← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 169 OF 170

Sashe 169

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ni ban gani ba”

“Baki nan lokacin amman taje kuma ba gashi mu munzo ba? Ke tsaya ma wai me kika sani a auren mace biyu?”

“Na sani ba, ka dauka ni jahila ce? Islamiyar da muke zuwa ai ina ganin masu miji daya su biyu, kuma Malam yana mana bayani ai, ni bana son na ga wata macen ta so ka, shiyasa nake son gobe ta yi mu tafi gida ma”

Gefen fuskarta ya sumbanta.

“Ni bana da wannan ra'ayin ma, baki ga Abiey ba tun bayan rasuwar Mahaifiyarsu Yasmeen be sake aure ba, ni ma bana son yawan aure mata daya ta wadace ni da yarana biyar ko hudu kamar dai Ummi”

Ta juyo ya kalleshi.

“Ni ina so da yawa kamar goma”

“Zaki iya haifar yara goma”

Dirty words ya watsa mata a kunne sai ta daga kai, alamar ta yarda.

“Laa ashe yarinyar nan ta lalace yanzu bata da kunya”

Ta yi saurin rufe fuskarta tana dariya sai ya rungume ta a kirjinsa daman duk tsayin nata iyakarta kafadarsa. Kamin goben ta yi Nuwaira duk ta matsu daman can bata son zuwa ba ita dai ta tsani Hajiya Jamila tun a lokacin da suke daf da zuwa Ummi ta fada mata abubuwan da Hajiya Jamila ta yi mata, sai ta ji duk ta tsaneta daman kuma ita bata iya tsanar mutum ba, gashi kuma ta yi mata zancen yan matan da suke gidan ita kuma ta maida abun gaske. Misalin sha daya na safe jirginsu ya tashi daga Katsina zuwa Abuja, a duk zaman jirgin Ameer yana kusa da matarsa hannunsa cikin nata, ba motsinta ba har numfashinta lura yake da yadda yake fita da shiga balle kuma idan ta yi zaman da be gamsu ba sai ta ji kamar zai yi effecting babynsa dake cikinsa ne.

Two days da dawowar wani sabon laulayi ya kama rufe Humairah daman tun da ta samu cikin kusan kullum cikin laulayi take idan ta yi wata daya lafiya wata biyu ko uku da zai zo sai ta ci kwakwar wahala. Around 2am mai ya tasheta sai ta sauka saman gadon a hankali ta nufi toilet a kasa ta zauna ta tara bakinta a ta yi da kwara aman. Tana cikin yi ta ji Ameer a bayanta yana shafa bayanta da hannunsa sai sannu yake fada mata cikin yanayin damuwa, kusan abun da ta ci da rana sai da ta amaye tass sannan ta samu sukuni, yana wanke mata tana hawaye domin tana wahala sosai da cikin nan. Da kansa ya cire rigar bachin dake jikinta ya cire tasa ya kunna shower ya tara jikinta sai ya tsaya daga bayanta ya saka hannayensa a gaba a karkashin cikinta ya daga mata cikin yayi sama sai ya lumshe ido tana jin kamar babu cikin ma gaba daya a jikinta nauyin cikin ya cire lamo ta yi a jikinsa ruwan dake sauka a saman kansa suna saukowa a kanta, kuzarin da ta rasa sai ta ji ya dawo har bachi ya fara daukarta a haka.

“My guideline”

Ta bude idon a hankali.

“Bachi zaki ki yi?”

Ta daga masa kai tana kara kwantawa a kirjinsa. Ya kashe shower ya dauko tawul ya daura mata ya daura ya riko hannunta suka fito saman gado ya kwantar da ita sai ta bata masa fuska domin ta san ba lallai ne ta iya bachin ma.

“Shiiiiiiiiii zaki yi bachi yanzu nan?”

“How?”

“Ina zuwa”

Wani lotion ya dauko ya matsa a hannunsa ya fara shafa mata a kafarta tana mata massage a hankali, a duk time din da yayi rubbing kafarta sai ya sumbance feet dinta har ya gama ya bude drawer ya dauko karamin cup din honey ya aje kusa sannan ya hau saman gadon ya ya fara bin jikinta yana shafa mata cikin siga mai dadi da kwantar da hankali.

“Kina bukatar cin wani abu? Kin ga ki amayar da komai”

“Aa bana so”

“Please ko kadan ne”

Kamar zata fashe masa da kuka ta ce.

“Ka daina min magiya bana so mana”

“Na daina, I'm sorry”

Ya sumbanci goshinta, sannan ya dagata ya jingina da gadon ita kuma ya kwanta jikinsa zumar ya dauka ya bude yana saka yatsansa ya lakato ya kai mata a baki.

