Sashe 24
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har wani daga gira daya yake, ko kadan baya jin komai a jikinsa sai ketar da yake ta sakawa, jefar da rigar hannunsa yayi ya bude motar ya shiga be saka kafafuwansa ba sai da ya cire talkamin kafarsa ya shiga motar haka, daga shi sai wando jean jikinsa ba riga sai farar fatar jikinsa da kuma mazanta dake kara fitar da zatin fuskarsa. Kunna motar yayi at first sai ta tashi sai da ya yunkura zai yi reverse sai ta tsaya, ya sake kunna ta mutu ya sake kunna ta sake mutuwa har sau hudu, jimmm yayi yana tunanin yadda rayuwa zata kasance masa idan motar nan bata tashi ba, ba zai yi mamaki ba idan ta ki tashi domin ya ci uban motar, yadda ya rika buga motar da icen dake gurin sai da gabanta ya lankwashe, abun da be saba ba sai gashi yana addu'a da fatan Allah yasa ta tashi. And he got lucky motar ta tashi abun yayi hamdala ga Allah sai gashi yana fito ya juya kanta da karfi ya koma hanyar da shigo da motar yana gudu sosai kamar an biyo shi. Babu inda ya nufa sai hanyar da zata sada shi da Abuja, tunanin yadda zai yi idan police ko sojoji suka tare shi a hanya be zo masa ba sai yanzu.
EID POV.
Yana tsaye bakin kofar dakin da Waira take yana kallon cikin dakinta dake hargitse, he felt very bad domin shi ne silar guduwarta a garin, guduwar da bashi da tabbacin Sarki zai yafe mata ko kuma ya kasheta kamar yadda ya alkawaranta.
“Waira duk saboda kar ki yi kewa babu ranar da bana kasancewa tare da ke, miyasa zaki tsorata har haka? Akan me zaki karya dokar dake nufin rayuwarki?”
Ya kai hannu ya taba kofar dakin, kamin ya sulale kasa ya zauna a hankali, tun da ta tafi kullum a gurin yake zama, idan baya dakinta to yana a gurin da ta saba zama ta ci yayan itatuwa, ko kadan baya son yayi tsafi ya ga halin da take ciki domin zuciya zata iya debarsa ya bi bayanta bayan kuma Sarki ya kafa masa doka tun a ranar da ta gudu cewar kar ya bi bayanta. Ya daurewa zuciyarsa ya bi Umarni Sarki na iya yanzu da zuciyarsa zata iya dauka, kamin ya shawo kan Sarki ya sassauta hukuncin da zartarwa Waira tun gabanin ya san zata gudu. Wani irin azaba ya ji hannunsa na yi kamar an jefa shi a ruwan zafi, an cire na kara a wuta, da sauri ya saka dayan hannunsa ya rike dayan da yayi masa mugun nauyi dafin na shiga har wuce iya inda zugin yake. Iyakar juriya yayi amman sai da ya kai kwance yana dafe da hannu tsabar azabar da ya ji hannun na masa, yanayin yadda gurin ke masa zafi dafin na masa yawo ya gane cewar maciji ne ya cizi Waira, mikewa yayi tsaye rike da hannu ya daga kansa sama ya lumtse ido. Sai ga wahala masu zafi sun sauko masa, ba Hawaye ne na kukan zafin da yake ji ba na cizon maciji ba, hawayen tausayin Waira yake a wane hali take ciki? Ta ina maciji ya cijeta? Daman tun da ta gudu babu ranar da ba ya tunanin halin da take ciki da kuma abun da zata ci, ko a ina ta boya, duk be sani ba kuma bashi bukatar ya sani a yanzu.
“Waira”
Ya fada yana jin azabar tana karuwa, har yawun bakinsa sun soma canjawa, gumin azaba da wahala na karyo masa a goshi har ya rasa inda zai saka kanshi. Lokaci daya kuma sai ya ji azabar ta dauke masa.
