Sashe 135
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ameer ya dawo da sauri yana murmushi ya rumgume Daddy.
“I love you Daddy idan ka raye ban san ya rayuwata zata kasance ba”
“Allah ya maka albarka, je ka samu abun da ka ci ka kwanta da wuri saboda ka samu tashi da dare nima zan taya ka, farincikinka shi ne nawa Ameer”
Tun da Ameer yake a duniya be taba jin kaunar Daddy irin na yau ba, domin shi ne ya fahimci damuwarsa kuma ya dauko hanyar magance masa ita. Be samu cin komai ba Before ya kwanta domin tunanin Waira ba ya barin shi jin yunwa haka ma bachi ko kadan kasa yi yayi, shi dai gani yake kamar idan ya runtse zai farka ne ya ga babu kaunar yar kyakkyawar matashiyar budurwa nan a ransa. Kamin lokacin da zai yi tsayuwar daren yayi duk ya kagu, domin ya san Allah ma ji rokon bawansa ne, kuma matukar ya dage kamar yadda Daddy ya fada masa zai samu biya bukata, walau Waira ta kaunace shi fiye da yadda yake sonta, ko kuma Allah ya musayya masa da wanda ta fita alheri a gareshi.
Haka ya saka shi dagewa yayi ta nafila har sai da ya ji ya yi iya yadda zai iya, sannan ya zauna ya bude al'qur'ane yayi ta karatu, daman dai sani da iya karatun Allah akwai shi a tare da shi, sai dai shashanci da bin hanyar shaida ne ya saka a gaba ya saka ya watsar da wadanda kyakkyawa halayyar da Daddy ya dade yana son gani a tare da shi. Kamin ya gabatar da bukatarsa sai da yayi tuba ga Allah ya daukarwa kansa alkawarin ba zai sake komawa a cikin wacan kazantar da ya taba kasancewa ba, ko da kuwa ya rasa Waira, a yanzu ya kai munzalin da zai san daidai da akasin haka. Lokaci yayi da ya kamata ya natsu ya fuskanci rayuwa domin akwai rayuwa akwai mutuwa at least ya kamata ya zama mutumen kirki kamar yadda Daddy da Umminsa da duk wani masoyinsa na gaske yake son gani.
Ya farka da farinciki da nishadin zuciya, ba na wanda ya samu biyan bukata ba, sai irin na wanda ya kusanci Sallah a lokacin da kowa yake bachi, Sallah kuma ta kusantar da shi ga Allah. Kusan wannan a bayyane yake duk wanda yake Sallah dare yana farkawa da farinciki da nishadi ko da bashi ko naira, fa kuma kusanci da yake karawa mutum ga Allah bayan hasken fuska da haiba da Allah ke sakawa bawa a fuskar duk wanda zai kalli mai Sallah dare.
Be tsaya jiran Daddy ko Mommy su fito ba, balle wani breakfast da ba damunsa yayi ba, zuciyarta bata bukatar arba da kowa sai abar kaunarsa Waira, dan haka ya shiga bathroom yayi wanka ya shirya cikin tufafin da suka fi yi masa kyau wato kananan kaya ya sanya turare mai kamshi, daman shi da turare 5&6 ne basa rabuwa da juna. Ya sauko da kuzarinsa ya fita harabar gidan, ko da be da abun fada mata shi dai yana bukatar ganinta, even if zaginshi zata yi ta fada masa magana marar dadi yana son jin duk abun da zai fito bakinta. Har ga Allah ya san yana son Waira irin son na mai fitar da mutun daga hankalinsa, mai saka namiji susucewa ya zama kamar wani soko, ba ita ce mace ta farko da ya fara gani ba, ya je gurare da yawa a duniya, tun yana da kurciyarsa har karatunsa zuwa yanzu da yake zaune a guri daya tare da familynsa amman be ga mace da ta dauke masa hankali ta birkita tunaninsa lokaci daya ba irin Waira. Yana tukin yana tuna duk wani moment na su na farinciki a baya, farkon fara haduwa da ita the way da take nuna farinciki idan suna tare, yadda take dagewa ta nuna ta san shi kuma tana son zama a kusa da shi, yadda yake iya tirsasa ta yi abun da bata so kamar cin abinci da bata saba ci ba, saka mata kaunar addinin musulunci da lurar da ida yadda addinin yake da kyau da gata, duk wannan ta tsaya ta saurareshi kuma ta fahimta ta gamsu, sai soyayyarsa ce kawai ta kasa samun muhallin a zuciyarta. It's because of abun da yayi ma Nimra or saboda abubuwan shaidanci da yayi ta aikatawa abaya ne. Har ya isa gidan aka bude masa gate ya faka motar be samu amsar tambayarsa. A ta inda zai ga windows din Waira ya faka yana hw spend time yana kallon gurin ji yake kanar zata leko tace masa Ameer darling good morning. Ya sauke ajiyar zuciya ya fi a kirga sannan ya bude ya fito daga cikin motar praying for her ya fara arba a idan idan ya shiga falon, sai dai hakan be saka hakonsa ya cin ma ruwa ba, domin ya shiga falon ya tararda Ummi da Maleek Mahmood Namra har ma da Abiey suna karyawa Waira bata tare da su, kamar wanda aka sarewa jiki haka ya shiga falon kallo daya zaka masa ka san ba su yake son gani ba, domin yawo yake da idonsa a inda ya san tana yawan zama ko zai ganta. Har yayi rabin falon sai kuma ya juya zai fita.
