← Book details Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 59

Sashe 31

Tame Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tattaro dukkan karfinta tayi itama suka kacame aikuwa nan dije ta nuna ita rainon kauye ce dan kuwa tuni ta samu lagon kausar kasancewar ita basu saba da irin wadan nan wahalhalunba da iyakar karfinta dije ta kama nonon kausar ta murde itama karar tayi nan ta shiga neman hanyar kwatar kai amma ina dije dan mugunta harda cije lebe takeyi jin da kausar tayi dije na shirin kasheta kuma ba mafita yasata gartsawa dije cizo a hannu ai kuwa jin zafin cizon yasa dije qara himma bata san lokacin data gwara kan kausar da plasman dake manne jikin t.v stand ba ji kakeyi kwararats ta sheqo kasa ta tsage

nan fa ihu ya hadu biyu ita kanta dijen daba damar kukan ne da tayi dan ta dan sha jiki su kuwa duk sun bude baki suna ihu humaira dataga abinda ya faru da wadanda suka fita tsageranci ai take jikinta ya hau bari dan dama duk burga ce sun fita kwaliti

sai yanzu hankalinta yakai ga bugun kofar da akeyi haggu da dama ma'ana dakin sajida da kuma kofar falon

duk ta rude ta rasa inda zata nufa ga ihun wadan nan na kwancen ita kuma dije tayi mata zuru masifa na cinta jira takeyi tasamu nama kawai

yanayinta ya kara tsorata humaira duk da tabi ta rude aikuwa nan ta fara kokarin guduwa dije ta rufa mata baya
tana fadin ai ba inda zaki dan uwarki yau ko ni ko ku badai kunce sai anyi yakin badar yau a gidan nan ba to sai munga karshen shi muga wakeda nasara nan ta yi cikinta da himma ganin hakan yasa humaira daukar duk wani abu data gani ta jefawa dije ita kuma tana gocewa wani yaje yasamu frame din dake manne a falon sai dai kaji rassss sun sheqo kasa

au to ai sai ki fadamin zakka kk son ku fitar shiyasa zakuyi mana barna a gidan duk da ban san nawa kk fasawa ba yayana ya siya ko ku kuka kawo 'yar uwarku dashi to bari na tayaki nan fa ta nufi dinning duk coolers din dake kai sai da ta dinga saita humaira dasu tana jifanta aikuwa kan kace me falo ya kacame da yayi kaca kaca

cikin zafi humaira tayo cikin dije bisa ga shawarar zuciyarta data bata akan cewa ta ci uban dije kawai yadda take lange langen nan suma su kausar rashin zuciyane yasa haka aikuwa tana zuwa dije tayi mata na 'yan wristelling ta kai mata wani wawan naushi amma fa bada hannunta ba da ludayin miyar da ita kanta humaira bata lura dashi ba ba shiri baki yayi tsartuwa aikuwa nan dije bata bata wata damar kuka ba sbd mugunta duk inda tasan saitin kashi ne saita buga harda goshi duk inda ta buga sai dai kaji yace kwalll ai kuwa saita saki dariya sbd zalunci gwiwar ta saita ta bada kwalll ai kuwa humaira ta bude dukkan muryarta tana ihu tana kiran wayyooo Aunty ki zo ki taimakemu wai bakuda imani ne bamai taimakon mu a hannun kinfi 'yan boko haram rashin imani ta fada tana me qara rushewa da kuka itako dije dariya ta shiga tana fadin muje zuwa mana ai yanzu aka fara ni yaseen ko rabin gajiya ban tashi yiba kawai muci gaba da kaftawa yau nayi muku alqawarin sai kunga kalar mazgar da baku taba gani ba

sajida da hankalinta ke mugun tashe ta kira habeeb yace mata yana kan hanya amma shuru gashi sai ihun 'yan uwanta take jiyowa wanda take addu'ar Allah yasa yarinyar bada mutanenta ta hada su ba suke caskala su dan tasan ita da an tabata sai sun kawo ziyara ita fargabarta ma abin ya tsaya iya wadanda suka jawo kar su ce a gidan zasu kwana yau an taba musu hantar su layin habeeb ta kuma kira nan ya shaida mata gashi nan shida naseer sun kusa zuwa tunawa tayi da spare keys din dake cikin lokarta nan ta shiga dubawa ta dauko na dakinta ta bude amma sai me ? sam takasa fitowa illah ziro kai datayi kadan batare da sun lura ba nan ta hango su kwance sunata wai wai tare da reto da jiki kamar suna takaraa makarantar allo ga dije nan kamar uwarsu tasa sun kama bakinsu da hannunsu amma fuskar nan tasu a kwabe sunata digar hawayen azaba

jin ana buga kofar ne sosai yasa sajida fitowa da kyar ta nufi kofar kamar ta tashi sama dan karma dije ta ankare da ita dan ita masifar yarinyar tsoro yake bata

dije ko tana lura da ita ta shareta dan ita kanta ta matsu a zo a rabata da wadannan kartin banzan a cewarta da bataga amfaninsu ba inda itace kamarsu ai aikin soja zata shiga dan jikinsu kalar wannan aikin ne amma sai gashi taga alama ko aikin office ma ba alamunsa anan

koda ta qarasa ta bude kofar taga ba key jiki dole ba yadda zatayi ta juyo falon kamar tasan yadda akayi nan ta shiga duba kan kujera ko kala batace ba kamar munafuka sim sim ta ganshi ta dauka ta bude kofar su ukune tsaye habeeb naseer da yusrah sai musa dake tsaye daga can bayansu wanda da za'ace arrrr yanzu zai sheka dan ya kudirarwa ransa baxai kuma shiga gidan nan ba matukar yaji ana sautin neman taimako

da sauri suka shigo inda sukayi cirko cirko ganin su mimi zaune suna reto da kawuna ga ciwuka ga falo daya hadu ya hade wadda ita kanta sajida sai yanzu ta lura da barnar da akayi

ya Allah habeeb ya fada kafin ya kalle su cikin bacin rai yace kaii uban mu ya faru haka naganku kamar kunyi Accident dubi yadda kuka mayarmin gida tamkar na mahaukata anya kunada hankali kuwa?

