Sashe 103
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Me yasa kika saka tunanin a ranki Waira? Idan kuma an yafe miki fa?”
Ta yi shiru tana kallon kasa. Maleek ya sauke ajiyar zuciya a sirrance sannan ya ce
“Waira shiga ciki, Jabir muje na sauke ka”
Ta matsa baya tana masa waving sannan ta nufi kofar falon Ummi.
“Allah ya kiyaye Jabir”
Ummi ta fada sannan ta bi bayan Waira. Jabir ya amsa da Ameen sannan ya karaso gurin Maleek yana fadin.
“Please don't be so harsh to her, idan abun da take ikirari ya faru abun da kake mata zai yi ta damunta”
“Ku ne dai kuke ganin kamar ina matsa mata, amman ni na san ina daga mata kafa sosai”
Ya fada sannan ya bude motarsa ya shiga. Sai da
Maleek da Jabir suka bar gidan tare da Juwairiyyya da zata masa sallama sannan ya Dr ta koma ciki tare da Yesmin, Mahmood kuma ya shiga tasa motar ya fice.
Ummi ta raka Waira har dakinta ta dauko mata tawul din da zata daura tana tambayarta.
“Waira ta Ameer ya ci cake din da na hada miki”
“Eh ya ci”
“Da gaske?”
Waira ta daga mata kai tana murmushi kamar yadda Ummi ma take murmushi kamin Waira ta gusar da murmushin sakamakon amsar da ta bata.
“Amman da na ce ke kika yi sai ya zubar”
“Wata kila zai dauke ni lokaci kamin Ameer ya fuskanci abun da nake nufi ya yafe min, zan jira har lokacin da zai fahimci gaskiya, har zuwa lokacin da zuciyarsa zata bude ya fahimce ni, sai ban sani ba ko rayuwa zata ba ni aron lokaci”
Waira ta karbi tawul din ta daura.
“Ummi school bag dina da ragowar cake din yana can a motarsa mu kira shi mu ce ya kawo”
Ummi ta girgiza mata kai.
“Zamu bari sai gobe da safe sai mu kira, kin ga yanzu ransa a bace yake”
“Okay Ummi”
Ummi ta shafa fuskarta.
“Allah ya miki albarka”
“Ameen”
AMEER POV.
Binsu yayi da kallo sai da suka wuce sannan ya shiga motarsa ya mika hannu ya rufe motar, zuciyarsa na mugun tafasa, a yanzu ya fahimci abun da take fada cewar Maleek baya sonta, daman can ya san halin Maleek baya son mata ko yan'uwansa ne balle ita da ta fado daga sama. Ba ma abun da ya bata masa rai kamar gadarar da Maleek din yake nuna masa.
“Zan gyawa yaron nan zama, sai na bashi mamaki”
Ya juya ya kalli jakarta da cake dinta dake cikin motar, sai ya daki sitiyarin motar da karfi, yana jin haushin yadda take tsoron Maleek.
“Ni na jefaki a wannan halin, zan rabaki da gidan nan soon”
Ya fada daidai lokacin da ya faka motarsa a harabar asibitin Hikima domin hankalinsa ba zai kwanta ba idan be je ya duba tsohuwar da ya kade ba. Ajiyar zuciya ya sauke ya mika hannunsa ya dauko jakar makarantar ya bude ya ciro littafanta yana dubawa, da textbook ya fara kamin ya duba notebook, ba laifi tana rubutu yadda xa a fahimta even though bata gwane sosai ba rubutun yan primary 4 take yi. Yana dubawa maganar da suka yi a dazun tana dawo masa, tausayinta ya cika masa zuciya. And she's right shi be rasa gata ba, kuma matar da take ikirarin ita mahaifiyarsa ce tana dakun zuwan ranar da zai karbi hakan, and he would ko dan abun da ta fada masa cewar Ummi tana dauke da cutar Leukemia, ba sosai ya san komai akan cutar ba, amman ya san cuta ce mai hatsari dake farautar rayuwar ďan adam. Ya aje mika hannuna ya dauko box din cake din da ta bari ya dauka ya bude, kallon shape din cake din yake yana, kamin ya fi karfin zuciyarsa ya kai hannu ya dauki spoon din dake gefe ya gutsiri cake din ya ci.