“Ameer”
Abiey ya kira shi sai ya juyo ba tare da ya amsa ba.
“Akwai abun da kake so ne?”
Yayi shiru, can kuma ya kalli upstairs.
“Ina son magana da Ummi ne”
“Ga Ummi ka a nan ai, bata upstairs”
Abiey ya nuna Ummi dake kallon Ameer cikin damuwa.
“Private”
Ameer ya fada yana dauke idonsa daga barin kallon stairs ya kalli Ummi.
“Ba privacy a nan gidan duk wanda zai yi magana sai dai yayi a gaban kowa dukanku daya ne ai, babu banbanci, idan har wani yana son kebewa sai dai ya kebe da ni, amman ban yarda ayi min yan ubanci ba a kebe da Ummi”
Kowa kallon Abiey yake da mamaki har shi Ameer da be gama fahimtar Abiey da wasa yake masa magabar ba ko kuma da gaske ne saboda ya ci fuskarsa.
“Go ahead gata nan zaune, zo ka fada mata”
Ameer ya matso yana kallon Abiey zuciyarsa da tunani kala kala.
“Akan Waira ne, ta min magana jiya da dare tace tana son ta musulunta ta hannuna saboda na samu wannan ladar, kuma na yi magana da Daddy ya ce zai yi magana da Imam dinsu, sai ya fada mana yadda za'ayi”
Kamin Ummi ta ce komai Abiey yayi murmushi.
“Maa Shaa Allah abu mai kyau, amman dai Ameer ai kasan ina cikin gidan nan ko? Kuma ina da hakki da Waira, kai da ita ina tunanin duk a karkashin ikona kuke, ya kamata ace ka fada min kamin ka aiwatar da komai, ko kuma an fada maka Daddynka ne ya fini son lada ko kuma ni ka raina capacity na ne?”
Ameer ya gagara cewa komai sai kallon rashin fahimta yake yi ma Abiey.
“Ka fada masa zan aiwatar da komai, ba sai yayi ba, yanzu ma muna tattaunawa ne akan maganar tafiyarta Umminka ta fada min cewar Waira tana son ta tafi, ni kuma na goyi bayan haka saboda na fara process din sanin danginta saboda hakan abu ne mai kyau ko dan sanin macen da za a gina iyali da ita, amman ina ganin ba zan barta ta tafi ita kadai ba, sai na sanar da police an ba mu police biyu ko uku, kuma a samu amincewar hukuma sannan kuma ku tafi tare da ita zai fi”
Maleek ya soke kai kasa gabansa sai bugawa yake da karfi. Ummi kuma tana kallon Abiey da wani irin burgewa ganin yana kokarin aiwatar da abun da bata tsammata ba a gurin Ameer. With confused Ameer ya dan ware hannunsa ya ce.
“Maybe ko zata tafi tare da Maleek saboda ta fi sakewa da shi for now ni ina da abubuwan yi da yawa”
“Amman kai zaka fi sanin hanya ai, kuma kai ka fi cewa ku tafi saboda kai kasan inda ka daukota”
Cewar Abiey yana nuna shi.
