Sashe 34
Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ai Alhaji basaika bada komai ba ni duk zanyi komai dan yarinyar nada kirki sosai
dije da tunda mamy tayi magana ta dago ta kalleta ta fahimci abinda take shirin aikata mata amma ba damar tayi magana haka jiki ba kwari ta mike tayi musu saida safe yayin da mamy ta bita da kallon sai kin raina kanki
******
shuru shuru har daddy ya gama abinda zaiyi ya tafi dije bata ji an qara mata maganar kudi ba sai bayan ya tafi mamy ta kirata ta shiga zaginta tare da sanar da ita indai tana raye to baxata kara bari taci kudin daddy ba sannan in tana son kanta da arziki ta tattara kayanta ta koma kauye
bakaramin damuwa dije ta shiga ba jin muguntar da mamy ta shirya mata yanzu ina mafita?
ba yadda za'ayi dai ta sanar da rufaida dan tana mata kokari akan komai yanzu kuma bikinta za'ayi yakamata ta taka rawar gani to yanzu yazatayi kenan ?
tunani ta shiga yi kafin daga baya tasami mafita tsalle ta buga tare da fadin yessss sai ni dijen.mai gari nawa
baseera dake zaune tana linke kayanta ta dago ta kalleta tace yadai lafiyarki kuwa ?ko sunzo ne in san nayi?
dariya dije tayi kafin tace kedai bari kawai wata tsiya zan tsula wlh a gidan nan
sakin baki baseera tayi kafin tace ke khadija tsiyar me kuma?dan Allah kada tarihi ya maimaita kansa ki hada harda ni
dariya dije tayi kafin tace wallahi ni har kin tunamin ma dan sam na manta da wannan lokacin dan a cikin shika shikan ta'addancin danayi bana sa wannan a ciki saboda kankantar sa
yanzu ke khadija wannan ne karami to shi babban ya yake kenan?
ki tambayi su yaya habeeb zasu baki labari
zaro ido tayi kafin tace rufamin asiri nidai dan girman Allah ki rufamin asiri kada ki hada dani
ai ke kada ki damu ko inawa kowa wlh banda ke Aunty na mamana badan kin haife ni ba ta karasa maganar tana dariya
haka suka dinga hirarsu cikin nishadi kwanciyar hanksli amma zuciyar dije nacan na saka da warwara
****
dare yayi dan kusan qarfe daya da wani abu ake nema kasancewar zafi akeyi sosai duk da A.c dake kunne da fanka hakan bai hana mamy jin zafi ba a cewarta dan haka ta fito falo ta dan kishingida har bacci mai nauyi ya dauketa
dije da saboda abinda ke ranta baccinma ta kasa yi saboda haka ta fito cikin sanda dan sam bata lura da mamy ba saida taji munshari
Alhmdllh ta fada a ranta inda direct ta nufi dakin mamy kai tsaye ta shiga bincike ko'ina inda tana bude wata hand bag din mamy tayi tozali da kudi rafar 'yan dubu dubu
dariya tayi inda ta dauki dauri biyu tasa kai ta fice tana dariya a ranta tana kissima dramer da za'ayi gobe
*niko nace su dije an fara 'dan hali ne ko kuma me?* 🤔
****
tunda asuba da dije tayi sallah ta fito falo ta zauna tare da tsintsiya a hannunta da mofa dake cikim bucket da ruwa tana nan zaune dataji kamar motsi saita mike da saur ta fara shara a haka har mamy ta fito shirye cikin shiga ta alfarma da alama fita zatayi
tunda dije ta ji motsi ta mike ta fara shara tanayi tana sharar kwallah kamar wadda aka cewa ubanta ya mutu
mamy ce ta kalleta cike da mamaki ganin yadda kwalla wata ke bin wata tace ke kuma uban me yasameki kike shara kina kuka kamar wadda aka sa dole
banza dije tayi da ita taci gaba da yadda takeyi duk da ta dan soma gajiya
ke ba magana nake miki ba ban son iskanci fa wallahi zan ci ubanki kijini da 'yar iskar yarinya
batare da dije ta dago ba ta ce kema zaifi miki kyau ki fara kuka tun yanzu dan ni na kusa gama nawa
cikin rashin fahimtar maganarta tace ban gane ba
kin kusa mutuwa
mamy shiyasa nake kuka
kijini da 'yar buta...........uba ubanki ne ke kashewa da zaki kalleni kice na kusa mutuwa to a ina kika sani
juya baya dije tayi ta ciro hakoran robar data siyo masu kamar na horo na wasan yara tasa wanda tun jiya taso tsorata mamy dashi da dare amma data samu kudin dataje nema kawai saita fasa ta barta ta huta yau sa gamu
to ko ke mayya ce wallahi kinyi kadan kice zan mutu yau kujini da shegiya kin juya min baya kamar allo juyo ki kalleni ki fadamin mana in daki bakinki sai hakoranki sun zube
jiyowa dije tayi sukayi ido hudu da mamy
wata razananniyar kara mamy tasaki yayin data yadda jakarta ta nufi daki amma ina dije ta cimmata ta rike mata kafa
runtse ido mamy tayi ta shiga ihu iya karfinta yayin da dije tayi saurin cire abin dan ta sami damar yin magana tace ki ciremin hokaran mana ko kin fasa?