“Bana so na ce bana son komai ba”

Da sauri ya janye hannunsa, domin ko kadan baya son bacin ranta a yanzu, ba dan tana da cikinsa sai dan hallayarta da dabi'un gashi ya sameta cikakkiyar mace, ba kamr yadda yake tunanin duk budurwa ta ta wuce 20 ba za a samu samu budurci a tare da ita ba, amman abun ya canja tunaninsa kuma ya tabbatar masa har gobe akwai na kwarai, and Humairah mace ce mai yawan dora shi a hanyar kwarai, tana nuna masa kulawa yadda yake son samu a mace, a yanzu kam ya yarda idan Allah ya hana ka wani abun zai baka wanda ya fishi ko ba komai Humairah cikakkiyar mace ce mai wayo da kaifin basira. Samun cikin da ta yi kuma sai ji a duniyar babu abun da ya fi masa wannan farincikin, be taba sanin dadin da ake ji idan aka taka matakin zama uba ba sai da matarsa ta samu ciki, wani lokaci haka zai zuba mata ido yayi ta kallonta irin he can't believe cikinsa ne a jikinta ya kamanin yarsa ko dansa zai kasance abun da ya yake yawan ayyanawa a ransa.

Digon zumar da ya sauka a bakinta ta lashe sai ta dan karkato ta kalleshi.

“Hubby”

“Hummm me kike so?”

“Zan sha zumar”

“I knew it ke da kike sarkin kwadayi, kuma zuma tana kara lafiya sosai fa”

Ya sake daukowa ta bude baki idan ya lakato sai ya saka mata har sai ta tsotse yatsansa sannan ya cire ya sake sakawa haka yayi ta mata har ta yi bachi. Sai ya zare yatsan a hankali ya saka tissue ya goge mata bakinta inda ba zai fita ba ya lakata yawunsa ya shafa ya gyara mata bakin sannan ya rufe zumar ya mika hannunsa ya aje ya dauki remote ya kashe wutar dakin, haka suka kwana daga ita har shi ba su farka ba sai da asuba shi yana jingine da gadon ita kuma yana kwance a kirjinsa.

Suna gama sallah ya cire hijab dinta ta aje, ya san yadda take matukar son kamshinsa dan haka ya dauko rigarsa mai maballai ya saka mata, babban riga ce sai ta dan sauko mata cikin kayanta ya duba ya dauko short ya saka mata wanda ya tsaya iya guiwarta ya saka mata hulla sannan ya zaunar da ita saman gadon ya durkusa kasa ya kama hannayenta ya rike.

“Good morning Fam”

Ta yi dariya, shi ma dariyar yayi ya kai bakinsa ya sumbanci katon cikinta sannan ya mike tsaye ya rumgumeta.

“I love you so much Humairah i love you with all my heart”

“I love you too”

“Me kike son ki ci?”

“Something new, kuma ranar nan da ka yi min miya ya kone na ji dadinshi”

“Stew?”

“Yeah ya min dadi ina son ka sake min ya kone”

“Okay akwai shi a fridge ai, zan dora a wuta ya kone”

Ya buge masa hannu jin yana kokarin aika mata da sakon da bata shirya karba a yanzu da safen nan ba.

“To ai ba ki gaishe ni shiyasa”

Sai ta mike tsaye gaba daya, ya saka hannunsa ya kama fuskarta ya hade bakinsu, wani kalar French kiss yake aikata mata in a soft lips, har sai da ta ga yana kokarin fita hayyacinsa sannan ta cire bakinta. Sai ya hade goshinsu numfashinsu ya gauraya yana kallon saman idonta dake rufe hannayensa kuma suka sauka a cikinta.

“I love you”

Ya furta mata murya can kasa. A tare suka shiga kitchen ta hau sama kusada sink ta zauna tana masa hira yana aiki, idan ya biyo ta kusa da ita sai sun sumbanci juna yake kaucewa haka dai har ya gama, sannan ya rikota suka sauko tana tafiya yana bayanta ya saka hannunsa ya tallafo mata cikin.

“Kenan ba yanzu za ayi ba?”

“Har yanzu ai be fito da wadda yake so ba, Maleek yace min tun tasowarsu Mahmood yana da ruwan ido sosai yanzu ma baki ji bakinsa ba duk zai yi magana cewa yake shi ba zai zauna da mace daya ba, shi ba zai dauki halin Abiey ba yayana da yawa yake son haifowa kamar ni”

Bata san lokacin da ta juyo da karfi ta kalleshi ba har sai da yayi mamaki.

“Kamar kai kamar Yaya?”

Ya rufe mata idon data zuba masa.

“Kamar haka”

Ya janye hannun.

“Kai ma aure aure zaka yi?”

“Nooo Yaya nake nufi ina son haihuwa da yawa na tara yara maza da mata”

“Oh na dauka aure da sai na cire maka cikinka na aje”

Be san lokacin da ya fashe da dariya ba.

“Dan Allah cire ki aje, har kyauta sai na miki, see dis Girl ku dai mata baku son kishiya? Allah yace ayi ba kuma kin sani”

“Zaka ba ni abincin na ci ko bata min rai zaka yi?”

Ya sumbanci hancinta da tsakiyar girarta.

“Lemme feed you Babyn baby”

Kujera yaja mata sai da ta fara zaunawa sannan ya zauna ya fara zuba musu abinci yana dariya, domin ya lura da gaske ta dauki zancen da zafi...

One year later......
Chapter 169 · 0% Book details