Sashe 1
Tubabbiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Root Entry WordDocument 0Table Data [12/31/2019, 3:00 PM] AsmaBaffa: BISMILLAH ALHMDLLH Ina matukar Godiya ga Allah da ya kawo mu,ya bani ikon Rubuta sabon Novel Dina YAR KWANGILA. Fans Ina sonku musamman masu Sharhi,Kar ku gaji da Sharhi shike bamu karfin gwiwar typing. Ina fata kamar yanda muka Fara lfy Allah ya bamu ikon gamawa lfy, Ina muku fatan Alheri,Allah ya Kara Mana lfy da tsawon Rai. TUBABBIYA 1 Official AsmaBaffa Copy by Zainab Butalawa MARCYCOOL and FLOWER page dinku ne na farko. Zamfara state Cikin kauyen Nahuce, Dattijuwa ce Kyakyawar gaske Fara tas da ita baza ta wuce 40yrs ba tana zaune cikin Dan sakarkarin gidansu cikin wata jemammiyar atamfarta, cikin lalatacciyar Hausarta wacce tayi Kama data Igbo can kudu ta Fara kiran suna da karfi tana Khadija...Khadija baza ki Bari ba,wannan wanne iskanshi ne wannan Abu naka,ke ko yaushe burinka ka tafi neman Kudi,Kwangilar banza kwangilar wofi, baka da ko sisi naka,Abinshi da kyar muke samu muci Instead of u muyi Sana'a mu samu kudin rufin Asiri Amma ke Sha Sha Sha kice kudi kika nema kiyi da yawa Haka,a kauyen Nan da muka dawo ga Yara suna zuwa gona suyi grass ko Firewood su siyar su Samu kudi Amma kinki,kece babba kece babbar banza,Ga Babanku ya rasu dangi Basu kula damu,Ki nutsu mu samu mu tsira da mutuncinmu kinki ke Dole kudi me yawa kike bukata ba Kya son motsa jikinki. Wacce aka Kira da Khadija ta turo Dan kyawawan lips dinta jajaye dasu tace yanzu Mama duk kokarin da nake ba Kya gani kullum fa a Rana nake yini Dan kawai na samo Mana na abinci ya kike so nayi,Nace da ke mu koma birni kinki,idan a birni ne Dole zamu samu aikin yi,ke Mama kamar Baki waye ba,kamar bamu zauna a Kudu ba Anambra state fa cikin birni muka taso Amma Mama ke so kike ayi ta aikin Wahala,wani aiki ne a kauyen Arewa in Banda na gona etc,Yanzu ki kwantar da hankalinki Mama na hada Yara kartai manya Almajirai Wanda Zan dinga samun Kwangilar aikin Gona sai na tafi da yarana suyi aikin Noman a biya mu kudi na cire nawa na biyasu kudin aikinsu,kudi za a samu Mama daga Nan har birni sai mu koma ko ya kika ce? Mama ta kalleta kawai tace Khadija ba dai surutu ba,Yanzu Taya manyan kartai zasu saurareki kina Yar 16yrs jibeki fa ki Kuma ba wani jikin girma ne dake ba sai iyayi da giggiwa,Murmushin da Khadija tayi har Dimple dinta suka loba. Tace Mama Mantawa kike da wace Ni,Dan kawai kina ganina kullum a araha,Baki San Nan wa Kika Haifa ba,maybe Matar shugaban kasa kike tare da ita,Baki sani ba ko Matar Gomna ce ma kawai kiyi Addua Mama. Dariya Mama ta saki ba shiri tace to Allah ya taimaka Khadija,yanzu je kiyi sallah kizo Kiyi aikin gidan Nan. Ba musu ta dauki buta tayi Alwala tare da gabatar da Sallar la'asar tana Gama Azkhar ta fito daga rubabben dakinsu ta Fara share share da sauran ayyuka,Wurin 5pm sai ga Maryam wacce suke ce Mata Merry tare da kannensu Ihsan da Ahmad sun dawo daga Islamiyya suna Hey Sister Hey Mama suka wuce ciki tare da Tube Uniform dinsu suka fito wurin Mama dake hada Jallof din Taliya,Khadija data fito daga wanka kenan tace Merry How far? a dey wooo sister,a done tired finished, Go and fresh up jooo cewar Mama