©️KhadeejaCandy
©️®️Copyright
2023
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*
_©Khadeeja Candy_
1️⃣3️⃣
Wani sabon tunanin ne ya zo masa hakan ya saka shi canja shawara, gefen hanya ya rika bi har ya samu wani Karamin shagon siyar da kaya, wani almajiri ya samu ya aika shi kiran mai shagon kasancewar akwai glass sai an bude za a shiga, ba shigar ce matsala ba rashin talkami da kuma rigar jikinsa ce matsala domin baya son ayi masa kallon mahaukaci. Almajirin na isa sai gaai shagon ya fito ya biyo bayansa. Tun kan ya isa Ameer ke masa kallon kasa da sama.
“Riga nake so wacce ta fi ko wace tsada, sai talkami idan kuna da su”
Shi ne abun da ya fada ya mika masa Atm din hannunsa tare da fada masa code.
“Akwai amman ba mu da machine din cire kudin, sai dai makocina shi kuma sai ya cire carjin dinshi”
“Ba matsala”
Ya fada ba tare da ya kalleshi ba, domin mutane kazanta suke ba shi a yanzu, Waira ma dake bayan motar jin yake kamar tana saman jikinta ne, kazantar dake jikinta ta lake masa a zuciya ya kasa manta abun da ya gani. Yana ji yana gani ya bata minti talatin a gurin kamin mutumen dake shakar Ameer ya kawo masa rigar da talkamin, domin jikinsa na bashi ba Ameer ba mutumen kwarai ba ne ganin sabuwar mota da aka buge gabanta gashi babu riga a jikinsa kuma babu talkami hakan na nuna sato motar yayi ko kuma wani abun dabam. Kallo daya Ameer yayi ma rigar da talkamin ya san ba ajinsa ba ne, sai dai babu yadda zai yi dole ya saka a haka, sai da yayi tsaki sannan ya karba tare da ATM din, a gaban mutumen ya saka rigar sannan ya ja motar yayi gaba, tafiya mai nisa yayi sannan ya saka talkamin ya faka motar gafen titi ya fita zuwa gurin wani mai shagon POS ya mika masa ATM din.
“300k nake so”
“Ranka ya dade ba za su samu ba, sai zuwa anjima sai dai 100+ idan kana so”
“Ba ni”
Mutumen ya fara aikin saka ATM din, dayan dake taya shi aiki kuma ya fara karga kudin, fuska babu annuri Ameer ke fada musu pin din, in less than 20min aka ciro kudin aka bashi ya karba, be damu da saka su aljihu ba ya riko su a hannu domin sun masa kazanta kasancewarsu tsofin kudi wasu ma sun yage sa'arsa daya sun saka masa su a leda. Bude motar yayi ya shiga ya dauki hanyar Kano sai da ya kusa isa gurin da police ke bada Hannu sai ya samu guri gefen titi ya faka motar inda ba za su hango shi ba, ya fita ya zagaya bayan motar da ya bude ya saka hannunsa ya warware nadin da yayi mata da carpet fuskarta ta fito, hakan nan ya samu kansa da tsaya yana kallon yadda hawaye suka bushe a fuskarta ga gashin kanta ya kara yamutsewa, abun ka da marar juriya sai amai ya sake cika masa baki da sauri yaja baya ya fara kwara amam dake fitowa daker domin babu komai a cikinsa sai yunwa, ya amayar da dan abun da ya ci jiya, gashi yau be saka komai a cikinsa ba. Cikin motar ya koma ya dauko gorar ruwa ya wanke bakinsa da fuskarsa, after that ya tuna ya taba abubuwa da yawa da be kamata hannunsa ya kai a fuskarsa ba tare da ya wanke ba.
