Sashe 4
Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ganin yadda maganar ta shigeshi yasa su habeeb tambayar sa wacece dije?
kanwarku ce diyar gurin inusa
ku tashi muje duka suka miki suka bi shi
koda suka iso gurin sun iske dandazon mutane an taru koda akaga me gari kowa ya ratse yabashi hanya ya isa gurin inda yaga dije tsaye me mashin ya rike mata hijabi itako ko a jikinta tanata gwagwiyar goruba
rasa ma me zai ce yayi inda ya qarasa yana fadin malam dan Allah sakarta mana
wlh baba bazan saketa ba sai an biyani kudina
nawa ne kudin naka?
naira hamsin ne
yanzu kai da duk akan nera hamsin katarawa mutane wannan jama'ar
toh ai hakkina ne naga kuma akan sana'ata ne
toh garin yaya kudi ya hadaku?
nan yakwashe komai yafada masa aljihu ya laluba ya ciro nera dari yabashi yace yabar canjin sannan yasaki dije malam yakama hannunta suka nufi cikin gida su habeeb sam basu lura ba dan suna waya ne da mumy sai da suka gama suka juya suka hango bayan me gari rike da hannun wata yarinya ze shiga gida nan suka nufi gidan suma
tsaye ya tadda matansa da sauran ahlin gidan duk tsaitsaiye suna jimamin abin nan yabasu labarin ainihin abinda yafaru kowa ya kalli dije wadda har yanzu bata cewa kowa kanzil ba tanata dai cin goribarta ana haka su naseer suka shigo kasancewar dije ta juya baya nan suka tambayu meya faru nan malam ya shiga sanar dasu cikin zolaya habeeb yace tab ashe kuwa yau sai na bawa budurwar kauye kashi dai dai nan dije ta juyo akayi ko sa'a tasha kwalliyar nan sai dai yau jambaki tasaka kanta kile sabanin baya
wani uban ihu naseer yasaki inda shima habeeb ya karba suka fara fadin gata nan itace suka kwasa da gudu sai dakin inna dudu suka rufo
mamaki ne yakama kowa yayin da dije ta zube a gurin tanata dariya ganin haka malam ya dauka shedananta ne dan haka be bi ta kanta ba ya nufi dakin da suka rufe anyi anyi su bude sunki dije ce ta taso tazo dai dai kofar windo ta leka tace in baku bude kofar nan ba saina kwakule muku idanu da sauri suka taso suka hau kokawar bude kofa tun daga nan malam ya fahimci karatun suna budewa dije ta kara fashewa da dariya zasuyi ihu me gari ya buga musu tsawa yace dama wannan ce aljanar datake tsorata ku?
eh itace wlh itace shi kanshi me garin yaso yin dariya ganin yadda duk jikinsu ke kyarma
to ai itace kanwarku diyar babanku inusa a shakiyancin dije nasan zata aikata fiye da haka
dimmm sukayi gaba dayansu inda suka kai dubansu ga dije wadda ta dallaro harshe tare da yimusu gwalo tace ni ba aljanah bace gyadata kuka takemin ta zube ina shirin in tsince naji fitsari na juya inyi koda na juyo naga kun takemin ita shine nayi maganinku
tunda tafara magana zuciyar mazan tahau lugude musamman. habeeb da yayi asarar hakorinsa guda na kasa saboda abin wayyo Allah
muje zuwa readers yawan comments yawan page
[16/12, 11:40] +234 806 493 3819: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
na
khadija usman
6⃣
*wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkan member's na khadija fans novels hakika naga ruwan comments da kuma masu bina pc nagode sosai Allah yabar kauna*
ta jima zaune kafin daga baya taji alamun dawowarshi mika mata yayi tare da canjin tace ya rike canjin ta karbi maganin a bakar leda ta shiga cikin gidan
tunani ta shiga yi shin wai ta inama zata fara ne wai wazata fara yiwa illa habeeb,nasir,mamy,ko uwar mugaye yusra ah ah takan ya habeeb zan fara tunda shi yafara min mugunta
mikewa tayi ta shiga kitchen cikin sa'a ta riski basira na zuba coffee cikin cups kallonta tayi tace sannu da aiki Anty na
murmushi basira tayi yayin data kamo hannun ta cike da tausayawar abinda aka mata dazu tace sannu dije kiyi haquri da abinda ke faruwa gidan nan ki dinga taka tsantsan da hajiya dan wlh batada imani suna iya hanaki abincin kwana ukun dasuka ce dan haka kada kidamu zan dinga boye miki a daki da zarar kin tashi ci zan nuna miki inda zan dinga ajiye miki
dariya dije tayi kafin tace kada ki damu Anty ai daga yau har zuwa kwanakin da suka dibar min zanci abinda raina ke so ke dai kawai kisa ido kiyi kallo nice fa dije wlh a kauyenmu anno ba ake cemin duk gidan dana leqa saina sasu jinya dan haka sai sun san nice sukawa haka da naso in canza amma naga basu san kara ba gara ayi gwari gwari
mamaki ne yakama basira inda take kallon dije daketa zaro zance ba wakafi ba aya duk da take qaramar yarinya dan ita a ganinta bazata wuce shekara sha biyar ba amma ta iya tsara zance kamar redio amma kuma in akayi la'akari da dabara irin ta mutanen kauye wannan ba komai bane
farantin data dora kofunan akai ta dauka da niyyar fita dije tace ina zaki kuma Aunty ?
