Sashe 9
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har sun kai bakin k'ofa Insp yace " idan ka k'ara shigowa hannunmu kan ka daki wasu ko ka yi fad'a da wasu to zaka yi watanni a kulle," cikin sauri Amir ya juyo ya dawo tare da fad'in yallab'ai kawai in zaka kulle ni ka kulle ni, amma na rantse maka da Allah akan Amira ba wanda zan k'yale, ko kallon banza akai mata to wallahi sai na kai duka, tun yanzu na fad'a maka gaskiyata gwara kawai ka maida ni cikin sel d'in zai fi," yana fad'in haka yana kuma tunkaro inda Insp d'in yake, Amira ce tai sauri ta rik'o hannun Amir d'in sannan ta kalli Insp tace " yallab'ai ka yi hak'uri, insha Allah zamu kiyaye, ta ja hannun Amir d'in suka fice daga station d'in, gida suka wuce kai tsaye fitar da ba'a yita ba kenan a ranar.
Insp kuwa koda suka fita binsu yai da kallo yana huci sannan ya girgiza kai yace " tun ganina da Amir d'innan naji ina zargin shi, kuma itama Amiran yanzu na fara zarginta ban yarda da su ba, kuma daga yau wallahi sai na sa musu ido a kan duk wani motsi nasu, hmmmmm baku san wanene kafi k'arfin mugu ba labarina kawai kuke ji, ba dai shaida kuke nema ba, zan nemota duk inda take."
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
_(Mamie)_
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```
PAGE 40 to 45
Zaune suke kowanne daga cikin su ranshi a b'ace saboda abinda ya faru yau ya b'ata musu shirin su, Amira ta d'ago kai ta kalli Amir tace " Amir kulawarka ta yi yawa a kaina meyasa, gaskiya in kana so mu shirya ka daina yin fad'a da mutane kaina."
Amir ya ji ba dad'i a cikin maganarta ta yanzu, kuma itama ta lura da hakan, ya kalleta yace " kiyi hak'uri ban yi hakan domin b'ata ranki ba, kuma bansan yin hakan zai zama laifi a gareki ba ko abun b'acin rai da ban yi ba, na yi haka ne domin kare ki daga sharrin su, kiyi hak'uri laifina ne da na biyewa umurnin zuciyata na aikata abinda ya zama silar b'acin ranki," yana gama fad'in haka sai ya tashi ya fito daga d'akin, lambun gidan yaje ya zauna tare da kife kanshi yana kuka.
Amira ce ta fito itama ta biyo shi tana neman inda yake, fita k'ofar gida ta yi tana dubawa, se dai ganin motar shi a k'ofar gidan ya tabbatar mata da ba tafiya ya yi ba, to yana ina tambayar da take ta yiwa zuciyarta kenan, nadamar maganganun da ta fad'a mishi take yi domin tasan duk a kanta da kulawar da yake mata ne tasa yai komai, nan ta ji gaba d'aya bata kyauta ba, tunaninta a yanzu kawai kar b'acin ransa ya sa ya jawo ya yi abinda zai cutar da shi, nan da nan itama ta fara hawaye, tana kukan tana waige waige ko zata ganshi can sai tunanin shiga lambu yazo mata, da sauri ta nufi wajen har tana cin tuntub'e.
Tana shiga wajen tun daga nesa ta hango shi, ta k'arasa da sauri har lokacin kuka yake yi ta zauna kusa da shi, sannan ta dafa shi tace " haba Amir meyasa kake yi min asarar hawayenka daga yin wannan maganar."
Amir ya d'ago ya kalleta da idanunsa da suka koma ja, kuma har sun fara kumbura saboda kuka, yace " ba ina yin kuka bane saboda maganar da kika fad'a min a'a, ina yin kuka ne a kan b'ata ranki da na yi, duk duniya idan da akwai abinda ya fi zama tashin hankali a gareni to b'acin ranki ne," yana gama fad'in haka ya koma zai mayar da kanshi ya cigaba da sana'ar tashi, sai ta hanashi komawa ta hanyar rik'e shi.
Amira ta kalle shi sannan tace " ka daina kukan haka to dan Allah bana so, ka yi hak'uri da abinda na fad'a maka, bana so ka sake yin rigima ne shiyasa na fad'a maka haka, amma nima naji zafi a raina lokacin da nake fad'a maka, kuma ni raina bai b'aci ba, koda ya b'aci ko na ji haushi bazan gwada shi a kan wanda yake zama sanadin farin cikina ba a koda yaushe, wanda ke samar da walwalata kuma yake farin cikin kasancewar shi a tare da ni a koda yaushe."