“Da hannu yafi dadi mu bama ci da spoon”
Maganar Waira ta fado, masa sai ya aje spoon din a muhallinsa ya zari tissue ya saka ya dauki cake din yana ci. Sai da ya ci kusan rabi sannan ya rufe mata saura ya saka mata a jakarta ya aje jakar gefe ya kwanta jikin kujerar yana sauke ajiyar zuciya, duk wata magana da Waira ta yi masa sai da ta dawo masa a lokacin, ta fada masa kusan abun da mahaifinsa Mr Bashir ya fada masa amman be fahimta ba sai a yanzu. Bude motar yayi ya fito nufi cikin asibitin, ya isa Emergency ya nufi dakin da aka ya barta sai ya tarar wasu ne ba ita ba. Nurses din dake gurin ya tambaya ta fada masa cewar an canja mata daki. Wani ta saka yayi masa jagora har dakin da aka maidata, Mutumen na nuna masa dakin ya juya yayi tafiyarsa. Ameer ya kalli room number din dakin sannan ya murda kofar ya shiga, first abun da ya fara arba da shi is Humairah tana tsaye gurin kan tsohuwar idonta yayi ja har ya kumbura, kana ganinta kasan ba kadan ta yi kuka ba. Tsayawa yayi yana kallonta da mamaki ita ma kallon mamaki take masa, Mamarta kuma ta mike tsaye tana kallonsa domin ta gane shi ne mai gidan yarta Humairah ta rike fuskarsa tun a ganin farko da ta yi masa, shi kam ba dan ganin Humairah ba da ba zai iya shaidar fuskokinsu ba daga ita uwar har kakar.
“Me kik.... Kakarki ce?”
Ta daga masa kai.
“Kai ka kadeta?”
“It wasn't intentionally, zan wuce ne ita kuma zata je karbo sadaka”
Ya karasa gurin gadon.
“Ya jikinta?”
“Da sauki amman har yanzu bata dawo hayyacinta ba”
“Ba zata dawo hayyacinta da wuri ba, tana bukatar lokaci”
“Ina wuni ranka ya dade”
Mahaifiyarta ta gaishe shi kamar zata risina.
“Lafiya kalau”
Ya amsa yana jin wani iri. Sannan ya kalli Humairah ya ce.
“Za'ayi muku komai a nan, zan tafi gida yanzu anjima kadan za a kawo muku abinci tare da kudi ku siye wani abun, kuma idan akwai abun da kuke bukata ki sanar da ni”
“Okay”
Da ok kawai ta amsa mahaifiyarta ta dora da godiya da addu'a, shi kuma ya juya ya fice bayan yayi ma tsohuwar fatar samun sauki. A lokacin da yake kokarin bude motarsa ya shiga ya ji muryar Humairah bayansa.
“How are you Ameer?”
Ya juyo ya kalleta.
“I'm fine”
“Ban ga haka a fuskarka ba”
“I will be fine”
Ta rumgume hannayenta.
“Ka yi magana da ita?”
“No maybe tonight idan zan kai jakar Waira”
“Who's Waira?”
Ya daga kansa yana kallon harabar gurin.
“Wata yarinya ce mai kyau fuska da kyakkyawar zuciya, ta iya kyautata lafazi, gata da jan hankali, abar tausayi ce kuma abar so, abar kulawa full-option ta hada komai, and someone has never been in her heart”
“I'm sorry Ameer. It since like ka yi saurin warkewa daga abun da ka yi ma Nimra. With due respect Ameer baka canja ba”
Ya matso kusa da ita.
“I canja Humairah kuma zan canja, shiyasa nake son na kyautatawa mata i won't break her heart, ba zan bari wani ya cutar da ita ba, she's the kind of girl I'm looking for, not just her zan kyautatawa kowa gwargwadon ikona, domin na fahimci ni ma alfarma nake ci”
Ta sauke ajiyar zuciya tana jin wani abu marar dadi ya tsaya mata a makoshi.
“Who's knows who my family is? Wace kalar rayuwa suke? Su waye su? Mutanen kirki ne ko na banza wace kalar rayuwa mahaifina yayi ban zani ba, kamar yadda Waira ma bata san waye mahaifinta ba, banbancinta da ni, ni ina da Daddy da Ummi a yanzu, ita kuma bata da kowa”
“if you want to change you should start from within.... Ina fata kuma ina kyautata zaton mahaifinka mutumen kirki ne wish you all the best”
Ta karasa tana murmushin karfin hali.