“Ohhhhhh”
Ya furta yana jin wani irin bakin ciki, a sake ya bar motar kamar yadda ya bar bayan motar ma a bude, ya dauki kudin dake ledar ya bar ATM din da komai a ciki, ya fito daga gurin zuwa gurin babban titi tafiya yayi mai nisa a kafa sannan ya tsallaka dayan side din da zai maida shi cikin KT yana tafiya yana taron mota har ya samu wanda bata da mutane da yawa ta tsaya, one after the other ya rika bin mutun biyu da suke bayan motar da kallo kamin ya kalli direba da yake ganin idan ya shiga motar kamin su isa KT ma mutuwa zai yi, domin irin motar nan ce da bata da Ac glass din motar ma a harfice yake balle kuma mutanen ciki.
“Ku tafi kawai”
Bayan ya gama bata musu lokaci, be tsaya jin abin da za su fada ba yayi gaba abunsa, can kuma ya sake taron wata motar, yayi haka ya kai sau biyar sannan ya samu wanda mutun biyu ne kawai a gaban motar bayan babu kowa, sai dai ita ma bata da Ac kuma motar kasuwace irin mai rawa din nan idan ana tukawa, hakan na dai ya daure ya shiga yana jin wani zazzabin wahala na taso masa, tasha ya fada masa za su kai shi he can pay ko bawa suke so shi dai bukatarsa ya ganshi a tasha.
Kamar yadda ya bukata haka suka kai shi har cikin tashar KT suka ce zai ba su 3k saboda lura da suka yi da alamar yana da su, ba musu ya bude ledar ya cire kudin da za su fi haka ya mika musu, sannan ya saka ragowar kudin aljihun wandonsa guda biyu ya bude motar ya fita.
‘What if wanda ya san shi ya ganshi a nan? Wannan ai zai zame masa abun kaskanci’
Shi ne abun da ya fara zuwa masa a rai, hakan ya saka shi nufar wani mai tereda dake siyar da facing cap ya siya ya saka ya siya bakin glass ya saka ya rufe idonsa. Sannan ya nufi gurin da yan union suke da su ya fara magana ya fada musu shatar mota mai kyau zuwa Kano, ya fadi inda za'a kai shi bayan yayi musu karyar motarsa ta lalace kuma tafiyar gaggawa ta kama shi, tun da yake a rayuwarsa be taba sanin haka tasha take a yamutse da mutane ga hayaniyar da yake ganin da ace shi da tuni ya kurmance, duk wani information na shi sai da suka karba sannan suka hada shi da direban da zai kaishi Kano, ba laifi ya samu mota mai dan kyau domin tsab take matsalar kawai bata da Ac, ba su bar gurin ba sai da ya siye lemu cake tare da ruwa da dan biscuits sannan suka kama hanya, direban ya tsaya ya sha mai a gidan mai dake hanyar fita KT sannan suka kama hanya. Kamin su isa Kano Ameer yayi amai ya kai sau hudu saboda warin man motar da yake ciki yana damunsa.
EID POV.
Yana tsaye bakin kofar dakin da Waira take yana kallon cikin dakinta dake hargitse, he felt very bad domin shi ne silar guduwarta a garin, guduwar da bashi da tabbacin Sarki zai yafe mata ko kuma ya kasheta kamar yadda ya alkawaranta.
“Waira duk saboda kar ki yi kewa babu ranar da bana kasancewa tare da ke, miyasa zaki tsorata har haka? Akan me zaki karya dokar dake nufin rayuwarki?”