*zan yi kokari. yi muku posting kullum.yanzu ku kara hakuri typing akwai wahala wallahi*
*Alqalamin khady* ✍
[3/15, 11:18 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TAME GARI*
NA
khadija usman
3⃣3⃣
innalillahi cewar mamy ta fada da karfinta baseera da taji ihun mamy ta leqo amma ganin dije a tsaye ga mamy ta kure da bango yasa ta fahimci dije ta fara aikinta kamar yadda tace dan haka ta sakada daga gefe tana kallon yadda za'a kwashe
su kuwa su habu driver da me gadi sun jiyo ihu amma basuda tabbacin daga inda ya fito dan haka suka baza kunne dan jin inda zai qara fitowa jin shuru ba'a kuma yi ba yasa suka qara maida hankali ga hirarsu
in banda rawa babu abinda jikin mamy keyi yayin da take ta tuna da mafarkan datake yawan yi akan dije ashe yarinyar dama garken aljanu ne akanta shiyasa ta addabi rayuwar kowa kenan duk irin tsarin datake sha na mayu da aljanu gashi beyi aiki akan wannan yarinyar ba yau abin yazo kanta sam takasa dagowa ta kalli dije
itako dije hakan ne ya qara bata dama ta kara maqe murya ita ala dole jinsin aljanu (niko nace dije ina tausaya miki ranar da dubunki ta cika aka ramfo ki) kince zaki ciremin hakora to ki tashi ki fara aikinki mana dan kin san sai kin nemo katafila wajen babbago shi to kada ki bata shekaru kinayi gara ki fara da wuri zan tausaya miki in rangwanta miki albarkacin kina matsayin uwa ga masoyiyar mu dan haka bari nasa a kawo miki kayan aiki irin namu zasu sauqaqa miki duk da bai zama lallai ki iya daga wasu daga ciki ba amma zan taimaka miki dan cikar burinki
wallahi ni banida wani buri a rayuwata cewar mamy baki na rawa idonta rufe ta hada hannu biyu gaban dije ni da kike ganina tun ina qaramata burina bai wuce inyi aure in haifi yara biyu ba kuma Allah ya cikamin bayan wannan yanzu banida wani kuma
ah ah kinada shi mana
wallahi banida shi
karima kina fa dashi
ranku ya dade dan daga jin muryar nan wlh kunfi dubu dan haka ku yadda banida shi
munce kinada shi kariiimaaaa dije ta fada cikin 'dan daga murya
ai mamy bata san lokacin data tuma a kasa ba tayi rufda ciki ta saki kuka wanda in bata manta ba ko kar tayi karya da saita ce marabinta da kuka tun na amarci 😂amma yau gata tsofai tsofai da ita an sata kuka wayyo ita karima
muryar dije taji tana fadin bama son musu a iya binciken da nayi mun gano kinada manyan buruka a rayuwarki ciki harda korar uwar dakinmu daga gidan nan
ni din banza ni na isa in raba hanta da jini ai khadija tafi kowa cancanta da zama a gidan nan ni duk duniya akwai yarinyar danake so irin ta
karya muka yi miki kenan?