wadan can 'yan sudan din zan kaiwa shayi wai da yamman nan kin san su
ah ah kawo inkai musu ki huta ai kinyi aiki kin gaji naga ma kamar bacci kikeji dan haka jeki kwanta ki dan huta zan qarasa aikin kije ki
toh kadafa kije suyi miki wata muguntar kuma
ah ah ba komai ai haquri zan basu kada ki damu
mika mata tray din tayi ta fita dai dai wani dan corridor ta labe ta fito da ledar daga jikinta ta bude juya maganin tayita yi dan ta rasa na bacci dana kashi kawai shahada tayi ta babbala sachet daya a cikin biyun ta juye cikin daya kofin dayan na hannunta ta fara barewa shima da alama kam wannan shine na baccin tafada a bayanne dan naga shi inna ta siyawa Ahmadu lokacin data daukoshi yaye shima duka guda goma ta juye ta dinga juyawa har duka suka narke kafin ta mike ta boye sauran a wani loko inta dawo ta dauka ta nufi part dinsu
ta dan jima a tsaye kafin daga haya tayi knoking
shigo kawai basira taji ance murda handle din kofar tayi ta kunna kai parlon da sallamar ta habeeb zaune daga shi sai boxer da singlet yana zaune yana duba system dinshi da alama wani aikin yakeyi me muhimmanci duba da yadda yamaida hankalinshi gaha daya ga abinda ke gabanshi
shiko naseer jallabiya ce a jikinshi yana zaune yana danna waya da alama charting yakeyi
naseer ne ya amsa sallamarta inda ya dago idonsa tare da wurga mata harara uban me yakawoki dakin nan ?
um dama itace batajin dadi shine tace in taimaka in kawo muku
tsaki yaja kafin ya maida hankali ga wayarshi
qarasawa tayi ta durkusa ta ajiye cup daya a gabanshi sannan ta nufi gurin habeeb shima ta ajiye masa nashi shi kam ko kallonta beyi ba dan haka ta mike ta nufi hanyar fita
har takai kofa taji muryarsa yana fadin idan naqara ganinki a dakin nan wlh saina lahira yafiki jin dadi shegiya me siffar aljanu nunar rana kawai
itadai bude kofar tayi tay ficewarta inda shi kuma ya jawo coffee dinsa yafara sha jiyayi na yau yafi na kullum dadi dan wani kamshi da dan zaki zaki yayi dan haka ya dinga sirba baji ba gani shima naseer haka yayita sheqe abinshi inda shi kuma beji wani canji ba
hamma yake tayi baji ba gani yayin da yafara ganin uku uku dan haka ya mike ya nufi bedroom yana tangadi kamar dan maye sam yarasa wannan wane irin bacci ne yazo mai lokaci daya
naseer daya bishi da kallo yana ambatar lfy dai bros naganka ka sauya
cikin murya irin ta wanda bacci yakama sosai yace lfy qalau kawai bacci nakeji bari in dan matse duk da naga yamma tayi
ok a tashi lfy
bai bashi amsa ba ya shige ciki kawai shi ko yaci gaba da abinda yakeyi
yana cikin haka kusan minti talatin yaji cikinsa yayi wata irin murdawa da ya dan share amma daga baya yaji bazai iya ba dan kamar ba haya yakeji dan haka ya mike ya shiga toilet din dake falon yana ko shiga yafara antayo abinsa rai fesss
itako dije tana fita kicin ta koma ta tarar da basira harta koma daki freidge ta bude ta fara kwashe lemukan ciki kamar wadda aka sa guda biyu kawai ta bari ta dauko su ta bude tare da zuzzuba wannan maganin kashin aciki kowanne sachet daya daya kana ta mayar ta rufe alamar motsin tafiya taji cikin sauri ta rufe friedge din ta tashi ta nufi cabinet tajawo filet ta kama daurayewa kamar me wanke wanke
mamy ce ta shigo kitchen din tana kiran sunan basira ganin dije a tsaye tana aiki yasata tambayar ina basira ta shiga?