Amir yai murmushin jin dad'in maganarta, Amira ta kalle shi tace " yauwa ko kai fa, ta share mishi hawayen fuskarsa da hannunta ta mik'e sannan ta mik'o mishi hannu tare da fad'in taso mu koma falo, Amir ya kama hannunta tare da mik'ewa suka koma cikin d'aki.
zama suka yi a kujera sannan Amir ya kalleta yace " naga kema kamar kin yi kuka, fad'amun me ya saki kuka?"
Amira tace " yo ba dole in yi kuka ba bansan ina ka shige ba," Amir yai murmushi zuciyar shi na fad'in lallai Amira ta fara damuwa da shi, dama abinda yake so kenan, ta shak'u dashi, ta damu da shi kafin ya kai ga furta mata, cikin ranshi yace lallai lokacin bayyana mata sirrin zuciyata ya kusa.
Amira ta kalle shi tace " me zan dafa maka, dan nima yau sai ka ci irin girki na, " Amir yace "a'a ki bari zan dafa mana kije ki kwanta kawai," Amira cikin ranta tace " dama so nake kace zaka yi shiyasa na fad'i haka saboda kar na nuna maka ina son girkin ka kai min dariya," Amir ya kwashe da dariya yace to ai ko yanzu na ji tunda a fili kika fad'i, inma a zuciya kike tunanin kin fad'i to ya fito fili," ya sake kwashe mata da dariya tare da yi mata gwalo, tab'e fuska tai kamar zata yi kuka, ta biyo shi da gudu sai da suka gama zagaye falon duk abinda ta samu tana wurga mishi duk sun haukata d'akin, sannan daga k'arshe Amir ya shige cikin kicin d'in tare da rufo k'ofar, daga falon Amira na numfarfashin wahala tace zaka fito ka sameni ne ai.
Amir yai murmushi, jin takunta alamar ta juya yasa ya k'arasa ciki ya fara gudanar da aikin da ya shigo da shi ciki, da yake akwai komai a cikin kicin d'in shiyasa sam bai fito ba.
Sai da ya kammala dukkanin abinda yake yi sannan ya fito, gani yai d'akin yai ras ko'ina an gyara shi, ga wani dadda'dan k'amshi da ya cika ko ina murmushi ya yi sannan a fili yace " kamar kin san ina mugun son mace me tsabta gaskiya na dace," bayan ya gama jera abincin ya shiga cikin d'aki domin kiran gimbiyar, se dai tarar da ita ya yi ta yi wankanta ta kwanta tana ta bacci, har ya duk'a zai tashe ta sai ya fasa, ya bar ta sai ta tashi dan kanta.
Makullin motar shi ya d'auka ya fita ya tafi gidan shi, wanka ya yi yai sallah sannan ya sake cakarewa cikin k'ananan kaya, ya sake d'aukar makulli ya fito sai gidan Amira.
Wani katafaren shago ya biya ya siya wani abu wanda ban lura da ko menene ba ya biya aka sa mishi cikin leda ya fito ya shiga motar shi, bai sake tsayawa ko ina ba sai gidan Amira.
Bayan yai fakin ya fito ya shiga ciki, koda ya shiga bai tarar da ita a falo ba, wucewa yai ciki ya tarar da ita har yanzu bacci kawai take sha, bubbuga gadon ya hau yi yana fad'in " malama ki tashi ni fa yunwa nake ji ke nake ta jira."
Amira ta tashi tare da ambaton sunan Allah, ta fad'a ban d'aki ta sake yin wanka sannan ta canza kaya ta fito, a falo ta tarar da Amir ya zuba abincinsa ya fara ci.
Amira ta kalle shi tace " shine baka jira ni na fito ba," Amir yace " kaiiii na jira ki har na gaji baki zo ba."
Amira ta zuba abincin itama ta fara ci, suna ci suna hira har suka gama.
Haka suka cigaba da gudanar da rayuwar su, koda yaushe suna tare, kuma komai tare suke yi, hatta girki tare suke yi, gyaran gidan tare suke yi, cin abinci a tare, hakan ya k'ara musu matsananciyar shak'uwa mai tsanani a tsakanin su, tsakanin Amir da gidansa se dai ya koma da dare ya kwanta gari na wayewa ya sake fitowa sai gidan amira.
Yau ya rage musu saura kwana d'aya tak a koma makaranta hakan yasa suka fara shirin komawa.
Bayan sun koma makaranta Amira taga canji sosai a makarantar su, domin duk wad'anda ta shak'u da su sun gujeta, ko cikinsu taje d'aya bayan d'aya suke guduwa, a tunanin su duk wanda ke tare da ita kashe shi ake yi, a aji ma haka ita da Amir kad'ai suke zama waje d'aya babu wanda yake shiga harkarta da shi kanshi Amir d'in.
Wannan canjin yai matuk'ar d'aga musu hankali daga Amiran har Amir d'in.
A ranar da ta fara ganin wannan canjin bata ma gama lecture ba ta bar makarantar, tana komawa gida taita kuka kamar ranta zai fita.
