Sashe 3
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana k'arasowa ta rik'e k'ugu sannan tace " aboki ya akayi ne, taso muje mu yi wasan tare," Amir yai murmushi sannan yace " a'a kuje kuyi wasanku, bana sha'awar yin komai yau," Amira ta kalle shi sannan tace " na rantse da Allah sai ka yi, ta kama hanunshi tana ja, tashi yayi ya bita, suna tafe tana mita tana fad'in " in zaka sani ka sani tunda Allah ya had'amu kwanakin baya a hanya ka zama abokina, kuma duk wanda ke tare da Amira baya zaman zuru kamar wani marayan da ya rasa kowa, koda yaushe kana zaune ba um ba um-um, ba abinda ka iya sai kallo, a wajen kallo ne kafi auki in ka fara kallona sai kace zaka cinye ni, tun kallonka na tsorata ni har ya fara bani haushi, haba kallo sai kace bak'auye," shi dai ba abinda yace mata banda binta a baya da yake tana rik'e da hannun nashi, kuma bai fasa kallonta ba, in ya kalleta sai ya kalli hannun shi da ta rik'e, juyowa tayi tana kallon shi nan take suka had'a ido tace " ahaf aikin kenan juyowa d'ari ni kake kallo ba canji, to ko maye ne kai sai dai kayi ka gama ka k'yaleni wallahi, dan nama na yafi k'arfinka," ta k'arashe maganar tare da murgud'a mishi baki, Amir yai murmushi, shi har ga Allah tsiwar Amira burgeshi take.
A haka tana mitar ta shi kuma yana dariya tare da cigaba da kallon nata har suka k'araso tsakiyar filin, hakanan dole Amir ya zage suka yi wasan tare su uku, se dai wannan karon da yake babu abun a ranshi ko kuwa kallon Amira ne ya shagaltar da shi oho Amira taita cinye su dukkansu, gwara ma Sadeeq ya ci d'aya, shi kuwa Amir ko d'ayan ma be samu ba.
Amira ce ta samu waje ta zauna tace " gaskiya na gaji tunda dai na ci ku har sau biyar kuma ba wanda yai nasara a kaina to Allah amfana wasa ya tashi hakanan."
Suma zama suka yi kusa da ita suna yi mata dariya, Amir yana gefen damanta, a yayin da Sadeeq shi kuma ke gefen hagunta.
Ruwa me sanyi suka sha, sannan Amira ta had'a komatsanta tace musu zata tafi gida, tai sallama da su ta juya, har ta fara tafiya Sadeeq ya kira sunanta.
Amira ta tsaya cak tare da juyowa, Sadeeq yace " gobe in kin shigo makaranta akwai maganar da nake so mu yi da ke, maganar ta shafemu ni da ke, kuma ta shafi zuciyata," Amira tai shiru tana tunani kodai Sadeeq ne ke turo mata sak'onnin nan, nan da nan zuciyarta ta kwab'eta kai gaskiya ba shi bane, wata zuciyar kuma tace to ki bari mana ki jira kiji me zaice miki goben mana sai ki tabbatar da abinda kike zargi hakanne ko akasin haka, a fili kuwa Amira tace " to me zai hana muyi maganar yanzu?" Sadeeq yace " a'a ki dai bari sai goben in Allah ya kaimu," Amira tace to shikenan Allah ya kaimu," ta juya ta kama hanyar gida, su kuma Sadeeq da Amir da yake Sadeeq da Sani a hostel suke na makarantar, shi kuma Amir ba a hostel yake ba zuwa yake yi ya koma, nan dai suka yi sallama suma kowa ya kama gabanshi.
Bayan Amira ta koma gida tayi wanka tai Alwala tai sallah, sannan ta kwanta bacci, gaf da la'asar ta tashi, tana tashi ta sake shek'a wanka sannan ta canza kaya ta yi sallar asri, (la'asar) bayan ta idar ta zauna kenan ta d'auko wayarta zata kira Dad d'inta da Mum sai ta ji sallama a k'ofar d'akinta.
Amsawa tayi, tare da bada izinin shigowa, wani yaro ne ya shigo hannun shi d'auke da farar takarda.
Mik'a mata wannan wasik'ar ya yi, sannan yace " wani mutumi ne ya bani yace in kawo miki, " Amira ta karb'a sannan tace " yanzu ina mutumin yake?" yaro yace " ya tafi, cewa ma ya yi kar na shigo sai ya sha kwanar layin, sannan sai in shigo in kawo miki," Amira tace " kasan mutumin?" yaro yace a'a banma tab'a ganinshi ba sai yau," Amira tace " shikenan jeka nagode."
