Sashe 25
Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*sai kun dinga hakuri da duk yadda kuka samu duk yadda naso in samu lokaci fiye da haka baya samuwa*
*Alqalamin khady*✍
[3/15, 6:29 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
2⃣4⃣
*har kullum bakina bazai gaji ba haka alkalamina bazai gaza ba wajen nuna godiyata ga daukakin masoya na wlh banida bakin dazan gode muku dashi bisa addu'ar da kukeyimin ina rokon Allah yaqara bani ikon faranta muku Allah yasa ko bayan nagama muku ta me gari kuci gaba da bibbiyata tare da nunamin soyayya fiye da yanzu ina mugu mugun sonku fiye da yadda kuke son ta me gari* 😘
gadan gadan ta nufo dije ita ko sai murmushi takeyi tana tsaye kyam cikin shirin zuwa makaranta
ganin da habeeb yayi dije na dariya tana kuma tsaye tana jiran karasowar sajida babu ko alamun tsoro a tare da ita bare tasa niyyar guduwa hakan yasa yasan akwai abinda ta shirya dan haka cikin daka tsawa yace
keeeee!!!!sajida bana son shashanci me kk shirin yi haka ?
tsayawa tayi cike da jin zafinsa ta juyo tace mataki zan dauka tunda kai ka kasa ta yaya zan zauna qaramar qanwata tana min iskanci wannan wace irin jaraba ce tunda yarinya tazo ta hanani sakewa ni da gidana sannan kai ka zuba mata ido tamkar kana tsoronta to gara na kawo qarshen wannan rashin mutuncin nata wlh nagaji ko ta bar gidan nan ko kuma wlh a fita da ita da ambulance
ido dije ta zaro😳ambulance fa kk ce Aunty na shiga uku kice dukan jinya zakimin to amma bakomai da sauki tunda bana mutuwa bane ko banza na mori zaman jinya dan naga in anje dubiya mutum yana tara abin arziki gashi ko ba komai ka dada samun kulawa gurin dangi dan haka kada ki damu zo ki daki iya yinki har ki gaji amma fa ki lura gurin bugun kada ki dakeni inda zanji zafin da hankalina zai fita in fama miki ciwo naga bai gama sabewa ba ni nama fasa zuwa makarantar zo ki jibgi rabonki yau hau ce ta hauni
rawa zuciyar sajida ta shiga yi jin furucin yarinyar anya kuwa wannan yarinyar ba jinsin shedan bace kai gaskiya da sake lahaulawala quwwata illahbillah Allah ka rabamu da wannan jaraba
shima habeeb a nasa bangaren haka ya shiga zancen zuci duk yadda akayi wannan yarinyar jinsin aljanu ce duba ma da yadda take da kyau ga farinta sak na aljanun sannan ga shegen rashin ji shiyasa ma take ita kadai gun iyayenta dama ance aljanu kishi garesu shiyasa ta hana iyayen haifar jinsin bil adama gashi yanzu ta zo ta addabe su su iyayen nata nacan suna cikin kwanciyar hankali ita kuma tana nan tana gasa su
muryar ta suka tsinkaya tana fadin Aunty tunanin me kk yi kada ma kice na tauye miki haqqinki gurin yin dukan ban barki kinyi yanda ranki ke so ba bari kawai in tube ki zabi inda yayi miki ki daka amma dan Allah ki dan daki gurin nama nama dan kin dai ga yadda nake ba wani naman kirki ne dani ba tana gama fadar haka suka ga ta shiga kokawar cire hijabi tana qoqarin cire jakar bayanta
basu tsinke da lamarin ba sai da sukaga ta shiga kiciniyar daga riga da alamar zata cire
ke meye haka kikeyi bakida hankali ne ya fada a dan hasale