sai yanzu suka farga da shigowar su aikuwa da sauri suka rarrafa suka bude baki cikin kuka kausar tace wlh yaya ku gaggauta fita da wannan yarinyar a gidan nan dan wlh batada hankali wlh bakaken aljanu gareta da alama sannan suna sata hauka wlh yaya zata iya kashe ku wata rana

cikin rawar murya yusra tace to ku wane tsautsayi yakaiku fada da ita kuma ke Aunty sajida ai laifinki ne meyasa baki sanar dasu fada da aljani ba dadi

cikin bacin rai tace su basuda hankali ai daka fara fada ka kalli fuskar wanda kk yi dashi kasani in mutum ne in ma aljani ne kuma nace musu baruwana suka ki ji gashi ban sunjawa kansu ai an zuqe musu jini dan da ganin yadda suke yanzu sai an musu karin jini

to ku meya kaiku taba da transfomer ana ruwan sama ?cewar naseer

wlh kaddara kasan ance me rabon shan duka bayajin kwaba ni babban takai cina na ji yadda aka sauyanin halitta duk da ban kalli madubi ba amma dana shafa goshina wlh naji kamar ma ba fuskata ba dan sai naji kamar ta Dila

wlh in kince dila kinyiwa kanki zabe me kyau bakiga yadda kika koma ba sai kace fukar bahaguwar bakar rakuma cewar naseer daya fada yana kunshe dariyarsa

wayyo ni na shiga uku wayyo Allah yanzu ni dan banida gata babu wanda ya duba yadda nake ba wanda ya saurareni sai 'yan uwanku kuke ta tasu cewar dije data dora hannu aka ta baje baki tana ihu

wadda ihunta yayi dai dai da shigowar mamy wadda tashigo a sukwane jin ihun sakamakon kiranta da yusrah tayi a waya cikin tashin hankali lokacin da basu san abinda ke faruwa ba sai ihu da sukaji..........

*Alqalamin khady* ✍
[3/15, 10:47 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*TA ME GARI*

na
khadija usman

3⃣0⃣

Au wato ma baki daku ba ne shiyasa kk cewa aci gaba cewar kausar data taso nan tayi kan dije ta shiga tillikar ta itama

duk da dije najin zafin dukan iya ji amma taurin zuciya yasa banda dariya babu abinda takeyi ganin hakan yasa su dakatawa suna kallonta tare da mayar da numfashi dan abinka da jinin hutu har sun gaji

itako dije harga Allah jikinta ya amshi duk sakonnin da suka aika mata ganin duk sun gaji sun tsaya yasa tace

badai har kun gaji da yakin sunkurun ba?

au bakinki be mutu ba kenan to bari ki gani in sa nawa hannun muci uwarki a zo a tattara ki a mayar dake kauye a welbarro

ah ah kinga dakata cewar dije naga abin naku zalunci ya shigo ciki abin taron dangi ne ni da gidan dan uwana amma an kafamin kahon zuqa kawai sbd nazo na zauna kamar akan uwar wani nake zaune

ke dan uwarki mu kk zagi ?

nidai bana son sharri bakiji na zageku ba amma in kunce hakan toh nafada din ta qarasa maganar tana murguda baki tare da gyara tsayuwarta ta coge tana yatsina fuska dan wlh fa ta daku a ranta tace shegu a haka kamar basuda kwari a she nama ya ratsasu da dan sauransu gashi suna shirin halakani

ai na fuskanci sai mun dirje bakin yarinyar nan yadda baxata samu bakin rashin kunyar nan ba rufe mana kofa mu lakadi shegiya yadda batada maceci da sauri mimi ta nufi kofa tasa mata key ta zare ta taho dashi a hannunta

kinga kausar rufe Aunty ta waje dan na lura itama bazata barmu muyi yadda muke soba tana iya hanamu maganin wannan shegiyar

dije dake tsaye taga kausar ta nufi dakin sajida saida ta zura kai ta ciki taga sajidar bata nan da alama tana toilet dan taji karar ruwa aikuwa ta zaro key din ta fito dashi ta waje ta rufe ta dawo falon a take zuciyar dije ta shiga lugude a ranta tace kinga dije ko ba komai sarkin yawa yafi sarkin karfi kuma wadannan kitika kitikan da suka koshi da madara gasu nan kamar shanu ki lababa ki tsere to ai kuma sun rufe kofa ya kenan

lura da sukayi dije kamar ta tsorata yasa su kara kaimin nufota tare da narka mata na maguzawa

dakewa dije tayi amma jikinta da zuciyarta kamar sa fado kasa dan rawa ko kafin mimi ta karaso tace mata kinga balama dakata nifa ba koriyar ciyawar da kk saba ci bace naga kin nufoni gadan gadan kina tande baki dabbar mayu
Chapter 31 · 0% Book details