“Thank you”
Ya amsa sannan ya saka key din ya bude motar ya shiga. Tana tsaye a gurin har ya bar asibitin. A hanya ya tsaya yayi sallah sannan ya kama hanyar gida. Yana isa ya cire jakar Waira ya saka a wata motar ya mikawa mai kula da motocin gidan key motar da ya dawo da ita.
“Ka wanke ta da kyau akwai jini a ciki, na kade wata mata ne muka kaita asibiti”
Jiki na rawa mutumen ya saka hannu biyu ya karba, yana mamakin yadda Ameer yake masa bayanin abun da ya faru, abun da be saba ba, ko da mutum zai bude ya gani a motar ba zai fada masa ga abun da ya aikata ba, shi a gidan babu mai jindadinsa dukansu suna zaune ne kawai saboda Mr Bashir yana kyautata musu kuma yana musu albashi mai tsoka. Ya shiga cikin falon cikin wani yanayi mai wuyar fassara, Mummy dake tsaye rike da remote ta kalleshi.
“Ameer ka dawo”
Ya kalleta, a lokacin da yake ďan iskan gari bata isa ta yi magana ya amsa mata ba sai ya ga dama, har ganin yake kamar sa'ido take masa tana masa munafurci a gurin Daddy, amman yanzu wannan duk ta kau.
“Eh”
Ya wuce sai kuma ya juya.
“Na kade wata mata by mistake amman na kaita asibiti, please ina son ki saka masu aikin gidan nan su zuba mata abinci, zan yi ma musa text din inda take da kudin da za a bata sai yaje ya kai musu”
“Subhanallahi amman dai baka ji ciwo ba ko?”
Ya amsa mata da kai.
“Matar da sauki?”
“Da sauki ina tunanin karaya ce”
“Allah ya sauwake, ya tsare gaba please Ameer ya kamata ka rika kula idan kana tuki, kuma ka rika sassautawa zuciyarka”
Sai da yayi kamar ya tsaya yi mata bayanin ba da gangan ya kade ya ba, it's not his fault sai kuma ya juya kawai ya nufi stairs.
Ta yi shiru tana kallon kasa. Maleek ya sauke ajiyar zuciya a sirrance sannan ya ce
“Waira shiga ciki, Jabir muje na sauke ka”
Ta matsa baya tana masa waving sannan ta nufi kofar falon Ummi.
“Allah ya kiyaye Jabir”
Ummi ta fada sannan ta bi bayan Waira. Jabir ya amsa da Ameen sannan ya karaso gurin Maleek yana fadin.
“Please don't be so harsh to her, idan abun da take ikirari ya faru abun da kake mata zai yi ta damunta”
“Ku ne dai kuke ganin kamar ina matsa mata, amman ni na san ina daga mata kafa sosai”
Ya fada sannan ya bude motarsa ya shiga. Sai da
Maleek da Jabir suka bar gidan tare da Juwairiyyya da zata masa sallama sannan ya Dr ta koma ciki tare da Yesmin, Mahmood kuma ya shiga tasa motar ya fice.
Ummi ta raka Waira har dakinta ta dauko mata tawul din da zata daura tana tambayarta.
“Waira ta Ameer ya ci cake din da na hada miki”
“Eh ya ci”
“Da gaske?”
Waira ta daga mata kai tana murmushi kamar yadda Ummi ma take murmushi kamin Waira ta gusar da murmushin sakamakon amsar da ta bata.
“Amman da na ce ke kika yi sai ya zubar”
“Wata kila zai dauke ni lokaci kamin Ameer ya fuskanci abun da nake nufi ya yafe min, zan jira har lokacin da zai fahimci gaskiya, har zuwa lokacin da zuciyarsa zata bude ya fahimce ni, sai ban sani ba ko rayuwa zata ba ni aron lokaci”
Waira ta karbi tawul din ta daura.
“Ummi school bag dina da ragowar cake din yana can a motarsa mu kira shi mu ce ya kawo”
Ummi ta girgiza mata kai.
“Zamu bari sai gobe da safe sai mu kira, kin ga yanzu ransa a bace yake”
“Okay Ummi”
Ummi ta shafa fuskarta.