rasss nake yaya kai dai kawai ka tsaya kasha kallo in zaka iya gara kabarta ta huce haushinta amma dan Allah ko da na suma ban samu nasarar ganin yadda aka fita dani aka sani a mota ba ko kuma ganin wanda ya daukeni ba ku taimaka ku dauki hoto ku ajiyemin sannan a sanar da masu zuwa dubiya musamman daga kauye in sun tashi riko abin dubiya su biyo da zabi da kaji kuma danyi kada a yanka ko a soya a kawowa aunty tayimin dahuwar 'yan birni inci in more sannan dan Allah aunty ki lura gurin dukan kada ki taba fuskata ki daki iya jiki sbd kar bakina ya nakasa ya hanani cin abincin daren yau sai dai in sha kunu da safe
*oh su dije jaraba wato magana ta fada musu a fakaice* 😏
ci gaba tayi da kokarin daga rigar wai ita a dole cirewa zatayi wanda inda cirewar gaske ne da tuni ta cire amma yanzu daga ta kama can sai ta kama nan ganin da sajida tayi yarinyar na kokarin yin tsirara gaban mijinta kun santa kuma da kishi haksn yasa bata san lokacin data kama hannunsa ba tajashi sukayi ciki tana ambatar ta shiga uku ba tana shiga dakin tasa key ta zauna gefen gado ta dafe kanta shima din habeeb zaman yayi dukansu aka rasa me magana
itako dije tana ganin yadda sajida tayi ta saki rigarta ta kama dariya tare da daukar jakarta da hijabinta ta nufi waje tana dariya tana fadin waya gaya miki da cirewar zanyi yadda zamani ya koma yanzu maza da mata duk suna iya ma mutum fyade inje ku nakasani ke da mijinki kunga araha yanzu ba gashi na kubuta ba dan wannan me qirar mazan inda ta riqeni wlh baxan sake moruwa ba inaga sai dai na koma kauye a cikin wannan yanayin ta qaraso bakin gate yadda yake tun jiya haka yake wato hakan ya nuna musa be fito ba tun jiya daya shiga kenan sai yanzu ta tuna abinda ya faru nan ma dariyar ta kuma yi taso leqa musa amma sai ta tsinkayi horn din motar makarantar su dan haka da sauri ta fita ta shiga suka wuce
****
ni fa gaskiya bazan iya ba wlh wannan jaraba har ina yarinya kamar 'yar shedan na fuskanci wata rana in tana gidan nan saita sa anzo an dau gawar mu daga Aljanu sai shaidanu duk sun cika mana gida nidai wlh asan yadda za'ayi
tunda ta fara maganar yake kallonta harta gaji tayi shuru
dan jim yayi kafin yace to yanzu ya kk so ayi korarta zanyi ko kuma me?
bance dole ka koreta ba amma ta koma gidan naseer tunda ai ba kai kadai bane dan uwanta
kina ganin komawarta can din shine mafita ? kada fa ki manta gida daya muke kuma ina son ki fuskanci wani abu game da yarinyar na fuskanci duk abinda ta lura mutum baya so to shi tafi yi yanzu kinga ai shi naseer be nuna mata abinda nake nuna mata kamar dana nuna bana son zamanta a nan amma kinga ai nan din ta dawo so inaga mafita daya ce mu lallaba ta har a hankali zansa ta bar gidan amma ki duba fa yadda taketa samu yin accident muna daga gida wuta bazata bi da khadija ba sai dai ruwa ruwan ma na sanyi dan ya zuwa yanzu na fuskanci yarinyar batada hankali
shiru tayi tana nazarin maganar sa zuwa can cikin sanyin murya da marairaicewa tace amma honey ni ba zaman nata ba kaga fa cousins kuke da ita ina jin tsoron kayi mata wani kallo ba matsayin qanwa ba
siririn tsaki yaja tare da fadin kinji matsalarki ai ke kishi yanzu ke ni me zanyi da wannan figigiyar yarinyar kamar kazar mayu wadda inda nayi auren wuri dana haifeta ko ke kanki kin san inda kinyi aure on time da yanzu kinada kamarta dan haka ban son shirmen banza mafita muke nema yanzu bana son shashanci