Ya kai hannu ya taba kofar dakin, kamin ya sulale kasa ya zauna a hankali, tun da ta tafi kullum a gurin yake zama, idan baya dakinta to yana a gurin da ta saba zama ta ci yayan itatuwa, ko kadan baya son yayi tsafi ya ga halin da take ciki domin zuciya zata iya debarsa ya bi bayanta bayan kuma Sarki ya kafa masa doka tun a ranar da ta gudu cewar kar ya bi bayanta. Ya daurewa zuciyarsa ya bi Umarni Sarki na iya yanzu da zuciyarsa zata iya dauka, kamin ya shawo kan Sarki ya sassauta hukuncin da zartarwa Waira tun gabanin ya san zata gudu. Wani irin azaba ya ji hannunsa na yi kamar an jefa shi a ruwan zafi, an cire na kara a wuta, da sauri ya saka dayan hannunsa ya rike dayan da yayi masa mugun nauyi dafin na shiga har wuce iya inda zugin yake. Iyakar juriya yayi amman sai da ya kai kwance yana dafe da hannu tsabar azabar da ya ji hannun na masa, yanayin yadda gurin ke masa zafi dafin na masa yawo ya gane cewar maciji ne ya cizi Waira, mikewa yayi tsaye rike da hannu ya daga kansa sama ya lumtse ido. Sai ga wahala masu zafi sun sauko masa, ba Hawaye ne na kukan zafin da yake ji ba na cizon maciji ba, hawayen tausayin Waira yake a wane hali take ciki? Ta ina maciji ya cijeta? Daman tun da ta gudu babu ranar da ba ya tunanin halin da take ciki da kuma abun da zata ci, ko a ina ta boya, duk be sani ba kuma bashi bukatar ya sani a yanzu.
“Waira”
Ya fada yana jin azabar tana karuwa, har yawun bakinsa sun soma canjawa, gumin azaba da wahala na karyo masa a goshi har ya rasa inda zai saka kanshi. Lokaci daya kuma sai ya ji azabar ta dauke masa.
©️KhadeejaCandy
©️®️Copyright
2023
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*
_©Khadeeja Candy_
1️⃣3️⃣
Wani sabon tunanin ne ya zo masa hakan ya saka shi canja shawara, gefen hanya ya rika bi har ya samu wani Karamin shagon siyar da kaya, wani almajiri ya samu ya aika shi kiran mai shagon kasancewar akwai glass sai an bude za a shiga, ba shigar ce matsala ba rashin talkami da kuma rigar jikinsa ce matsala domin baya son ayi masa kallon mahaukaci. Almajirin na isa sai gaai shagon ya fito ya biyo bayansa. Tun kan ya isa Ameer ke masa kallon kasa da sama.
“Riga nake so wacce ta fi ko wace tsada, sai talkami idan kuna da su”
Shi ne abun da ya fada ya mika masa Atm din hannunsa tare da fada masa code.
“Akwai amman ba mu da machine din cire kudin, sai dai makocina shi kuma sai ya cire carjin dinshi”
“Ba matsala”
Ya fada ba tare da ya kalleshi ba, domin mutane kazanta suke ba shi a yanzu, Waira ma dake bayan motar jin yake kamar tana saman jikinta ne, kazantar dake jikinta ta lake masa a zuciya ya kasa manta abun da ya gani. Yana ji yana gani ya bata minti talatin a gurin kamin mutumen dake shakar Ameer ya kawo masa rigar da talkamin, domin jikinsa na bashi ba Ameer ba mutumen kwarai ba ne ganin sabuwar mota da aka buge gabanta gashi babu riga a jikinsa kuma babu talkami hakan na nuna sato motar yayi ko kuma wani abun dabam. Kallo daya Ameer yayi ma rigar da talkamin ya san ba ajinsa ba ne, sai dai babu yadda zai yi dole ya saka a haka, sai da yayi tsaki sannan ya karba tare da ATM din, a gaban mutumen ya saka rigar sannan ya ja motar yayi gaba, tafiya mai nisa yayi sannan ya saka talkamin ya faka motar gafen titi ya fita zuwa gurin wani mai shagon POS ya mika masa ATM din.
