin kyama da kazanta take rayuwa, shaukin son sanin mahaifinsa da kuma ganin kakarsa ya mantar da shi komai. Be taba tunanin haka ake ji idan aka hadu da uba ko dangi uba na kusa ba sai yau, lallai yau ya yarda shi ba ďan Mr Bashir ba ne, domin be taba jin shaukin da sarkewar zuciya dan gani ko tarayya da wani a cikin family Mr Bashir ma, amman gashi a yau yana yi, zuciyarsa har wani fisga take how he wish ace Mahaifinsa ma yana raye.
“Hajiya, ban yi zaton abun zai bayyana ta haka ba, ban yi zaton ta haka abun zai zo ba, ban san ta ina zan fara miki bayani ki fahimta ba, Ameer ji...ka... Kan...ki... Ne.... Ne.... Dan.... Da.... Na.... Na... Na... Na... Na....”
Sai numfashinta ya sarke da halshenta ta kasa karasa sentences din dake gaba.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un..... Ta ya? Ba yar ta mutu ba? Wa muka binne kenan?”
“Wadda kuka binne ba jikarku ba ce, ba ni na haifeta ba, ni ďa na haifa ba mace ba”
“Yanzu kuma kin kara rikita ni, toh da kika haife shi ina kika boye shi? A ina kika aje shi har ya girma? Idan ma gaskiya ne me zai saka ki aikata hakan?”
“Gaskiya ne Hajiya, Wallahi wannan yaron ďan Deen ne, jininsa ne ďan da na haifa ne”
Hajiya ta kalli Ameer tana bata fuska irin na tsofin dake kokarin ganin sun ci karfin kuka, amman ina sai da ta yi sai dai bata bari sautin kukan ya fito ba.
“Me yasa kika boye shi? Kamaninshi sak na Zaharardeen tun ranar da na fara ganinsa na ga kama yake da Deen, amman zuciyata bata raya min cewar shi jinina ba ne, me yasa kika boye shi? Me zaki yi tabbatar min da yaron nan jika ne? Ta ina zam gamsu?”
Ta inda Ummi ta ji zata iya, ta fara fede mata biri da wutsiya, ita kuka Humairah kuka Hajiya kuka Ameer hawaye.
Hajiya tayi kuri da ido sai hawaye take bayan gama kukan. Ummi ta share majina ta kalli Hajiya da yanayin da take ciki ta ce.
“Hajiya ki ce wani abu mana”
Hajiya ta kalleta ta kalli Ameer sai ta sauke dauke idonta.
“Dan Allah Hajiya ki yi magana ko da tsunuwa zaki furta min na cancanta, kuma na shirya tarbonta da Ameen, amman ni ban aikata hakan a nufin na cutawa kowa a cikinku ba, ban aikata haka ba saboda na son zuciya ba”
“Toh me zan ce Zahra?”
“Ki fadi duk abun da kike son fada Hajiya, na cancanta, na shirya neman afuwarki sai dai ban yo zaton abun zai zo mana ta wannan sigar ba, tunanina da zatona kuna kano har yanzu, ina ta kokarin shirya zuwa kano na kai Ameer a gurinki na nuna masa ku da sauran dangi kuma na roki yafiyarku”
“Zaharadeen be miki komai ba sai alheri Zahra, talaka ne, amman tufafinki baya bari ki wanke, sai dai ya wanke miki ya goge, ko da ya aureki baki iya girki ba, amman haka yake zaune da ke, sai dai ya siyo muku abinci ko ya girka, kamin ki fadi kina son wani abu ya aikata miki, kowa yace be zon Zahra Deen be son shi, saboda ke babu halin da be shiga ba, akan me zaki saka masa da wannan? Me ya miki? Cewar dole ce ta saka kika aikata saboda kina tsoron rasa rayuwarsa shin kin kai ni ni uwarsa ne? Ba gashi kin yi aure kin cigaba da rayuwa ba? Ni ko fa? Ba ni da mai maye min gurbinsa, duk na tuna cewar Deen ya tafi be bar min jika ba sai na yi kamar na yi hauka, zuciyarki bata raya miki ina bukatar ba ki kawo min shi ko sau daya na gani? Malam ya har ya bar duniya be san yana da jika ba, ya zaki yi da hakkinsa? Wace Wahala ce taki Malam be sha ba, amman sai ki saka masa da wannan? Saboda muna talakawa ne ko kuma saboda kina ganin ba mu da hakki ne? Shim kaunar Deen ne baki yi har yanzu ko kuma son zuciya ne kawai irin an ďan adam?”
Gefen mayafi Ummi ta saka ta share hawayenta tana jin wani gwarin guiwar magana yana tunkarota.
“Hajiya zaki iya tuna, wani lokaci da Deen ya tirsasa Dr Zainab yayar Abiey yin karya ta yi min kazafi cewar ina dauke da cutar HIV? Saboda kawai a fasa aurena da Abiey? Kuma yayi nasara Ammy da yan'uwanta suka ce ba zai aureni ba? Mutumen da na fara so aka saka mana ranar aure? Kuma ba a fadi haka ba sai a ranar da za a daura min aure? Bayan tara mutane da shela? Zaki iya tunawa?”
“Ramuwa kika yi kenan? Amman shi Deen ai ya aikata miki haka ne saboda yana kaunarki, tun da kuka taso yaron nan yake kaunar, kawai saboda ya san ba za'a yarda ya aureki ba ne ya saka shi aikata haka, kuma a cikin wasiyar da ya bar miki ai ya fada komai”
Ummi ta daga kai
“Kwarai ya fada min saboda yana sona ne, saboda yana tsoron rasa ni ne? Saboda yana son rayuwa da ni ne? Saboda idan babu ni a rayuwarsa zai iya shiga wani hali, komai yana cikin kaina ban manta ba”
Ta mike tsaye.