wallahi ko uban ubana bai isa yace kuna qarya ba kuda a halittar ku sam baku san wani abu wai shi karya ba ta yaya zance kuna qarya ai ban isa ba takarasa maganar tana me jan majina da matso hawaye
to tunda kin san haka meyasa kike shiga shirgin daba naki ba mun so mu sauqaqa miki shiyasa muka sa ta koma gidan 'ya'yanki amma kika san yadda kikayi kika dawo da ita nan wannan ma bai isheko ba wato saida kk hana mai gidan biya mata bukatar data tambaya alhalin ke bayi mata zakiyi ba
wallahi yaseen kwarankwasa kinji na rantse ba laifina bane dawowar ta gidan nan wlh sharrin yarana ne dan dama shi habeeb tun yana shan nono na fuskanci baida son mutane shi kuwa naseer tsegumi to yawan tsegumin su yasa nace ta dawo gida kuma kinga abin Allah saiya hadasu da munafukan mata wlh ba yin kaina bane su suka dinga zuga mazan to dama abu ya tadda hali musamman naseer da yusra sarakan munafurci su suka qara iza wutar duk da nasan gaskiya nasan khadija batada fitina to sbd bana son sunanta ya baci shiyasa naje na taho da ita kuma batun Alhaji danace kada ya bata kudi wlh ni nayi niyyar yimata komai da take bukata dan yanzu haka ma can nayi inda zan gwangwajeta da kaya na alfarma inda nake son tafi amaryar ma haduwa da tsari dan kun san khadija ba baya ba wajen kyau sannan ga.......
ya isa haka amma kin makaro dan yanzu haka har su akuyatu wadanda muke cousins da su sun dauki wani abu a jakarki yanzu zasu tafi suyi sadaka da su domin almajiran mu sun cika kofar gidan nan
cikin mamy ne yabada kuuuu wata muguwar gudawa ta taso mata jin wai an kwashi kudi a jakarta za'a rabawa almajiran aljanu wayyo ta shiga uku bata ankare ba ko taji ta jika wandonta da dan karamin zawo
jin dan doyi da dije tayi yasata fadin warin me nakeji haka ta fada tana toshe hancinta
mamy data tabbatar bako tantama zawi tayi yasata fadin wlh inaga jaba ce ko beraye sukayi tusa a store duk da zuciyarta na rawa ta fadi hakan dan tasan sun gama sanin me tayi amma bari tayi karyar kare kai Allah yasa kada su gano
dije da tunda mamy tayi magana ta dago ta kalleta ta fahimci abinda take shirin aikata mata amma ba damar tayi magana haka jiki ba kwari ta mike tayi musu saida safe yayin da mamy ta bita da kallon sai kin raina kanki
******
shuru shuru har daddy ya gama abinda zaiyi ya tafi dije bata ji an qara mata maganar kudi ba sai bayan ya tafi mamy ta kirata ta shiga zaginta tare da sanar da ita indai tana raye to baxata kara bari taci kudin daddy ba sannan in tana son kanta da arziki ta tattara kayanta ta koma kauye
bakaramin damuwa dije ta shiga ba jin muguntar da mamy ta shirya mata yanzu ina mafita?
ba yadda za'ayi dai ta sanar da rufaida dan tana mata kokari akan komai yanzu kuma bikinta za'ayi yakamata ta taka rawar gani to yanzu yazatayi kenan ?
tunani ta shiga yi kafin daga baya tasami mafita tsalle ta buga tare da fadin yessss sai ni dijen.mai gari nawa
baseera dake zaune tana linke kayanta ta dago ta kalleta tace yadai lafiyarki kuwa ?ko sunzo ne in san nayi?
dariya dije tayi kafin tace kedai bari kawai wata tsiya zan tsula wlh a gidan nan
sakin baki baseera tayi kafin tace ke khadija tsiyar me kuma?dan Allah kada tarihi ya maimaita kansa ki hada harda ni
dariya dije tayi kafin tace wallahi ni har kin tunamin ma dan sam na manta da wannan lokacin dan a cikin shika shikan ta'addancin danayi bana sa wannan a ciki saboda kankantar sa
yanzu ke khadija wannan ne karami to shi babban ya yake kenan?