Yaron na fita Amira ta bud'e takardar nan ta fara karantawa.
_Amincin Allah ya cigaba da tabbata ga kyakkyawar sarauniyar zuciyata, idan ba zaki damu ba zan so na kasance farin cikin ki a rayuwa, ina sonki so na hak'ik'a, so na gaskiya, so na har abada, zuciyata ta yarda dake, da soyayyarki nake alfahari, kuma a ko'ina nai miki alk'awari idan har kina tare da ni ba zaki tab'a zubar da hawaye ba, soyayyarki itace abun yi cikin dare har zuwa safiya, ke kad'ai ce fatana, tunanina, mafarkina, da walwalata, wallahi ina matuk'ar sonki, idan kika gujeni bazan iya aikata komai ba, ki tausayawa rayuwata ki amince da ni da soyayyata, ina jiran amsarki idan kin rubuta amsar ki ajiye a wajen zamanki cikin aji zan zo in d'auka, kuma ina ganin amsarki zan bayyana gareki, na barki lafiya._
Bayan ta gama karantawa taja doguwar ajiyar zuciya, sannan a fili tace " koma wanene koda ace na ganka ka yimin ina sonka, idan ka shigo hannuna wahalar da zan baka zaka sha mamakinta, Allah ya kaimu goben.
Washe gari da wuri Amira tai shiri ta fita makaranta saboda zumud'in abu biyu, yau ta k'udurta a ranta sai ta gano wanene wannan yake turo mata sak'onni, sai kuma son jin maganar da Sadeeq yace zasu yi da ita.
Tsayawa ta yi ganin cincirindon d'alibai da malamai har da police cikin harabar makarantar tasu, nan da nan gabanta ya fara fad'uwa tana tunanin menene ya faru a makarantar su haka da sassafen nan, hango abokanta su Suhaima da Abdul ne yasa ta tunkari wajen su da sauri, ta yi tambayar duniyar nan su fad'a mata abinda ke faruwa amma abin mamaki sai kuka suke yi, kuma kamar ma ganinta shi ya k'ara sa su yin kukan.
Nan hankalinta ya k'ara tashi, barin wajen su tayi tunda sun k'i yi mata magana, abinda yafi d'aure mata kai shine duk wanda ta tare ta tambayeshi abinda yake faruwa sai su kasa bata amsa se ma kuka ko hawaye da suke k'ara zubarwa, hakan yasa ta tunkari wajen da mutanen suka taru, ta kutsa cikin su har ta samu ta shigo gaba, se dai abinda idanunta suka gani ya yi matuk'ar razanar da ita.
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
_(Mamie)_
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```{Gidan zaman lafiya da amana insha Allah}```
PAGE 15 to 20
Gawar Sadeeq ne a wajen babu alamar rai a tare da shi.
Zaro idanu ta yi tare da kiran sunan shi cikin wata irin razananniyar k'ara, k'arasawa tai kusa da shi, ta tsugunna sannan ta saki wani irin kuka tare da jijjigashi tana fad'in " Sadeeq bana son irin wannan wasan, dan Allah ka tashi," ganin ko motsi baya yi yasa ta tashi ta fita daga wajen duk kallo kuma sai ya koma wajenta suna tayata kokawa rashin da tayi, domin kowa yasan irin muguwar shak'uwar dake tsakanin su da Sadeeq d'in.
Amira ta doshi wajen su Abdul da gudu, tana k'arasawa ta kalli Sani tace " Sani dan Allah fad'amin a mafarki nake ganin komai ko, ai ba gaskiya bane ko?" Sani yai shiru tare da duk'ar da kai yana cigaba da kuka.
Matsawa tai kusa da Abdul ta kalle shi cikin kuka tare da nuna inda gawar take tace " jiya fa muna tare dashi, mun dad'e tare muna wasan gudu yau kuma ace ya mutu," Preety ce tazo ta rik'eta tare da fad'in Amira dan Allah kiyi shiru kar kije kiy sab'o," Amira ta juyo da kallonta gun Preety tace " yace yau zai fad'a min wata magana shine zai mutu kafin ya fad'a min ko," k'arasawa tai wajen Suhaima wadda babu abinda take yi sai kuka kamar ranta zai fita, saboda itama taji mutuwar Sadeeq domin ta dad'e tana k'aunarshi.