“Yeah amman Maleek zai fi”
Abiey ya daga kafadunsa
“Shikenan ba zan takura ka ba, duk yadda ka so haka za'ayi, shiga ka taso ta sai ku yi breakfast din a tare ita ma bata ci abinci ba”
“No... Zan yi... ”
Ameer ya so ya musa, sai dai ganin Abiey ya girgiza masa kai alamar aa ya saka dole ya fasa furta abun da zai fada ya nufi upstairs mamaki fal a zuciyarsa, Namra ma mamaki take, balle kuma Maleek da Mahmood da suke ganin kamar Abiey dinsu aka dauke aka kawo wani. Ummi kam jindadi ya hana ta cewa komai. A hankali ya tura kofar dakin Waira ya shiga tsoron kar tace ya mata ba daidai ba ya saka shi tsayawa bakin kofar dakin yana kallon yadda take shafa baby rabbit dinta da hannunta.
“Waira zan iya shigowa?”
Ta juyo ta kalleshi tare da daga masa kai, sai ya maida kofar a hankali ya rufe ya karasa inda take zaune a kasa, ya zauna ya hade kafafuwansa yana kallonta.
“Good morning”
Ya fada yana yafawa fuskarsa murmushi. Tunanin ita ya kamata ta fara gaishe shi ya hana ta amsawa, sai ma mika masa guiwarta da ta yi.
“Good Morning”
“How are you doing today? Beautiful Angel”
Ta sauke kanta kasa ganin irin kallon da yake mata kirin yake jira ya fada cikin idonta ya narke kamar ruwa.
“Abiey ya ce ki fito muje falo mu karya, kuma na yi magana da Daddy na akan musuluntar da zaki yi, yace zai yi magana da Imam dinsu, but then sai kuma Abiey a yanzu yake min maganar cewar zai yi komai ba sai Daddy ya shigo ba, i don't know ko haka din yayi miki?”
Bata ce komai ba, kanta na kasa har lokacin, shi kam a yanzu dai baya gajiya da kallon duk wani abu da ya shafe ta balle kuma ita din kanta.
“Ko kin fi son ki karya a nan?”
“Bari na wanke baki”
“I love you Daddy idan ka raye ban san ya rayuwata zata kasance ba”
“Allah ya maka albarka, je ka samu abun da ka ci ka kwanta da wuri saboda ka samu tashi da dare nima zan taya ka, farincikinka shi ne nawa Ameer”
Tun da Ameer yake a duniya be taba jin kaunar Daddy irin na yau ba, domin shi ne ya fahimci damuwarsa kuma ya dauko hanyar magance masa ita. Be samu cin komai ba Before ya kwanta domin tunanin Waira ba ya barin shi jin yunwa haka ma bachi ko kadan kasa yi yayi, shi dai gani yake kamar idan ya runtse zai farka ne ya ga babu kaunar yar kyakkyawar matashiyar budurwa nan a ransa. Kamin lokacin da zai yi tsayuwar daren yayi duk ya kagu, domin ya san Allah ma ji rokon bawansa ne, kuma matukar ya dage kamar yadda Daddy ya fada masa zai samu biya bukata, walau Waira ta kaunace shi fiye da yadda yake sonta, ko kuma Allah ya musayya masa da wanda ta fita alheri a gareshi.
Haka ya saka shi dagewa yayi ta nafila har sai da ya ji ya yi iya yadda zai iya, sannan ya zauna ya bude al'qur'ane yayi ta karatu, daman dai sani da iya karatun Allah akwai shi a tare da shi, sai dai shashanci da bin hanyar shaida ne ya saka a gaba ya saka ya watsar da wadanda kyakkyawa halayyar da Daddy ya dade yana son gani a tare da shi. Kamin ya gabatar da bukatarsa sai da yayi tuba ga Allah ya daukarwa kansa alkawarin ba zai sake komawa a cikin wacan kazantar da ya taba kasancewa ba, ko da kuwa ya rasa Waira, a yanzu ya kai munzalin da zai san daidai da akasin haka. Lokaci yayi da ya kamata ya natsu ya fuskanci rayuwa domin akwai rayuwa akwai mutuwa at least ya kamata ya zama mutumen kirki kamar yadda Daddy da Umminsa da duk wani masoyinsa na gaske yake son gani.