“300k nake so”
“Ranka ya dade ba za su samu ba, sai zuwa anjima sai dai 100+ idan kana so”
“Ba ni”
Mutumen ya fara aikin saka ATM din, dayan dake taya shi aiki kuma ya fara karga kudin, fuska babu annuri Ameer ke fada musu pin din, in less than 20min aka ciro kudin aka bashi ya karba, be damu da saka su aljihu ba ya riko su a hannu domin sun masa kazanta kasancewarsu tsofin kudi wasu ma sun yage sa'arsa daya sun saka masa su a leda. Bude motar yayi ya shiga ya dauki hanyar Kano sai da ya kusa isa gurin da police ke bada Hannu sai ya samu guri gefen titi ya faka motar inda ba za su hango shi ba, ya fita ya zagaya bayan motar da ya bude ya saka hannunsa ya warware nadin da yayi mata da carpet fuskarta ta fito, hakan nan ya samu kansa da tsaya yana kallon yadda hawaye suka bushe a fuskarta ga gashin kanta ya kara yamutsewa, abun ka da marar juriya sai amai ya sake cika masa baki da sauri yaja baya ya fara kwara amam dake fitowa daker domin babu komai a cikinsa sai yunwa, ya amayar da dan abun da ya ci jiya, gashi yau be saka komai a cikinsa ba. Cikin motar ya koma ya dauko gorar ruwa ya wanke bakinsa da fuskarsa, after that ya tuna ya taba abubuwa da yawa da be kamata hannunsa ya kai a fuskarsa ba tare da ya wanke ba.
“Ohhhhhh”
Ya furta yana jin wani irin bakin ciki, a sake ya bar motar kamar yadda ya bar bayan motar ma a bude, ya dauki kudin dake ledar ya bar ATM din da komai a ciki, ya fito daga gurin zuwa gurin babban titi tafiya yayi mai nisa a kafa sannan ya tsallaka dayan side din da zai maida shi cikin KT yana tafiya yana taron mota har ya samu wanda bata da mutane da yawa ta tsaya, one after the other ya rika bin mutun biyu da suke bayan motar da kallo kamin ya kalli direba da yake ganin idan ya shiga motar kamin su isa KT ma mutuwa zai yi, domin irin motar nan ce da bata da Ac glass din motar ma a harfice yake balle kuma mutanen ciki.
“Ku tafi kawai”
Bayan ya gama bata musu lokaci, be tsaya jin abin da za su fada ba yayi gaba abunsa, can kuma ya sake taron wata motar, yayi haka ya kai sau biyar sannan ya samu wanda mutun biyu ne kawai a gaban motar bayan babu kowa, sai dai ita ma bata da Ac kuma motar kasuwace irin mai rawa din nan idan ana tukawa, hakan na dai ya daure ya shiga yana jin wani zazzabin wahala na taso masa, tasha ya fada masa za su kai shi he can pay ko bawa suke so shi dai bukatarsa ya ganshi a tasha.
Kamar yadda ya bukata haka suka kai shi har cikin tashar KT suka ce zai ba su 3k saboda lura da suka yi da alamar yana da su, ba musu ya bude ledar ya cire kudin da za su fi haka ya mika musu, sannan ya saka ragowar kudin aljihun wandonsa guda biyu ya bude motar ya fita.
‘What if wanda ya san shi ya ganshi a nan? Wannan ai zai zame masa abun kaskanci’
Shi ne abun da ya fara zuwa masa a rai, hakan ya saka shi nufar wani mai tereda dake siyar da facing cap ya siya ya saka ya siya bakin glass ya saka ya rufe idonsa. Sannan ya nufi gurin da yan union suke da su ya fara magana ya fada musu shatar mota mai kyau zuwa Kano, ya fadi inda za'a kai shi bayan yayi musu karyar motarsa ta lalace kuma tafiyar gaggawa ta kama shi, tun da yake a rayuwarsa be taba sanin haka tasha take a yamutse da mutane ga hayaniyar da yake ganin da ace shi da tuni ya kurmance, duk wani information na shi sai da suka karba sannan suka hada shi da direban da zai kaishi Kano, ba laifi ya samu mota mai dan kyau domin tsab take matsalar kawai bata da Ac, ba su bar gurin ba sai da ya siye lemu cake tare da ruwa da dan biscuits sannan suka kama hanya, direban ya tsaya ya sha mai a gidan mai dake hanyar fita KT sannan suka kama hanya. Kamin su isa Kano Ameer yayi amai ya kai sau hudu saboda warin man motar da yake ciki yana damunsa.