ki tambayi su yaya habeeb zasu baki labari
zaro ido tayi kafin tace rufamin asiri nidai dan girman Allah ki rufamin asiri kada ki hada dani
ai ke kada ki damu ko inawa kowa wlh banda ke Aunty na mamana badan kin haife ni ba ta karasa maganar tana dariya
haka suka dinga hirarsu cikin nishadi kwanciyar hanksli amma zuciyar dije nacan na saka da warwara
****
dare yayi dan kusan qarfe daya da wani abu ake nema kasancewar zafi akeyi sosai duk da A.c dake kunne da fanka hakan bai hana mamy jin zafi ba a cewarta dan haka ta fito falo ta dan kishingida har bacci mai nauyi ya dauketa
dije da saboda abinda ke ranta baccinma ta kasa yi saboda haka ta fito cikin sanda dan sam bata lura da mamy ba saida taji munshari
Alhmdllh ta fada a ranta inda direct ta nufi dakin mamy kai tsaye ta shiga bincike ko'ina inda tana bude wata hand bag din mamy tayi tozali da kudi rafar 'yan dubu dubu
dariya tayi inda ta dauki dauri biyu tasa kai ta fice tana dariya a ranta tana kissima dramer da za'ayi gobe
*niko nace su dije an fara 'dan hali ne ko kuma me?* 🤔
****
tunda asuba da dije tayi sallah ta fito falo ta zauna tare da tsintsiya a hannunta da mofa dake cikim bucket da ruwa tana nan zaune dataji kamar motsi saita mike da saur ta fara shara a haka har mamy ta fito shirye cikin shiga ta alfarma da alama fita zatayi
tunda dije ta ji motsi ta mike ta fara shara tanayi tana sharar kwallah kamar wadda aka cewa ubanta ya mutu
mamy ce ta kalleta cike da mamaki ganin yadda kwalla wata ke bin wata tace ke kuma uban me yasameki kike shara kina kuka kamar wadda aka sa dole
banza dije tayi da ita taci gaba da yadda takeyi duk da ta dan soma gajiya
ke ba magana nake miki ba ban son iskanci fa wallahi zan ci ubanki kijini da 'yar iskar yarinya
batare da dije ta dago ba ta ce kema zaifi miki kyau ki fara kuka tun yanzu dan ni na kusa gama nawa
cikin rashin fahimtar maganarta tace ban gane ba
kin kusa mutuwa
mamy shiyasa nake kuka
kijini da 'yar buta...........uba ubanki ne ke kashewa da zaki kalleni kice na kusa mutuwa to a ina kika sani
juya baya dije tayi ta ciro hakoran robar data siyo masu kamar na horo na wasan yara tasa wanda tun jiya taso tsorata mamy dashi da dare amma data samu kudin dataje nema kawai saita fasa ta barta ta huta yau sa gamu
to ko ke mayya ce wallahi kinyi kadan kice zan mutu yau kujini da shegiya kin juya min baya kamar allo juyo ki kalleni ki fadamin mana in daki bakinki sai hakoranki sun zube
jiyowa dije tayi sukayi ido hudu da mamy
wata razananniyar kara mamy tasaki yayin data yadda jakarta ta nufi daki amma ina dije ta cimmata ta rike mata kafa
runtse ido mamy tayi ta shiga ihu iya karfinta yayin da dije tayi saurin cire abin dan ta sami damar yin magana tace ki ciremin hokaran mana ko kin fasa?