shikenan zanyi kokarin danne zuciyata amma pls cikin qanqanin lokaci mu san abinyi tabar gidan nan
insha Allah dan na fiki matsuwa da hakan
ah ah wlh nafika
eh to yanzu kam kin fini tunda dubi yadda aka haramta miki sa jambakin safe ba ya qarasa maganar yana kunshe dariya
ganin yadda ta kalli madubi ta bata rai yasa shi matsowa kusa da ita ya fara aikin rarrashi
******
koda dije ta dawo daga makaranta direct part din yusra ta nufa ita kadai ta iske zaune a falo tana kallo harga Allah batayi murnar ganin dije ba duk da zaman kadaicin ya dameta dan me gidan ya fita masallaci ita kuma sajida batada wani sakewar fuska inba gaban mijinta ba nan fa sbd kissa kamar ta hadiyeka amma da zarar an barku ku kadai zata cukule dan haka bata fiya shiga inda take ba yake kawai take yiwa dije bayan ta zauna ta gaisheta
suna a haka dije ta miqe tace bari ta koma part din sajida har bakin kofa yusrah ta rakota ita ko dije abin ma mamaki yake bata ganin yadda inta je guri tace zata tafi ake murnar tafiyarta fiye da murnar zuwanta
koda ta shiga falon da sallama dauke a bakinta ta iske sajida zaune ita da wata mata da yara biyu cikin sakin fuska suka amsa mata su duka
qarasawa tayi harda dan rissinawa ta gaida matar ta amsa mata cike da fara'a nan ta juya ta gaida sajida itama da fara'a a fuskarta ta amsa mata karo na farko kenan a zamanta a gidan
shigewa tayi daki tana zuwa ta cire kagan makaranta ta shiga toilet danyin wanka da alwalawa dan gabatar da sallah
tana shiga Amina ta kalli sajida tace Amarya wannan qanwarki ce halan na ganta kyakkyawa da ita masha Allah ga hankali
murmushi sajida tayi a ranta tace me hankali a gwiwa dai amma a zahiri tace eh qanwata ce tunda qanwar oga ce
kai gaskiya na gaba da hankalinta wlh anan take da zama kenan?
eh sajida ta fada a takaice
suna tsaka da haka dije ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa kanta ko dankwali babu ta qaraso gurinsu tana hamma tare da fadin Aunty wlh yunwa nakeji
kije ga abinci can saman dinning tayi mata nuni da hannu
juyawa dije tayi a ranta tana yaba acting irin na sajida wato dan taga bakuwa shine take nuna kamar ba komai tsakaninsu hmmm to bari itama ta biye mata gara taci ta koshi kafin ta fuskanci qalu balen gaba
*Alqalamin khady*✍
[3/15, 6:29 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
2⃣4⃣
*har kullum bakina bazai gaji ba haka alkalamina bazai gaza ba wajen nuna godiyata ga daukakin masoya na wlh banida bakin dazan gode muku dashi bisa addu'ar da kukeyimin ina rokon Allah yaqara bani ikon faranta muku Allah yasa ko bayan nagama muku ta me gari kuci gaba da bibbiyata tare da nunamin soyayya fiye da yanzu ina mugu mugun sonku fiye da yadda kuke son ta me gari* 😘
gadan gadan ta nufo dije ita ko sai murmushi takeyi tana tsaye kyam cikin shirin zuwa makaranta
ganin da habeeb yayi dije na dariya tana kuma tsaye tana jiran karasowar sajida babu ko alamun tsoro a tare da ita bare tasa niyyar guduwa hakan yasa yasan akwai abinda ta shirya dan haka cikin daka tsawa yace
keeeee!!!!sajida bana son shashanci me kk shirin yi haka ?