“Allah ya miki albarka”
“Ameen”
AMEER POV.
Binsu yayi da kallo sai da suka wuce sannan ya shiga motarsa ya mika hannu ya rufe motar, zuciyarsa na mugun tafasa, a yanzu ya fahimci abun da take fada cewar Maleek baya sonta, daman can ya san halin Maleek baya son mata ko yan'uwansa ne balle ita da ta fado daga sama. Ba ma abun da ya bata masa rai kamar gadarar da Maleek din yake nuna masa.
“Zan gyawa yaron nan zama, sai na bashi mamaki”
Ya juya ya kalli jakarta da cake dinta dake cikin motar, sai ya daki sitiyarin motar da karfi, yana jin haushin yadda take tsoron Maleek.
“Ni na jefaki a wannan halin, zan rabaki da gidan nan soon”
Ya fada daidai lokacin da ya faka motarsa a harabar asibitin Hikima domin hankalinsa ba zai kwanta ba idan be je ya duba tsohuwar da ya kade ba. Ajiyar zuciya ya sauke ya mika hannunsa ya dauko jakar makarantar ya bude ya ciro littafanta yana dubawa, da textbook ya fara kamin ya duba notebook, ba laifi tana rubutu yadda xa a fahimta even though bata gwane sosai ba rubutun yan primary 4 take yi. Yana dubawa maganar da suka yi a dazun tana dawo masa, tausayinta ya cika masa zuciya. And she's right shi be rasa gata ba, kuma matar da take ikirarin ita mahaifiyarsa ce tana dakun zuwan ranar da zai karbi hakan, and he would ko dan abun da ta fada masa cewar Ummi tana dauke da cutar Leukemia, ba sosai ya san komai akan cutar ba, amman ya san cuta ce mai hatsari dake farautar rayuwar ďan adam. Ya aje mika hannuna ya dauko box din cake din da ta bari ya dauka ya bude, kallon shape din cake din yake yana, kamin ya fi karfin zuciyarsa ya kai hannu ya dauki spoon din dake gefe ya gutsiri cake din ya ci.
“Da hannu yafi dadi mu bama ci da spoon”
Maganar Waira ta fado, masa sai ya aje spoon din a muhallinsa ya zari tissue ya saka ya dauki cake din yana ci. Sai da ya ci kusan rabi sannan ya rufe mata saura ya saka mata a jakarta ya aje jakar gefe ya kwanta jikin kujerar yana sauke ajiyar zuciya, duk wata magana da Waira ta yi masa sai da ta dawo masa a lokacin, ta fada masa kusan abun da mahaifinsa Mr Bashir ya fada masa amman be fahimta ba sai a yanzu. Bude motar yayi ya fito nufi cikin asibitin, ya isa Emergency ya nufi dakin da aka ya barta sai ya tarar wasu ne ba ita ba. Nurses din dake gurin ya tambaya ta fada masa cewar an canja mata daki. Wani ta saka yayi masa jagora har dakin da aka maidata, Mutumen na nuna masa dakin ya juya yayi tafiyarsa. Ameer ya kalli room number din dakin sannan ya murda kofar ya shiga, first abun da ya fara arba da shi is Humairah tana tsaye gurin kan tsohuwar idonta yayi ja har ya kumbura, kana ganinta kasan ba kadan ta yi kuka ba. Tsayawa yayi yana kallonta da mamaki ita ma kallon mamaki take masa, Mamarta kuma ta mike tsaye tana kallonsa domin ta gane shi ne mai gidan yarta Humairah ta rike fuskarsa tun a ganin farko da ta yi masa, shi kam ba dan ganin Humairah ba da ba zai iya shaidar fuskokinsu ba daga ita uwar har kakar.
“Me kik.... Kakarki ce?”
Ta daga masa kai.
“Kai ka kadeta?”
“It wasn't intentionally, zan wuce ne ita kuma zata je karbo sadaka”
Ya karasa gurin gadon.
“Ya jikinta?”
“Da sauki amman har yanzu bata dawo hayyacinta ba”
“Ba zata dawo hayyacinta da wuri ba, tana bukatar lokaci”
“Ina wuni ranka ya dade”
Mahaifiyarta ta gaishe shi kamar zata risina.
“Lafiya kalau”
Ya amsa yana jin wani iri. Sannan ya kalli Humairah ya ce.