Amir ya fito daga lecture ya nemi Amira ya rasa, ya kira wayarta amma bata d'aga ba, ba shiri ya figi motarsa sai gidan Amira, ko motar be kashe ba ya fito ba tare da ya rufe murfin motar ba ya shige gidan, zaune ya ganta kan kujera ta kifa kai da gwiwa tana kuka, wata irin doguwar ajiyar zuciya ya saki na jin dad'in ganinta.
Insp kuwa koda suka fita binsu yai da kallo yana huci sannan ya girgiza kai yace " tun ganina da Amir d'innan naji ina zargin shi, kuma itama Amiran yanzu na fara zarginta ban yarda da su ba, kuma daga yau wallahi sai na sa musu ido a kan duk wani motsi nasu, hmmmmm baku san wanene kafi k'arfin mugu ba labarina kawai kuke ji, ba dai shaida kuke nema ba, zan nemota duk inda take."
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
_(Mamie)_
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```
PAGE 40 to 45
Zaune suke kowanne daga cikin su ranshi a b'ace saboda abinda ya faru yau ya b'ata musu shirin su, Amira ta d'ago kai ta kalli Amir tace " Amir kulawarka ta yi yawa a kaina meyasa, gaskiya in kana so mu shirya ka daina yin fad'a da mutane kaina."
Amir ya ji ba dad'i a cikin maganarta ta yanzu, kuma itama ta lura da hakan, ya kalleta yace " kiyi hak'uri ban yi hakan domin b'ata ranki ba, kuma bansan yin hakan zai zama laifi a gareki ba ko abun b'acin rai da ban yi ba, na yi haka ne domin kare ki daga sharrin su, kiyi hak'uri laifina ne da na biyewa umurnin zuciyata na aikata abinda ya zama silar b'acin ranki," yana gama fad'in haka sai ya tashi ya fito daga d'akin, lambun gidan yaje ya zauna tare da kife kanshi yana kuka.
Amira ce ta fito itama ta biyo shi tana neman inda yake, fita k'ofar gida ta yi tana dubawa, se dai ganin motar shi a k'ofar gidan ya tabbatar mata da ba tafiya ya yi ba, to yana ina tambayar da take ta yiwa zuciyarta kenan, nadamar maganganun da ta fad'a mishi take yi domin tasan duk a kanta da kulawar da yake mata ne tasa yai komai, nan ta ji gaba d'aya bata kyauta ba, tunaninta a yanzu kawai kar b'acin ransa ya sa ya jawo ya yi abinda zai cutar da shi, nan da nan itama ta fara hawaye, tana kukan tana waige waige ko zata ganshi can sai tunanin shiga lambu yazo mata, da sauri ta nufi wajen har tana cin tuntub'e.
Tana shiga wajen tun daga nesa ta hango shi, ta k'arasa da sauri har lokacin kuka yake yi ta zauna kusa da shi, sannan ta dafa shi tace " haba Amir meyasa kake yi min asarar hawayenka daga yin wannan maganar."
Amir ya d'ago ya kalleta da idanunsa da suka koma ja, kuma har sun fara kumbura saboda kuka, yace " ba ina yin kuka bane saboda maganar da kika fad'a min a'a, ina yin kuka ne a kan b'ata ranki da na yi, duk duniya idan da akwai abinda ya fi zama tashin hankali a gareni to b'acin ranki ne," yana gama fad'in haka ya koma zai mayar da kanshi ya cigaba da sana'ar tashi, sai ta hanashi komawa ta hanyar rik'e shi.
Amira ta kalle shi sannan tace " ka daina kukan haka to dan Allah bana so, ka yi hak'uri da abinda na fad'a maka, bana so ka sake yin rigima ne shiyasa na fad'a maka haka, amma nima naji zafi a raina lokacin da nake fad'a maka, kuma ni raina bai b'aci ba, koda ya b'aci ko na ji haushi bazan gwada shi a kan wanda yake zama sanadin farin cikina ba a koda yaushe, wanda ke samar da walwalata kuma yake farin cikin kasancewar shi a tare da ni a koda yaushe."
Amir yai murmushin jin dad'in maganarta, Amira ta kalle shi tace " yauwa ko kai fa, ta share mishi hawayen fuskarsa da hannunta ta mik'e sannan ta mik'o mishi hannu tare da fad'in taso mu koma falo, Amir ya kama hannunta tare da mik'ewa suka koma cikin d'aki.
zama suka yi a kujera sannan Amir ya kalleta yace " naga kema kamar kin yi kuka, fad'amun me ya saki kuka?"
Amira tace " yo ba dole in yi kuka ba bansan ina ka shige ba," Amir yai murmushi zuciyar shi na fad'in lallai Amira ta fara damuwa da shi, dama abinda yake so kenan, ta shak'u dashi, ta damu da shi kafin ya kai ga furta mata, cikin ranshi yace lallai lokacin bayyana mata sirrin zuciyata ya kusa.