batajin dadi ne shine nake tayata kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta
wani wawan kallo mami ta watsa mata kafin tace hmmm ai dama aikin shiyafi dacewa dake a gidan nan maza ki daukomin lemo a friedge ki kawo mana dinning muna jira zamuci abinci
toh ta amsa ita kuma mamy ta juya ta fita
dariya dije ta fara yi tare da fadin komai kuke so zanyi muku amma ni da lfyr ku zan fanshe
lemukan ta diba ta nufi falon inda ta iske mamy da yusra har sun fara cin abincin ajiye lemon tayi da niyyar juyawa taji yusrah tace
ke aljana me siffar tumatur uban waye zai zuba miki lemon toh
dawowa tayi ta bude ta zubawa kowa ita gwara ma da suka ce ta zuba musu din dan da sun taba murfin da da kansu zasu gane an bude lemo a zuciyarta tana jinjina kalar muguntar da zata yiwa yusrah dan da Alama tata saita fi ta kowa barin gurin tayi da sauri ta nufi dakinsu
inda su hajiya aka baje koma aka dankari abinci da drinks. kasancewar lemon da sanyi kuma na roba ne shiyasa suka kusa shanye su dan kadan suka bari
sun dan jima suna hira kafin mamy taji cikinta ya murda alamar tanajin bayan gida
mikewa tayi ta shiga bedroom dinta ta afka toilet
kanwarku ce diyar gurin inusa
ku tashi muje duka suka miki suka bi shi
koda suka iso gurin sun iske dandazon mutane an taru koda akaga me gari kowa ya ratse yabashi hanya ya isa gurin inda yaga dije tsaye me mashin ya rike mata hijabi itako ko a jikinta tanata gwagwiyar goruba
rasa ma me zai ce yayi inda ya qarasa yana fadin malam dan Allah sakarta mana
wlh baba bazan saketa ba sai an biyani kudina
nawa ne kudin naka?
naira hamsin ne
yanzu kai da duk akan nera hamsin katarawa mutane wannan jama'ar
toh ai hakkina ne naga kuma akan sana'ata ne
toh garin yaya kudi ya hadaku?
nan yakwashe komai yafada masa aljihu ya laluba ya ciro nera dari yabashi yace yabar canjin sannan yasaki dije malam yakama hannunta suka nufi cikin gida su habeeb sam basu lura ba dan suna waya ne da mumy sai da suka gama suka juya suka hango bayan me gari rike da hannun wata yarinya ze shiga gida nan suka nufi gidan suma
tsaye ya tadda matansa da sauran ahlin gidan duk tsaitsaiye suna jimamin abin nan yabasu labarin ainihin abinda yafaru kowa ya kalli dije wadda har yanzu bata cewa kowa kanzil ba tanata dai cin goribarta ana haka su naseer suka shigo kasancewar dije ta juya baya nan suka tambayu meya faru nan malam ya shiga sanar dasu cikin zolaya habeeb yace tab ashe kuwa yau sai na bawa budurwar kauye kashi dai dai nan dije ta juyo akayi ko sa'a tasha kwalliyar nan sai dai yau jambaki tasaka kanta kile sabanin baya
wani uban ihu naseer yasaki inda shima habeeb ya karba suka fara fadin gata nan itace suka kwasa da gudu sai dakin inna dudu suka rufo
mamaki ne yakama kowa yayin da dije ta zube a gurin tanata dariya ganin haka malam ya dauka shedananta ne dan haka be bi ta kanta ba ya nufi dakin da suka rufe anyi anyi su bude sunki dije ce ta taso tazo dai dai kofar windo ta leka tace in baku bude kofar nan ba saina kwakule muku idanu da sauri suka taso suka hau kokawar bude kofa tun daga nan malam ya fahimci karatun suna budewa dije ta kara fashewa da dariya zasuyi ihu me gari ya buga musu tsawa yace dama wannan ce aljanar datake tsorata ku?