wacce ta tsege gogoro irin na manyan Matan Kudu. Khadija kuwa English wear dinta tasa Riga da wando pencil sabo da girman kudu ne Basu fiye sa kayan Hausawa ba sai na turawa Yan gwanjo sabo da rashin sabo. Da dare bayan sunci Abinci Sunyi Sallar Isha Allo suka dauka har Khadija suka tafi makarantar Allon dare ta kauyen. Malam liman yace Khadija biya muji karatun naki, Khadija ta Fara nuna rubutun da tsinke tana Alu, ambaki,wau,zal,ba,Alu Baki,lallan hakuri,minjaye nu'ara,Aya,Alu lallan da shadda,Khadija na zuwa Kan Lallan da shadda ta Dago da sauri tace Hey Malam a Qur'ani har da Shadda tazo? Shi yasa take da tsada da daraja,Liman ya kalleta kawai yayi Murmushi sabo da Khadija Sam Bata gane karatun Allo kawai Yi takeyi ta haddace. Bata yi Shuru ba tace Hakuri hhhhh ta sheke da dariya tace wlh bazan sawa Dana Sunan Nan ba ai gwara Na Sa Masa Nu'ara,Liman ya daka Mata tsawa yace Nan karatu ake ba gurin shiririta bane,kalli kannenki su ba ruwansu,Merry ce ta matso kusa da Khadija itama Ana biya mata, Akace lunguda Merry tace Lungu kawai,Khadija da Bata iya rike dariya sai ta kwashe da dariya tace liman Dan Allah ka fada Mana wannan ba larabci bane? Liman yace larabcine ainihin rubutun Amma Malam bahaushe ne ya fassara da Hausa domin ayi Saurin ganewa,haba yanzu naji zance Dole shadda ta fito a ciki,Bulala liman ya shaudawa Khadija ta saki kara ba shiri suka ci gaba da karatunsu da karfi Khadija ta Ware Murya ba gidan da baa jinta a makwafta,gashi hausarsu Sam Bata fita irin ta Igbo ce bakinsu ya canja. Washe gari akwai wata Igbo Madam Ngozi da Dennis mijinta a kauyen Wanda suka zo kauyen tare da bude katafaran Shago na siyar da kayan kanti,ganin Maman su Khadija sun dawo garin,gasu wayayyu,sannan daga kudu suka dawo kauyen Arewa,sannan Har yaren Igbo suke ji sosai,shike Nan Arnan Igbo Nan suka Kulla zumunci da gidan su Khadija,sosai suke taimakawa su Khadija da kayan Abinci, yau Ma Madam Ngozi tana gidan su Khadija Suna Hira da Maman Khadija cikin Harshen Igbo duk da cewar Suma Ngozi sanadin zamansu a kauyen Shekara da shekaru sun iya Hausa sosai sai dai da kaji Sautin kasan ba Asalin Hausawa bane, Madam Ngozi tace Maman Khadija akwai wani yarona Babba a Enugu yace Yana so Musulunci,Yana son ya musulunta,Ni bana son musulunci Amma yaron ya dage ban san ya Zan Masa ba,Babanshi yace a kyaleshi ya musulunta to Ni gaskiya na hakura na kyaleshi ya musulunta Amma bana so yayi Almajiri,Su Mama me zasuyi ba dariya ba,sabo da tunanin Ngozi Almajiranta tana daga cikin rukunan musulunci,Kuma sunga yanda Almajirai ke komawa a kasar Nan shi yasa,Mama ce ta ganar da ita Mene Almajiri Kuma ta gamsu. Yau da Sassafe Mama ta Kora su Khadija makarantar Allo bayan an Gama Karatu Khadija tana zaune Almajiran da ake kawowa daga kauye ne suke Bata Tausayi,Yan Yara kanana sabo da rashin Imani,iyaye baza su iya daukan nauyinsu ba,yaro da iyayensa Amma a kawoshi Wata uwa duniya yayi ta garari Yana wahala karshe ya lalace ya koma Dan fashi, Kidnapping,Dan Shirka,Dan Ta'adda etc,zuciyar yaro ta bushe da rashin Imani sabo da ya taso a wahala. wasu ma marayune suna da dangi amma sai su kasa rikesu su turosu Almajiranta,sanyi ya Kare musu,Rana,ga wahala malamai suna