Amira ta kalle shi tace " me zan dafa maka, dan nima yau sai ka ci irin girki na, " Amir yace "a'a ki bari zan dafa mana kije ki kwanta kawai," Amira cikin ranta tace " dama so nake kace zaka yi shiyasa na fad'i haka saboda kar na nuna maka ina son girkin ka kai min dariya," Amir ya kwashe da dariya yace to ai ko yanzu na ji tunda a fili kika fad'i, inma a zuciya kike tunanin kin fad'i to ya fito fili," ya sake kwashe mata da dariya tare da yi mata gwalo, tab'e fuska tai kamar zata yi kuka, ta biyo shi da gudu sai da suka gama zagaye falon duk abinda ta samu tana wurga mishi duk sun haukata d'akin, sannan daga k'arshe Amir ya shige cikin kicin d'in tare da rufo k'ofar, daga falon Amira na numfarfashin wahala tace zaka fito ka sameni ne ai.
Amir yai murmushi, jin takunta alamar ta juya yasa ya k'arasa ciki ya fara gudanar da aikin da ya shigo da shi ciki, da yake akwai komai a cikin kicin d'in shiyasa sam bai fito ba.
Sai da ya kammala dukkanin abinda yake yi sannan ya fito, gani yai d'akin yai ras ko'ina an gyara shi, ga wani dadda'dan k'amshi da ya cika ko ina murmushi ya yi sannan a fili yace " kamar kin san ina mugun son mace me tsabta gaskiya na dace," bayan ya gama jera abincin ya shiga cikin d'aki domin kiran gimbiyar, se dai tarar da ita ya yi ta yi wankanta ta kwanta tana ta bacci, har ya duk'a zai tashe ta sai ya fasa, ya bar ta sai ta tashi dan kanta.
Makullin motar shi ya d'auka ya fita ya tafi gidan shi, wanka ya yi yai sallah sannan ya sake cakarewa cikin k'ananan kaya, ya sake d'aukar makulli ya fito sai gidan Amira.
Wani katafaren shago ya biya ya siya wani abu wanda ban lura da ko menene ba ya biya aka sa mishi cikin leda ya fito ya shiga motar shi, bai sake tsayawa ko ina ba sai gidan Amira.
Bayan yai fakin ya fito ya shiga ciki, koda ya shiga bai tarar da ita a falo ba, wucewa yai ciki ya tarar da ita har yanzu bacci kawai take sha, bubbuga gadon ya hau yi yana fad'in " malama ki tashi ni fa yunwa nake ji ke nake ta jira."
Amira ta tashi tare da ambaton sunan Allah, ta fad'a ban d'aki ta sake yin wanka sannan ta canza kaya ta fito, a falo ta tarar da Amir ya zuba abincinsa ya fara ci.
Amira ta kalle shi tace " shine baka jira ni na fito ba," Amir yace " kaiiii na jira ki har na gaji baki zo ba."
Amira ta zuba abincin itama ta fara ci, suna ci suna hira har suka gama.
Haka suka cigaba da gudanar da rayuwar su, koda yaushe suna tare, kuma komai tare suke yi, hatta girki tare suke yi, gyaran gidan tare suke yi, cin abinci a tare, hakan ya k'ara musu matsananciyar shak'uwa mai tsanani a tsakanin su, tsakanin Amir da gidansa se dai ya koma da dare ya kwanta gari na wayewa ya sake fitowa sai gidan amira.
Yau ya rage musu saura kwana d'aya tak a koma makaranta hakan yasa suka fara shirin komawa.
Bayan sun koma makaranta Amira taga canji sosai a makarantar su, domin duk wad'anda ta shak'u da su sun gujeta, ko cikinsu taje d'aya bayan d'aya suke guduwa, a tunanin su duk wanda ke tare da ita kashe shi ake yi, a aji ma haka ita da Amir kad'ai suke zama waje d'aya babu wanda yake shiga harkarta da shi kanshi Amir d'in.
Wannan canjin yai matuk'ar d'aga musu hankali daga Amiran har Amir d'in.
A ranar da ta fara ganin wannan canjin bata ma gama lecture ba ta bar makarantar, tana komawa gida taita kuka kamar ranta zai fita.
Amir ya fito daga lecture ya nemi Amira ya rasa, ya kira wayarta amma bata d'aga ba, ba shiri ya figi motarsa sai gidan Amira, ko motar be kashe ba ya fito ba tare da ya rufe murfin motar ba ya shige gidan, zaune ya ganta kan kujera ta kifa kai da gwiwa tana kuka, wata irin doguwar ajiyar zuciya ya saki na jin dad'in ganinta.