Amira ta kalli Suhaima tace " kema kin yarda ya mutu kenan ko, ni wallahi ban yarda ba wasa yake mana kuma zai tashi bari kiga, tashi ta yi ta nufi kan gawar tana jijjiga shi tana fad'in Sadeeq dan Allah ka tashi, kar kai min haka duk duniya banda amini sama da kai ka tashi ta kwanta a jikinshi tare da cigaba da kuka.
Amir wanda shigowar shi kenan cikin makarantar ake fad'a mishi abinda ke faruwa, k'arasawa yai inda gawar take jikin shi a sanyaye ya dafata, d'agowa ta yi, tana ganin Amir ne sai ta mik'e ta fad'a jikinshi tare da cigaba da kuka me ban tausayi, shima hawaye kawai yake ta faman zubarwa, k'ok'arin janta yake su bar cikin taron jama'an ya samu ya maidata gida, se dai luuuuu tayi zata zame daga jikin shi tai k'asa.
Da sauri ya tare ta, sannan aka samo ruwa tana kan jikin shi aka yarfa mata, cikin ikon Allah kuwa ta farfad'o da sunan Sadeeq a bakinta, kuka take yi musu tana fad'in a kaita wajen Sadeeq.
Abdul ne ya kalli Amir yace "gaskiya ya kamata ka kaita gida Amir," 'yan sanda da malaman makarantar ma abinda suka ce kenan a kaita gida.
Hakan kuwa aka yi, ya d'auketa ya saka ta cikin motar ta da tazo da ita suka tafi.
Iyayen Sadeeq ne suka k'araso cike da rud'u, firgici, da tashin hankali, sunyi kuka kamar me, amma ya zasu yi Allah ya basu shi kuma ya karb'i abinsa.
Bayan 'yan sanda sun gama binciken su da suke yi shima likita ya gama aune aunen sa, sannan babban jami'in 'yan sandan ya bawa iyayen Sadeeq umurni kan su tafi da shi ai mishi sallah, kuma insha Allah zasu ji sakamakon bincike akan gawar da suka yi, sannan dole a cikin d'aliban makarantar nan suma akwai yiwuwar a tattauna da su.
Iyayen Sadeeq suka ce ba inda zasu matsa daga nan sai an fad'a musu abinda yai silar mutuwar d'an su.
A haka tana mitar ta shi kuma yana dariya tare da cigaba da kallon nata har suka k'araso tsakiyar filin, hakanan dole Amir ya zage suka yi wasan tare su uku, se dai wannan karon da yake babu abun a ranshi ko kuwa kallon Amira ne ya shagaltar da shi oho Amira taita cinye su dukkansu, gwara ma Sadeeq ya ci d'aya, shi kuwa Amir ko d'ayan ma be samu ba.
Amira ce ta samu waje ta zauna tace " gaskiya na gaji tunda dai na ci ku har sau biyar kuma ba wanda yai nasara a kaina to Allah amfana wasa ya tashi hakanan."
Suma zama suka yi kusa da ita suna yi mata dariya, Amir yana gefen damanta, a yayin da Sadeeq shi kuma ke gefen hagunta.
Ruwa me sanyi suka sha, sannan Amira ta had'a komatsanta tace musu zata tafi gida, tai sallama da su ta juya, har ta fara tafiya Sadeeq ya kira sunanta.
Amira ta tsaya cak tare da juyowa, Sadeeq yace " gobe in kin shigo makaranta akwai maganar da nake so mu yi da ke, maganar ta shafemu ni da ke, kuma ta shafi zuciyata," Amira tai shiru tana tunani kodai Sadeeq ne ke turo mata sak'onnin nan, nan da nan zuciyarta ta kwab'eta kai gaskiya ba shi bane, wata zuciyar kuma tace to ki bari mana ki jira kiji me zaice miki goben mana sai ki tabbatar da abinda kike zargi hakanne ko akasin haka, a fili kuwa Amira tace " to me zai hana muyi maganar yanzu?" Sadeeq yace " a'a ki dai bari sai goben in Allah ya kaimu," Amira tace to shikenan Allah ya kaimu," ta juya ta kama hanyar gida, su kuma Sadeeq da Amir da yake Sadeeq da Sani a hostel suke na makarantar, shi kuma Amir ba a hostel yake ba zuwa yake yi ya koma, nan dai suka yi sallama suma kowa ya kama gabanshi.