eh itace wlh itace shi kanshi me garin yaso yin dariya ganin yadda duk jikinsu ke kyarma
to ai itace kanwarku diyar babanku inusa a shakiyancin dije nasan zata aikata fiye da haka
dimmm sukayi gaba dayansu inda suka kai dubansu ga dije wadda ta dallaro harshe tare da yimusu gwalo tace ni ba aljanah bace gyadata kuka takemin ta zube ina shirin in tsince naji fitsari na juya inyi koda na juyo naga kun takemin ita shine nayi maganinku
tunda tafara magana zuciyar mazan tahau lugude musamman. habeeb da yayi asarar hakorinsa guda na kasa saboda abin wayyo Allah
muje zuwa readers yawan comments yawan page
[16/12, 11:40] +234 806 493 3819: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
na
khadija usman
6⃣
*wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkan member's na khadija fans novels hakika naga ruwan comments da kuma masu bina pc nagode sosai Allah yabar kauna*
ta jima zaune kafin daga baya taji alamun dawowarshi mika mata yayi tare da canjin tace ya rike canjin ta karbi maganin a bakar leda ta shiga cikin gidan
tunani ta shiga yi shin wai ta inama zata fara ne wai wazata fara yiwa illa habeeb,nasir,mamy,ko uwar mugaye yusra ah ah takan ya habeeb zan fara tunda shi yafara min mugunta
mikewa tayi ta shiga kitchen cikin sa'a ta riski basira na zuba coffee cikin cups kallonta tayi tace sannu da aiki Anty na
murmushi basira tayi yayin data kamo hannun ta cike da tausayawar abinda aka mata dazu tace sannu dije kiyi haquri da abinda ke faruwa gidan nan ki dinga taka tsantsan da hajiya dan wlh batada imani suna iya hanaki abincin kwana ukun dasuka ce dan haka kada kidamu zan dinga boye miki a daki da zarar kin tashi ci zan nuna miki inda zan dinga ajiye miki
dariya dije tayi kafin tace kada ki damu Anty ai daga yau har zuwa kwanakin da suka dibar min zanci abinda raina ke so ke dai kawai kisa ido kiyi kallo nice fa dije wlh a kauyenmu anno ba ake cemin duk gidan dana leqa saina sasu jinya dan haka sai sun san nice sukawa haka da naso in canza amma naga basu san kara ba gara ayi gwari gwari
mamaki ne yakama basira inda take kallon dije daketa zaro zance ba wakafi ba aya duk da take qaramar yarinya dan ita a ganinta bazata wuce shekara sha biyar ba amma ta iya tsara zance kamar redio amma kuma in akayi la'akari da dabara irin ta mutanen kauye wannan ba komai bane
farantin data dora kofunan akai ta dauka da niyyar fita dije tace ina zaki kuma Aunty ?
wadan can 'yan sudan din zan kaiwa shayi wai da yamman nan kin san su
ah ah kawo inkai musu ki huta ai kinyi aiki kin gaji naga ma kamar bacci kikeji dan haka jeki kwanta ki dan huta zan qarasa aikin kije ki
toh kadafa kije suyi miki wata muguntar kuma
ah ah ba komai ai haquri zan basu kada ki damu
mika mata tray din tayi ta fita dai dai wani dan corridor ta labe ta fito da ledar daga jikinta ta bude juya maganin tayita yi dan ta rasa na bacci dana kashi kawai shahada tayi ta babbala sachet daya a cikin biyun ta juye cikin daya kofin dayan na hannunta ta fara barewa shima da alama kam wannan shine na baccin tafada a bayanne dan naga shi inna ta siyawa Ahmadu lokacin data daukoshi yaye shima duka guda goma ta juye ta dinga juyawa har duka suka narke kafin ta mike ta boye sauran a wani loko inta dawo ta dauka ta nufi part dinsu
ta dan jima a tsaye kafin daga haya tayi knoking
shigo kawai basira taji ance murda handle din kofar tayi ta kunna kai parlon da sallamar ta habeeb zaune daga shi sai boxer da singlet yana zaune yana duba system dinshi da alama wani aikin yakeyi me muhimmanci duba da yadda yamaida hankalinshi gaha daya ga abinda ke gabanshi
shiko naseer jallabiya ce a jikinshi yana zaune yana danna waya da alama charting yakeyi
naseer ne ya amsa sallamarta inda ya dago idonsa tare da wurga mata harara uban me yakawoki dakin nan ?