Basu aikin wahala suna zaluntar yaran sabo da ba yayansu bane,Wasu yaran Kuma sun Riga da sun kangare a gida basa Jin magana,maimakon a Basu tarbiya a kula dasu ayi musu Addua sai iyaye su jefosu duniya suce a kaishi Almajiranta karatu ko zai nutsu,karshe basa karatun kirki sai wahala su Kara lalacewa shike Nan su Zama bala'i a kasa. Sannan mutane ma idan akace wannan Almajiri ne to bashi da daraja a idon Alumma sadaka ma sai abincin da aka rage,ko ya lalace za a Basu,ko a sasu aiki a ki biyansu hakkinsu,Idan yaro yayi magana ace ai Almajiran yanzu Basu da kunya Basu da mutunci baza a Basu Dan Allah ba,ya kamata iyaye musamman na kauye mu Gyara damu Alumma a taru a gyara. Yaro Yana karami yake Fara koyon shirka,burinsa ya samu Hajiya Yana kawo Mata rubutu tana bashi abinci etc. Khadija tana kallon wani Dan yaro karami Yana Bata Tausayi baifi 7yrs ba Yara suna ta tafiya makarantar boko har yaran Malam din duk sunyi Shirin makarantar boko Amma Almajiran su Babu dama Sai Malam ne ma yake hada kansu zai kaisu gonarsa suyi Masa aikin gona,wasu Kuma ya fito musu da manyan itace zasu fassakarawa matansa na girki,Haka wasu sun kwashi wankin matansa sun tafi Rafi,wasu Kuma sun tafi aikin karfi na gini zasu samo Masa kudin cefane sabo da me? Iyayen da Suka bashi yaransu ya koyar dasu Basu tallafawa malamin da kayan Abinci ba bare ya kula da yaransu. Makarantar boko kudi ake tsugewa a biyawa Yara Amma na addini sai ace kyauta,Malam ya kashe lokacinsa na neman Kudi ya koyar da Yara Amma an Hana shi sisin da zai ciyar da iyalansa Dole yaranmu susha wahala a wajen Malaman ba a biyansu ko a taimakesu da abinci kawai Dan karatun Addini ne sai a ce kyauta. Khadija tana mamaki Yaran da zasuyi faskaren Basu Fi 10yrs ba, da kyar suke daga gatarin,sun hada zufa,ko daya Basu faskara ba,Ado ne Dan gidan Malam zai tafi makarantar boko daya cikin Almajiran yace Dan Allah Ado jeka gida ka dakko Mana wani gatarin me kyau wannan Bai da kyau muyi sauri mu Gama Kar Malam ya zanemu,Kallon Banza Ado ya musu yace Baku Isa ba na makara a schl kuje Yan wahala ku dakko da kanku Mana ai Kuna shiga gidan,ya tuka kekensa ya bar wajen,Haka daya yaron yaje gidan ya karbo gatarin sukaci gaba da yi Amma sun kasa komai,Khadija tana gefe tana kallonsu cike da tausayinsu. Malam ne ya fito daga dakinsa Wanda yake saukar mutane da suke Masa layi wajen karben rubutu da layoyi na maganin asirinsu,zagin yaran ya farayi Yana shafda musu bulala Basu faskara ko daya ba,Khadija tayi sauri ta Karasa wajen tare da fisge bulalar daga hannun Malam da lalatacciyar Hausarta Wanda watarana ma sai ta kasa fadar Abu da Hausa sai da turanci ko yaren Igbo,watarana Kuma sai tayi tunanin kalmar da Hausa kafin ta gano ta fada tace haba Liman, Imani Babu? Ina yaranka gasu can manya sun tafi schl boko shine zaka duka wannan yaron Mena suka maka? Kai wlh baka da Imani Malam,Foolish man ne kai,Liman yace Ke Dan ubanki ko ubanki Adamu Bai Isa ya fada min Haka ba bare ke Arnan banza. Khadija da karfi tace ewoooo wonder shall never end so you call me Arna Dan burauba shege,Har ga Allah Khadija tunaninta bakar maganace tayi da Hausa ba zagi ba, liman yace sai Naga gatanku a garin Nan tunda Kika shiga safgata