← Book details Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 59

Sashe 7

Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

hannu tasa ta share mata hawaye tare da fadin ah ah kadeeja dena kuka mana kin manta ke kika cemin so kikeyi kiyi karatu kizama lawyer ki dinga taimakon mutane da iyayenki ba?ke fa kika cemin so kikeyi innarki da baffanki su dawo birni ki gina musu katon gida innarki ta dena daka baffa yabar zuwa gona kenan kin fasa?haba dijangala ta me gari kin san dai bayan wuya se dadi wata rana se labari duk irin cin zalinki da sukeyi wata rana zasu dena ke da zaki girma ki zama hajiya ga gida ga babbar mota ku biyo layi keda me garinki kinsa shi a gaba eye kuma ma idan kince zaki tafi ni ki barni dawa?ai kafata kafarki domin ni dake yanzu mutu ka raba dan haka bana son in kara jin kin sami damuwa akan mutannan kiyi haquri kinji duk me haquri natare da riba tashi maza kici abincinki kada ya huce

maganganun basira sunyi tasiri a zuciyar dije shiyasa ta dan kwantar da hankalinta amma fa wlh ta quduri aniyar duk wanda yayi mata saita rama bakomai zata haqura ba

abincin taci kafin ta tashi tayi wanka inda basira keta bata labaran ban dariya har ta warware gaba daya

*******

haka rayuwa taci gaba da tafiya yayin da dije keta fuskantar muzgunawa itako tanata musu kalolin mugunta amma har yanzu basu dagota ba duk da ya zuwa yanzu ta qara girma kyanta na fulanin asali yaqara bayyana yayin da makerin budurci na nan na kera dije yayin data hadu da qawaye 'ya'yan masu kudi 'yan gayu duk a gunsu take koyar duk wani abu first class yanzu batada aiki sai karatu koda yaushe tana daki ko kicin tana taya baseera aiki sam dijen yanzu ta canza babu wata hayaniya taxama so cool ba yawan surutu su kansu mutan gidan wuyar haduwa sukeyi kasancewar batada amfani a wajensu yasa basu wani damu da rashin ganinta ba ya zuwa yanzu me gari yazo yakai sau hudu kuma ganinta dayakeyi ta canza yasashi jin dadi da kwanciyar hankalin qara barinta gidan kawun nata

******

a dai dai wannan lokacin ana shirye shiryen auran matasan gidan yayin da naseer zai auri yusrah 'yar qanwar mamy shi kuma habeeb zai auri sajida diyar abokin daddy ce babanta ambasserddor ne sajida yarinya ce fist class maqura ce gurin wayewa tanada ilimi sosai amma bata aiki kusan sa'ar habeeb ce dan da kadan ya girme mata amma kasancewar shi namiji ne me son classic lady kuma dayake batada wani girman jiki shiyasa yaji ya kamu da sonta inda suke zuba soyayya ta bugawa a jarida

yau bikin saura sati uku anata hidimar gyara gidan shiyasa kowa yake busy yusrah kam a gidan mamy take domin mahaifiyarta sun rabu da mahaifinta tun tana qarama maman ta kuma wani auren amma a saudiyya suke zaune da mijin kuma mahaifin yusrah ya hanata 'yarsa gashi kuma matar dayake aure batada kirki hakan yasa yusrah gudowa gidan mamy inda kusan nan ta qarasa girmanta

******

yusrah ce zaune da kawayenta a main parlor suna ta tsara yadda hidimar bikin zai kasance

dije ce ta fito sanye da riga da wando indian design kanta babu dankwali sai yalolon gashinta da bashida cika sai matuqar tsawo datasa band ta kama shi ta kuma tufke jelar tayi gammo da ita tun zuwan daddy wancan lokacin ta karbi kudi a gurinsa ta siyo kayan sawa masu kyau da tsada dan ya fada mata komai take so ta tambayeshi kada taji tsoro shiyasa yanzu batada matsala da duk wasu kayan kyale kyale ga qawarta rufaida Aliyu na sayo masu sosai dan itama yarinyar akwai son daukar wanka kuma babanta yanada kudi sosai gashi tanada yayye maza itace kuma auta shiyasa take fantamawa

kitchen ta nufa domin dauko ruwa dan ya zuwa yanzu ta sauqaqawa kanta shan pure water itama faro take sha kamar kowa na gidan

tana daf da shiga ta ji yusra tace keeeee

da kamar ta share sai kuma taga be dace ba dan tasan da ita take dan haka saita tsaya tare da juyowa ta kura mata idanunta masu kama dana mejin bacci

wata kawar yusra ce wow yusrah ina kuka samu wannan kyakkyawar baturiya zance ko balarabiya ne ma oho

me aikin mu ce

me aiki?

kalisat ta tambaya tare da juya lamarin son kudi irin na iyayen yarinyar wannan a yanzu ai jari ce ko tace kadara amma fa hadari ce ga duk gidan da sukayi gangancin daukarta aiki yanzu a ganinta bazata wuce shekara sha bakwai amma dubi yadda take ina ga takai ashirin kuma yusrah ce ta katse mata tunaninta ta hanyar cewa ke me kike so a kawo miki ?

hmmm ni indomie ma ya isa me dan yaji pls juyawa tayi ga sauran kawayenta tace ku kuma fa dayar tace ita kunun aya take so dayar kuma wai jellop din macaroni d kifi sai drinks ko wanne ita kuwa yusrah cewa tayi farfesun kayan cikin rago take so ta kuma hada mata zobo

murmushi dije tayi kafin tace iya wannan sun isa ko kuna buqatar wasu abubuwan

tsawa yusra ta daka mata tare da fadin kijini da munafukar yarinya ina ruwanki da sun ishemu ko basu ishemu ba ai mun san abinda muke buqata shiyasa muka fada miki iya su din dayalla wuce kibawa mutane wuri kiyi abinda nasaki