um dama itace batajin dadi shine tace in taimaka in kawo muku
tsaki yaja kafin ya maida hankali ga wayarshi
qarasawa tayi ta durkusa ta ajiye cup daya a gabanshi sannan ta nufi gurin habeeb shima ta ajiye masa nashi shi kam ko kallonta beyi ba dan haka ta mike ta nufi hanyar fita
har takai kofa taji muryarsa yana fadin idan naqara ganinki a dakin nan wlh saina lahira yafiki jin dadi shegiya me siffar aljanu nunar rana kawai
itadai bude kofar tayi tay ficewarta inda shi kuma ya jawo coffee dinsa yafara sha jiyayi na yau yafi na kullum dadi dan wani kamshi da dan zaki zaki yayi dan haka ya dinga sirba baji ba gani shima naseer haka yayita sheqe abinshi inda shi kuma beji wani canji ba
hamma yake tayi baji ba gani yayin da yafara ganin uku uku dan haka ya mike ya nufi bedroom yana tangadi kamar dan maye sam yarasa wannan wane irin bacci ne yazo mai lokaci daya
naseer daya bishi da kallo yana ambatar lfy dai bros naganka ka sauya
cikin murya irin ta wanda bacci yakama sosai yace lfy qalau kawai bacci nakeji bari in dan matse duk da naga yamma tayi
ok a tashi lfy
bai bashi amsa ba ya shige ciki kawai shi ko yaci gaba da abinda yakeyi
yana cikin haka kusan minti talatin yaji cikinsa yayi wata irin murdawa da ya dan share amma daga baya yaji bazai iya ba dan kamar ba haya yakeji dan haka ya mike ya shiga toilet din dake falon yana ko shiga yafara antayo abinsa rai fesss
itako dije tana fita kicin ta koma ta tarar da basira harta koma daki freidge ta bude ta fara kwashe lemukan ciki kamar wadda aka sa guda biyu kawai ta bari ta dauko su ta bude tare da zuzzuba wannan maganin kashin aciki kowanne sachet daya daya kana ta mayar ta rufe alamar motsin tafiya taji cikin sauri ta rufe friedge din ta tashi ta nufi cabinet tajawo filet ta kama daurayewa kamar me wanke wanke
mamy ce ta shigo kitchen din tana kiran sunan basira ganin dije a tsaye tana aiki yasata tambayar ina basira ta shiga?
batajin dadi ne shine nake tayata kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta
wani wawan kallo mami ta watsa mata kafin tace hmmm ai dama aikin shiyafi dacewa dake a gidan nan maza ki daukomin lemo a friedge ki kawo mana dinning muna jira zamuci abinci
toh ta amsa ita kuma mamy ta juya ta fita
dariya dije ta fara yi tare da fadin komai kuke so zanyi muku amma ni da lfyr ku zan fanshe
lemukan ta diba ta nufi falon inda ta iske mamy da yusra har sun fara cin abincin ajiye lemon tayi da niyyar juyawa taji yusrah tace
ke aljana me siffar tumatur uban waye zai zuba miki lemon toh
dawowa tayi ta bude ta zubawa kowa ita gwara ma da suka ce ta zuba musu din dan da sun taba murfin da da kansu zasu gane an bude lemo a zuciyarta tana jinjina kalar muguntar da zata yiwa yusrah dan da Alama tata saita fi ta kowa barin gurin tayi da sauri ta nufi dakinsu
inda su hajiya aka baje koma aka dankari abinci da drinks. kasancewar lemon da sanyi kuma na roba ne shiyasa suka kusa shanye su dan kadan suka bari
sun dan jima suna hira kafin mamy taji cikinta ya murda alamar tanajin bayan gida
mikewa tayi ta shiga bedroom dinta ta afka toilet