“Za'ayi muku komai a nan, zan tafi gida yanzu anjima kadan za a kawo muku abinci tare da kudi ku siye wani abun, kuma idan akwai abun da kuke bukata ki sanar da ni”
“Okay”
Da ok kawai ta amsa mahaifiyarta ta dora da godiya da addu'a, shi kuma ya juya ya fice bayan yayi ma tsohuwar fatar samun sauki. A lokacin da yake kokarin bude motarsa ya shiga ya ji muryar Humairah bayansa.
“How are you Ameer?”
Ya juyo ya kalleta.
“I'm fine”
“Ban ga haka a fuskarka ba”
“I will be fine”
Ta rumgume hannayenta.
“Ka yi magana da ita?”
“No maybe tonight idan zan kai jakar Waira”
“Who's Waira?”
Ya daga kansa yana kallon harabar gurin.
“Wata yarinya ce mai kyau fuska da kyakkyawar zuciya, ta iya kyautata lafazi, gata da jan hankali, abar tausayi ce kuma abar so, abar kulawa full-option ta hada komai, and someone has never been in her heart”
“I'm sorry Ameer. It since like ka yi saurin warkewa daga abun da ka yi ma Nimra. With due respect Ameer baka canja ba”
Ya matso kusa da ita.
“I canja Humairah kuma zan canja, shiyasa nake son na kyautatawa mata i won't break her heart, ba zan bari wani ya cutar da ita ba, she's the kind of girl I'm looking for, not just her zan kyautatawa kowa gwargwadon ikona, domin na fahimci ni ma alfarma nake ci”
Ta sauke ajiyar zuciya tana jin wani abu marar dadi ya tsaya mata a makoshi.
“Who's knows who my family is? Wace kalar rayuwa suke? Su waye su? Mutanen kirki ne ko na banza wace kalar rayuwa mahaifina yayi ban zani ba, kamar yadda Waira ma bata san waye mahaifinta ba, banbancinta da ni, ni ina da Daddy da Ummi a yanzu, ita kuma bata da kowa”
“if you want to change you should start from within.... Ina fata kuma ina kyautata zaton mahaifinka mutumen kirki ne wish you all the best”
Ta karasa tana murmushin karfin hali.
“Thank you”
Ya amsa sannan ya saka key din ya bude motar ya shiga. Tana tsaye a gurin har ya bar asibitin. A hanya ya tsaya yayi sallah sannan ya kama hanyar gida. Yana isa ya cire jakar Waira ya saka a wata motar ya mikawa mai kula da motocin gidan key motar da ya dawo da ita.
“Ka wanke ta da kyau akwai jini a ciki, na kade wata mata ne muka kaita asibiti”
Jiki na rawa mutumen ya saka hannu biyu ya karba, yana mamakin yadda Ameer yake masa bayanin abun da ya faru, abun da be saba ba, ko da mutum zai bude ya gani a motar ba zai fada masa ga abun da ya aikata ba, shi a gidan babu mai jindadinsa dukansu suna zaune ne kawai saboda Mr Bashir yana kyautata musu kuma yana musu albashi mai tsoka. Ya shiga cikin falon cikin wani yanayi mai wuyar fassara, Mummy dake tsaye rike da remote ta kalleshi.
“Ameer ka dawo”
Ya kalleta, a lokacin da yake ďan iskan gari bata isa ta yi magana ya amsa mata ba sai ya ga dama, har ganin yake kamar sa'ido take masa tana masa munafurci a gurin Daddy, amman yanzu wannan duk ta kau.
“Eh”
Ya wuce sai kuma ya juya.
“Na kade wata mata by mistake amman na kaita asibiti, please ina son ki saka masu aikin gidan nan su zuba mata abinci, zan yi ma musa text din inda take da kudin da za a bata sai yaje ya kai musu”
“Subhanallahi amman dai baka ji ciwo ba ko?”
Ya amsa mata da kai.
“Matar da sauki?”
“Da sauki ina tunanin karaya ce”
“Allah ya sauwake, ya tsare gaba please Ameer ya kamata ka rika kula idan kana tuki, kuma ka rika sassautawa zuciyarka”
Sai da yayi kamar ya tsaya yi mata bayanin ba da gangan ya kade ya ba, it's not his fault sai kuma ya juya kawai ya nufi stairs.