tsayawa tayi cike da jin zafinsa ta juyo tace mataki zan dauka tunda kai ka kasa ta yaya zan zauna qaramar qanwata tana min iskanci wannan wace irin jaraba ce tunda yarinya tazo ta hanani sakewa ni da gidana sannan kai ka zuba mata ido tamkar kana tsoronta to gara na kawo qarshen wannan rashin mutuncin nata wlh nagaji ko ta bar gidan nan ko kuma wlh a fita da ita da ambulance
ido dije ta zaro😳ambulance fa kk ce Aunty na shiga uku kice dukan jinya zakimin to amma bakomai da sauki tunda bana mutuwa bane ko banza na mori zaman jinya dan naga in anje dubiya mutum yana tara abin arziki gashi ko ba komai ka dada samun kulawa gurin dangi dan haka kada ki damu zo ki daki iya yinki har ki gaji amma fa ki lura gurin bugun kada ki dakeni inda zanji zafin da hankalina zai fita in fama miki ciwo naga bai gama sabewa ba ni nama fasa zuwa makarantar zo ki jibgi rabonki yau hau ce ta hauni
rawa zuciyar sajida ta shiga yi jin furucin yarinyar anya kuwa wannan yarinyar ba jinsin shedan bace kai gaskiya da sake lahaulawala quwwata illahbillah Allah ka rabamu da wannan jaraba
shima habeeb a nasa bangaren haka ya shiga zancen zuci duk yadda akayi wannan yarinyar jinsin aljanu ce duba ma da yadda take da kyau ga farinta sak na aljanun sannan ga shegen rashin ji shiyasa ma take ita kadai gun iyayenta dama ance aljanu kishi garesu shiyasa ta hana iyayen haifar jinsin bil adama gashi yanzu ta zo ta addabe su su iyayen nata nacan suna cikin kwanciyar hankali ita kuma tana nan tana gasa su
muryar ta suka tsinkaya tana fadin Aunty tunanin me kk yi kada ma kice na tauye miki haqqinki gurin yin dukan ban barki kinyi yanda ranki ke so ba bari kawai in tube ki zabi inda yayi miki ki daka amma dan Allah ki dan daki gurin nama nama dan kin dai ga yadda nake ba wani naman kirki ne dani ba tana gama fadar haka suka ga ta shiga kokawar cire hijabi tana qoqarin cire jakar bayanta
basu tsinke da lamarin ba sai da sukaga ta shiga kiciniyar daga riga da alamar zata cire
ke meye haka kikeyi bakida hankali ne ya fada a dan hasale
rasss nake yaya kai dai kawai ka tsaya kasha kallo in zaka iya gara kabarta ta huce haushinta amma dan Allah ko da na suma ban samu nasarar ganin yadda aka fita dani aka sani a mota ba ko kuma ganin wanda ya daukeni ba ku taimaka ku dauki hoto ku ajiyemin sannan a sanar da masu zuwa dubiya musamman daga kauye in sun tashi riko abin dubiya su biyo da zabi da kaji kuma danyi kada a yanka ko a soya a kawowa aunty tayimin dahuwar 'yan birni inci in more sannan dan Allah aunty ki lura gurin dukan kada ki taba fuskata ki daki iya jiki sbd kar bakina ya nakasa ya hanani cin abincin daren yau sai dai in sha kunu da safe
*oh su dije jaraba wato magana ta fada musu a fakaice* 😏
ci gaba tayi da kokarin daga rigar wai ita a dole cirewa zatayi wanda inda cirewar gaske ne da tuni ta cire amma yanzu daga ta kama can sai ta kama nan ganin da sajida tayi yarinyar na kokarin yin tsirara gaban mijinta kun santa kuma da kishi haksn yasa bata san lokacin data kama hannunsa ba tajashi sukayi ciki tana ambatar ta shiga uku ba tana shiga dakin tasa key ta zauna gefen gado ta dafe kanta shima din habeeb zaman yayi dukansu aka rasa me magana
itako dije tana ganin yadda sajida tayi ta saki rigarta ta kama dariya tare da daukar jakarta da hijabinta ta nufi waje tana dariya tana fadin waya gaya miki da cirewar zanyi yadda zamani ya koma yanzu maza da mata duk suna iya ma mutum fyade inje ku nakasani ke da mijinki kunga araha yanzu ba gashi na kubuta ba dan wannan me qirar mazan inda ta riqeni wlh baxan sake moruwa ba inaga sai dai na koma kauye a cikin wannan yanayin ta qaraso bakin gate yadda yake tun jiya haka yake wato hakan ya nuna musa be fito ba tun jiya daya shiga kenan sai yanzu ta tuna abinda ya faru nan ma dariyar ta kuma yi taso leqa musa amma sai ta tsinkayi horn din motar makarantar su dan haka da sauri ta fita ta shiga suka wuce
****
ni fa gaskiya bazan iya ba wlh wannan jaraba har ina yarinya kamar 'yar shedan na fuskanci wata rana in tana gidan nan saita sa anzo an dau gawar mu daga Aljanu sai shaidanu duk sun cika mana gida nidai wlh asan yadda za'ayi
tunda ta fara maganar yake kallonta harta gaji tayi shuru
dan jim yayi kafin yace to yanzu ya kk so ayi korarta zanyi ko kuma me?