Ya farka da farinciki da nishadin zuciya, ba na wanda ya samu biyan bukata ba, sai irin na wanda ya kusanci Sallah a lokacin da kowa yake bachi, Sallah kuma ta kusantar da shi ga Allah. Kusan wannan a bayyane yake duk wanda yake Sallah dare yana farkawa da farinciki da nishadi ko da bashi ko naira, fa kuma kusanci da yake karawa mutum ga Allah bayan hasken fuska da haiba da Allah ke sakawa bawa a fuskar duk wanda zai kalli mai Sallah dare.
Be tsaya jiran Daddy ko Mommy su fito ba, balle wani breakfast da ba damunsa yayi ba, zuciyarta bata bukatar arba da kowa sai abar kaunarsa Waira, dan haka ya shiga bathroom yayi wanka ya shirya cikin tufafin da suka fi yi masa kyau wato kananan kaya ya sanya turare mai kamshi, daman shi da turare 5&6 ne basa rabuwa da juna. Ya sauko da kuzarinsa ya fita harabar gidan, ko da be da abun fada mata shi dai yana bukatar ganinta, even if zaginshi zata yi ta fada masa magana marar dadi yana son jin duk abun da zai fito bakinta. Har ga Allah ya san yana son Waira irin son na mai fitar da mutun daga hankalinsa, mai saka namiji susucewa ya zama kamar wani soko, ba ita ce mace ta farko da ya fara gani ba, ya je gurare da yawa a duniya, tun yana da kurciyarsa har karatunsa zuwa yanzu da yake zaune a guri daya tare da familynsa amman be ga mace da ta dauke masa hankali ta birkita tunaninsa lokaci daya ba irin Waira. Yana tukin yana tuna duk wani moment na su na farinciki a baya, farkon fara haduwa da ita the way da take nuna farinciki idan suna tare, yadda take dagewa ta nuna ta san shi kuma tana son zama a kusa da shi, yadda yake iya tirsasa ta yi abun da bata so kamar cin abinci da bata saba ci ba, saka mata kaunar addinin musulunci da lurar da ida yadda addinin yake da kyau da gata, duk wannan ta tsaya ta saurareshi kuma ta fahimta ta gamsu, sai soyayyarsa ce kawai ta kasa samun muhallin a zuciyarta. It's because of abun da yayi ma Nimra or saboda abubuwan shaidanci da yayi ta aikatawa abaya ne. Har ya isa gidan aka bude masa gate ya faka motar be samu amsar tambayarsa. A ta inda zai ga windows din Waira ya faka yana hw spend time yana kallon gurin ji yake kanar zata leko tace masa Ameer darling good morning. Ya sauke ajiyar zuciya ya fi a kirga sannan ya bude ya fito daga cikin motar praying for her ya fara arba a idan idan ya shiga falon, sai dai hakan be saka hakonsa ya cin ma ruwa ba, domin ya shiga falon ya tararda Ummi da Maleek Mahmood Namra har ma da Abiey suna karyawa Waira bata tare da su, kamar wanda aka sarewa jiki haka ya shiga falon kallo daya zaka masa ka san ba su yake son gani ba, domin yawo yake da idonsa a inda ya san tana yawan zama ko zai ganta. Har yayi rabin falon sai kuma ya juya zai fita.
“Ameer”
Abiey ya kira shi sai ya juyo ba tare da ya amsa ba.
“Akwai abun da kake so ne?”
Yayi shiru, can kuma ya kalli upstairs.
“Ina son magana da Ummi ne”
“Ga Ummi ka a nan ai, bata upstairs”
Abiey ya nuna Ummi dake kallon Ameer cikin damuwa.
“Private”
Ameer ya fada yana dauke idonsa daga barin kallon stairs ya kalli Ummi.
“Ba privacy a nan gidan duk wanda zai yi magana sai dai yayi a gaban kowa dukanku daya ne ai, babu banbanci, idan har wani yana son kebewa sai dai ya kebe da ni, amman ban yarda ayi min yan ubanci ba a kebe da Ummi”
Kowa kallon Abiey yake da mamaki har shi Ameer da be gama fahimtar Abiey da wasa yake masa magabar ba ko kuma da gaske ne saboda ya ci fuskarsa.