Allah ya huci zuciyarki Aunty

ta juya ta shiga kitchen tana shiga kamar abun arziki duk abinda suka lissafa ba abinda bata hada ba kuma harta gama Anty basirra bata shigo ba sai da ta jera komai akan wani qaton tray kafin ta nufi parlon yusrah na ganinta ta qara hade fuska wai ita oga

tsugunnawa tayi tare da fadin gashi anty nagama nan ta shiga ajiye wa kowa abinda ya buqata tana gamawa tayi hanyar fita waje yusrah ta rakata da harara kasancewar an dan fara hada hadar biki mamy sun tafi dubai hado lefe shiyasa gidan shuru

kharleesart ce ta fara dibar indomie din domin taci da zafinta domin kuwa yadda ta ganta a ido ga kamshi tanayi tasan zatayi testing tana sawa a bakinta da sauri ta dawo da ita domin wani tsinnanen yaji ne wa nda yake barazanar dauke harshenta

kallonta yusra tayi dai dai takai spoon din hanta bakinta da dukan kuzarinta da sauri ta fito da ita domin wani dan iskan daci dataji ga shi ba alamun maggi ko wasu kayan dandano a ciki shukrah wadda itama dai dai nan ta bude fillet dinta ta diba takai bakinta wani kafirin tsami daya kashe mata haqora tayi saurin hadiyewa maryam kam tana kai kofin kunun aya taji wani mugun gishiri daya kusa dauke mata fatar harshe

miqewa yusrah tayi ta shiga dandana abincin kowa jin abinda taji da sauri ta furzar cike da bacin rai ta miqe da niyyar fita ta jawo dije ta kime ta son ranta dan yau bata san ma kalar dukan dazatayi mata ba watakil saita sumar da ita a yadda takejin zuciyarta

alamar bude falon taji anyi kuma an mayar an rufe ta cikin labule

cike da masifa ta nufo gun ta yaye labulen wata razananniyar qara tayi sakamakon ganin dije idanunta a wurqile ta wani markwade harshe hannunta rike da wata zabgegiyar bulalar ice ga kuma wuqar da ake sara qashi da ita nufo ta tayi ita kuma ta fara ja baya sauran ma duk miqewa sukayi cike da tsoro kowacce na neman maboya

gidan ubanwa zaku ? dije ta fada da wata malkwadaddiyar murya

jikinsu ne yahau kyarma suka qanqame juna suna shirin yin ihu tace duk wanda yayimin ihu a cikinku saina tsaga bakinsa da wannan wuqar ta daga wuqar hannunta qanqame juna suka qarayi suna kuka barinma yusra data qame guri daya dan ita tsoron me aljanu takeyi sosai

ubanwa yasa kusa godiyarmu aiki saboda bama so ta wahala muka girka muku irin girkinmu kuma kuce bazaku ci ba ke harda tashi da tafiya kice zaki kamota ki daka ko ta nuna yusarah

baki na rawa kamar mejin sanyi tace wa..ll..a...hi ah ah bulalar hannunta ta daga ta zuba mata zatayi ihu tace kul kikamin kuka inba haka ba zan sa 'dana yazo ya yini yana dukanki da bulalar qarfe

kama bakinta tayi ta rike tana mutsu mutsu tsananin azabar bulalar daya shigeta ba'amagana jikinta yasaba da hutu gashi yau an daketa da bulalar aljanu wai a hakan ma danta roba ce inaga ansa mata ta qarfe dan haka ta qara gum da bakinta

meye nufinku musha wahalar girka muku abincin kuce bazaku ci ba ko me?

mu din banza cewar maryam wlh zamu ci yanzun nan zamu
ci ko?

da sauri suka shiga girgiza kai eh eh wlh mu mun isa musaku wahalar banza

toh kuyi maza kowacce taci abinda tasa a dafa mata inba haka ba saina sa aljani duna yaxo yayi muku durar kabaki

toh toh munji zamu ci wlh kuyi haquri bayin Allah

kowacce ci takeyi tana kuka duk harshensu ya amsa ga zufa gashi basa son ko kallon fuskar ta ai dama dagani kasan wannan kyan ba'a banza ba harda hadin aljanu

saida suka cinye komai tass bnda kuka da majina da dallo harshe ba abinda sukeyi sunata budar baki sannan ta miqe tace daga yau ko kallon banza kuka karawa godiyarmu wlh saina ci ubanku kuma naji kun fadawa wani wannan abinda yafaru duk saina biki gidajenku ni kadai nasan mezan muku ku tashi ku fita waje zan tafi inbar godiyata tayi bacci

da gudu suka nufi qofa harshe a waje baki bude kamar irin mayu suna fita suka zube gurin shukrah data sha kunu aya me gishiri amai kawai takeyi itada yusrah suko su kaleesart banda kartawa ba abinda cikinsu keyi alamar y yamutse kenan

suna fita ta rushe da dariya tare da hada kwanukan ta nufi kicin tana fadin shegun banza wlh kadan kuka gani dan na fuskanci saina gyara muku zama tana wanke kwanukan data bata tana dariya a haka harta gama ta fita ta dauki ruwanta ta koma daki har yanzu dai basira bacci takeyi Allah sarki kodan yawan aikin datakeyi ne

sukuwa suna nan zaune duksun baza baki sun baje a gurin banda kuka da kakari da nishi ba abinda sukeyi motar su naseer ta kunno kai

*alqalamin shady*✍
Chapter 7 · 0% Book details