bance dole ka koreta ba amma ta koma gidan naseer tunda ai ba kai kadai bane dan uwanta
kina ganin komawarta can din shine mafita ? kada fa ki manta gida daya muke kuma ina son ki fuskanci wani abu game da yarinyar na fuskanci duk abinda ta lura mutum baya so to shi tafi yi yanzu kinga ai shi naseer be nuna mata abinda nake nuna mata kamar dana nuna bana son zamanta a nan amma kinga ai nan din ta dawo so inaga mafita daya ce mu lallaba ta har a hankali zansa ta bar gidan amma ki duba fa yadda taketa samu yin accident muna daga gida wuta bazata bi da khadija ba sai dai ruwa ruwan ma na sanyi dan ya zuwa yanzu na fuskanci yarinyar batada hankali
shiru tayi tana nazarin maganar sa zuwa can cikin sanyin murya da marairaicewa tace amma honey ni ba zaman nata ba kaga fa cousins kuke da ita ina jin tsoron kayi mata wani kallo ba matsayin qanwa ba
siririn tsaki yaja tare da fadin kinji matsalarki ai ke kishi yanzu ke ni me zanyi da wannan figigiyar yarinyar kamar kazar mayu wadda inda nayi auren wuri dana haifeta ko ke kanki kin san inda kinyi aure on time da yanzu kinada kamarta dan haka ban son shirmen banza mafita muke nema yanzu bana son shashanci
shikenan zanyi kokarin danne zuciyata amma pls cikin qanqanin lokaci mu san abinyi tabar gidan nan
insha Allah dan na fiki matsuwa da hakan
ah ah wlh nafika
eh to yanzu kam kin fini tunda dubi yadda aka haramta miki sa jambakin safe ba ya qarasa maganar yana kunshe dariya
ganin yadda ta kalli madubi ta bata rai yasa shi matsowa kusa da ita ya fara aikin rarrashi
******
koda dije ta dawo daga makaranta direct part din yusra ta nufa ita kadai ta iske zaune a falo tana kallo harga Allah batayi murnar ganin dije ba duk da zaman kadaicin ya dameta dan me gidan ya fita masallaci ita kuma sajida batada wani sakewar fuska inba gaban mijinta ba nan fa sbd kissa kamar ta hadiyeka amma da zarar an barku ku kadai zata cukule dan haka bata fiya shiga inda take ba yake kawai take yiwa dije bayan ta zauna ta gaisheta
suna a haka dije ta miqe tace bari ta koma part din sajida har bakin kofa yusrah ta rakota ita ko dije abin ma mamaki yake bata ganin yadda inta je guri tace zata tafi ake murnar tafiyarta fiye da murnar zuwanta
koda ta shiga falon da sallama dauke a bakinta ta iske sajida zaune ita da wata mata da yara biyu cikin sakin fuska suka amsa mata su duka
qarasawa tayi harda dan rissinawa ta gaida matar ta amsa mata cike da fara'a nan ta juya ta gaida sajida itama da fara'a a fuskarta ta amsa mata karo na farko kenan a zamanta a gidan
shigewa tayi daki tana zuwa ta cire kagan makaranta ta shiga toilet danyin wanka da alwalawa dan gabatar da sallah
tana shiga Amina ta kalli sajida tace Amarya wannan qanwarki ce halan na ganta kyakkyawa da ita masha Allah ga hankali
murmushi sajida tayi a ranta tace me hankali a gwiwa dai amma a zahiri tace eh qanwata ce tunda qanwar oga ce
kai gaskiya na gaba da hankalinta wlh anan take da zama kenan?
eh sajida ta fada a takaice
suna tsaka da haka dije ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa kanta ko dankwali babu ta qaraso gurinsu tana hamma tare da fadin Aunty wlh yunwa nakeji
kije ga abinci can saman dinning tayi mata nuni da hannu
juyawa dije tayi a ranta tana yaba acting irin na sajida wato dan taga bakuwa shine take nuna kamar ba komai tsakaninsu hmmm to bari itama ta biye mata gara taci ta koshi kafin ta fuskanci qalu balen gaba