“Go ahead gata nan zaune, zo ka fada mata”
Ameer ya matso yana kallon Abiey zuciyarsa da tunani kala kala.
“Akan Waira ne, ta min magana jiya da dare tace tana son ta musulunta ta hannuna saboda na samu wannan ladar, kuma na yi magana da Daddy ya ce zai yi magana da Imam dinsu, sai ya fada mana yadda za'ayi”
Kamin Ummi ta ce komai Abiey yayi murmushi.
“Maa Shaa Allah abu mai kyau, amman dai Ameer ai kasan ina cikin gidan nan ko? Kuma ina da hakki da Waira, kai da ita ina tunanin duk a karkashin ikona kuke, ya kamata ace ka fada min kamin ka aiwatar da komai, ko kuma an fada maka Daddynka ne ya fini son lada ko kuma ni ka raina capacity na ne?”
Ameer ya gagara cewa komai sai kallon rashin fahimta yake yi ma Abiey.
“Ka fada masa zan aiwatar da komai, ba sai yayi ba, yanzu ma muna tattaunawa ne akan maganar tafiyarta Umminka ta fada min cewar Waira tana son ta tafi, ni kuma na goyi bayan haka saboda na fara process din sanin danginta saboda hakan abu ne mai kyau ko dan sanin macen da za a gina iyali da ita, amman ina ganin ba zan barta ta tafi ita kadai ba, sai na sanar da police an ba mu police biyu ko uku, kuma a samu amincewar hukuma sannan kuma ku tafi tare da ita zai fi”
Maleek ya soke kai kasa gabansa sai bugawa yake da karfi. Ummi kuma tana kallon Abiey da wani irin burgewa ganin yana kokarin aiwatar da abun da bata tsammata ba a gurin Ameer. With confused Ameer ya dan ware hannunsa ya ce.
“Maybe ko zata tafi tare da Maleek saboda ta fi sakewa da shi for now ni ina da abubuwan yi da yawa”
“Amman kai zaka fi sanin hanya ai, kuma kai ka fi cewa ku tafi saboda kai kasan inda ka daukota”
Cewar Abiey yana nuna shi.
“Yeah amman Maleek zai fi”
Abiey ya daga kafadunsa
“Shikenan ba zan takura ka ba, duk yadda ka so haka za'ayi, shiga ka taso ta sai ku yi breakfast din a tare ita ma bata ci abinci ba”
“No... Zan yi... ”
Ameer ya so ya musa, sai dai ganin Abiey ya girgiza masa kai alamar aa ya saka dole ya fasa furta abun da zai fada ya nufi upstairs mamaki fal a zuciyarsa, Namra ma mamaki take, balle kuma Maleek da Mahmood da suke ganin kamar Abiey dinsu aka dauke aka kawo wani. Ummi kam jindadi ya hana ta cewa komai. A hankali ya tura kofar dakin Waira ya shiga tsoron kar tace ya mata ba daidai ba ya saka shi tsayawa bakin kofar dakin yana kallon yadda take shafa baby rabbit dinta da hannunta.
“Waira zan iya shigowa?”
Ta juyo ta kalleshi tare da daga masa kai, sai ya maida kofar a hankali ya rufe ya karasa inda take zaune a kasa, ya zauna ya hade kafafuwansa yana kallonta.
“Good morning”
Ya fada yana yafawa fuskarsa murmushi. Tunanin ita ya kamata ta fara gaishe shi ya hana ta amsawa, sai ma mika masa guiwarta da ta yi.
“Good Morning”
“How are you doing today? Beautiful Angel”
Ta sauke kanta kasa ganin irin kallon da yake mata kirin yake jira ya fada cikin idonta ya narke kamar ruwa.
“Abiey ya ce ki fito muje falo mu karya, kuma na yi magana da Daddy na akan musuluntar da zaki yi, yace zai yi magana da Imam dinsu, but then sai kuma Abiey a yanzu yake min maganar cewar zai yi komai ba sai Daddy ya shigo ba, i don't know ko haka din yayi miki?”
Bata ce komai ba, kanta na kasa har lokacin, shi kam a yanzu dai baya gajiya da kallon duk wani abu da ya shafe ta balle kuma ita din kanta.
“Ko kin fi son ki karya a nan?”
“Bari na wanke baki”