*zan yi kokari. yi muku posting kullum.yanzu ku kara hakuri typing akwai wahala wallahi*
*Alqalamin khady* ✍
[3/15, 11:18 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TAME GARI*
NA
khadija usman
3⃣3⃣
innalillahi cewar mamy ta fada da karfinta baseera da taji ihun mamy ta leqo amma ganin dije a tsaye ga mamy ta kure da bango yasa ta fahimci dije ta fara aikinta kamar yadda tace dan haka ta sakada daga gefe tana kallon yadda za'a kwashe
su kuwa su habu driver da me gadi sun jiyo ihu amma basuda tabbacin daga inda ya fito dan haka suka baza kunne dan jin inda zai qara fitowa jin shuru ba'a kuma yi ba yasa suka qara maida hankali ga hirarsu
in banda rawa babu abinda jikin mamy keyi yayin da take ta tuna da mafarkan datake yawan yi akan dije ashe yarinyar dama garken aljanu ne akanta shiyasa ta addabi rayuwar kowa kenan duk irin tsarin datake sha na mayu da aljanu gashi beyi aiki akan wannan yarinyar ba yau abin yazo kanta sam takasa dagowa ta kalli dije
itako dije hakan ne ya qara bata dama ta kara maqe murya ita ala dole jinsin aljanu (niko nace dije ina tausaya miki ranar da dubunki ta cika aka ramfo ki) kince zaki ciremin hakora to ki tashi ki fara aikinki mana dan kin san sai kin nemo katafila wajen babbago shi to kada ki bata shekaru kinayi gara ki fara da wuri zan tausaya miki in rangwanta miki albarkacin kina matsayin uwa ga masoyiyar mu dan haka bari nasa a kawo miki kayan aiki irin namu zasu sauqaqa miki duk da bai zama lallai ki iya daga wasu daga ciki ba amma zan taimaka miki dan cikar burinki
wallahi ni banida wani buri a rayuwata cewar mamy baki na rawa idonta rufe ta hada hannu biyu gaban dije ni da kike ganina tun ina qaramata burina bai wuce inyi aure in haifi yara biyu ba kuma Allah ya cikamin bayan wannan yanzu banida wani kuma
ah ah kinada shi mana
wallahi banida shi
karima kina fa dashi
ranku ya dade dan daga jin muryar nan wlh kunfi dubu dan haka ku yadda banida shi
munce kinada shi kariiimaaaa dije ta fada cikin 'dan daga murya
ai mamy bata san lokacin data tuma a kasa ba tayi rufda ciki ta saki kuka wanda in bata manta ba ko kar tayi karya da saita ce marabinta da kuka tun na amarci 😂amma yau gata tsofai tsofai da ita an sata kuka wayyo ita karima
muryar dije taji tana fadin bama son musu a iya binciken da nayi mun gano kinada manyan buruka a rayuwarki ciki harda korar uwar dakinmu daga gidan nan
ni din banza ni na isa in raba hanta da jini ai khadija tafi kowa cancanta da zama a gidan nan ni duk duniya akwai yarinyar danake so irin ta
karya muka yi miki kenan?
wallahi ko uban ubana bai isa yace kuna qarya ba kuda a halittar ku sam baku san wani abu wai shi karya ba ta yaya zance kuna qarya ai ban isa ba takarasa maganar tana me jan majina da matso hawaye
to tunda kin san haka meyasa kike shiga shirgin daba naki ba mun so mu sauqaqa miki shiyasa muka sa ta koma gidan 'ya'yanki amma kika san yadda kikayi kika dawo da ita nan wannan ma bai isheko ba wato saida kk hana mai gidan biya mata bukatar data tambaya alhalin ke bayi mata zakiyi ba
wallahi yaseen kwarankwasa kinji na rantse ba laifina bane dawowar ta gidan nan wlh sharrin yarana ne dan dama shi habeeb tun yana shan nono na fuskanci baida son mutane shi kuwa naseer tsegumi to yawan tsegumin su yasa nace ta dawo gida kuma kinga abin Allah saiya hadasu da munafukan mata wlh ba yin kaina bane su suka dinga zuga mazan to dama abu ya tadda hali musamman naseer da yusra sarakan munafurci su suka qara iza wutar duk da nasan gaskiya nasan khadija batada fitina to sbd bana son sunanta ya baci shiyasa naje na taho da ita kuma batun Alhaji danace kada ya bata kudi wlh ni nayi niyyar yimata komai da take bukata dan yanzu haka ma can nayi inda zan gwangwajeta da kaya na alfarma inda nake son tafi amaryar ma haduwa da tsari dan kun san khadija ba baya ba wajen kyau sannan ga.......
ya isa haka amma kin makaro dan yanzu haka har su akuyatu wadanda muke cousins da su sun dauki wani abu a jakarki yanzu zasu tafi suyi sadaka da su domin almajiran mu sun cika kofar gidan nan
cikin mamy ne yabada kuuuu wata muguwar gudawa ta taso mata jin wai an kwashi kudi a jakarta za'a rabawa almajiran aljanu wayyo ta shiga uku bata ankare ba ko taji ta jika wandonta da dan karamin zawo
jin dan doyi da dije tayi yasata fadin warin me nakeji haka ta fada tana toshe hancinta
mamy data tabbatar bako tantama zawi tayi yasata fadin wlh inaga jaba ce ko beraye sukayi tusa a store duk da zuciyarta na rawa ta fadi hakan dan tasan sun gama sanin me tayi amma bari tayi karyar kare kai Allah yasa kada su gano