Bayan Amira ta koma gida tayi wanka tai Alwala tai sallah, sannan ta kwanta bacci, gaf da la'asar ta tashi, tana tashi ta sake shek'a wanka sannan ta canza kaya ta yi sallar asri, (la'asar) bayan ta idar ta zauna kenan ta d'auko wayarta zata kira Dad d'inta da Mum sai ta ji sallama a k'ofar d'akinta.
Amsawa tayi, tare da bada izinin shigowa, wani yaro ne ya shigo hannun shi d'auke da farar takarda.
Mik'a mata wannan wasik'ar ya yi, sannan yace " wani mutumi ne ya bani yace in kawo miki, " Amira ta karb'a sannan tace " yanzu ina mutumin yake?" yaro yace " ya tafi, cewa ma ya yi kar na shigo sai ya sha kwanar layin, sannan sai in shigo in kawo miki," Amira tace " kasan mutumin?" yaro yace a'a banma tab'a ganinshi ba sai yau," Amira tace " shikenan jeka nagode."
Yaron na fita Amira ta bud'e takardar nan ta fara karantawa.
_Amincin Allah ya cigaba da tabbata ga kyakkyawar sarauniyar zuciyata, idan ba zaki damu ba zan so na kasance farin cikin ki a rayuwa, ina sonki so na hak'ik'a, so na gaskiya, so na har abada, zuciyata ta yarda dake, da soyayyarki nake alfahari, kuma a ko'ina nai miki alk'awari idan har kina tare da ni ba zaki tab'a zubar da hawaye ba, soyayyarki itace abun yi cikin dare har zuwa safiya, ke kad'ai ce fatana, tunanina, mafarkina, da walwalata, wallahi ina matuk'ar sonki, idan kika gujeni bazan iya aikata komai ba, ki tausayawa rayuwata ki amince da ni da soyayyata, ina jiran amsarki idan kin rubuta amsar ki ajiye a wajen zamanki cikin aji zan zo in d'auka, kuma ina ganin amsarki zan bayyana gareki, na barki lafiya._
Bayan ta gama karantawa taja doguwar ajiyar zuciya, sannan a fili tace " koma wanene koda ace na ganka ka yimin ina sonka, idan ka shigo hannuna wahalar da zan baka zaka sha mamakinta, Allah ya kaimu goben.
Washe gari da wuri Amira tai shiri ta fita makaranta saboda zumud'in abu biyu, yau ta k'udurta a ranta sai ta gano wanene wannan yake turo mata sak'onni, sai kuma son jin maganar da Sadeeq yace zasu yi da ita.
Tsayawa ta yi ganin cincirindon d'alibai da malamai har da police cikin harabar makarantar tasu, nan da nan gabanta ya fara fad'uwa tana tunanin menene ya faru a makarantar su haka da sassafen nan, hango abokanta su Suhaima da Abdul ne yasa ta tunkari wajen su da sauri, ta yi tambayar duniyar nan su fad'a mata abinda ke faruwa amma abin mamaki sai kuka suke yi, kuma kamar ma ganinta shi ya k'ara sa su yin kukan.
Nan hankalinta ya k'ara tashi, barin wajen su tayi tunda sun k'i yi mata magana, abinda yafi d'aure mata kai shine duk wanda ta tare ta tambayeshi abinda yake faruwa sai su kasa bata amsa se ma kuka ko hawaye da suke k'ara zubarwa, hakan yasa ta tunkari wajen da mutanen suka taru, ta kutsa cikin su har ta samu ta shigo gaba, se dai abinda idanunta suka gani ya yi matuk'ar razanar da ita.
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
_(Mamie)_
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```{Gidan zaman lafiya da amana insha Allah}```
PAGE 15 to 20
Gawar Sadeeq ne a wajen babu alamar rai a tare da shi.
Zaro idanu ta yi tare da kiran sunan shi cikin wata irin razananniyar k'ara, k'arasawa tai kusa da shi, ta tsugunna sannan ta saki wani irin kuka tare da jijjigashi tana fad'in " Sadeeq bana son irin wannan wasan, dan Allah ka tashi," ganin ko motsi baya yi yasa ta tashi ta fita daga wajen duk kallo kuma sai ya koma wajenta suna tayata kokawa rashin da tayi, domin kowa yasan irin muguwar shak'uwar dake tsakanin su da Sadeeq d'in.
Amira ta doshi wajen su Abdul da gudu, tana k'arasawa ta kalli Sani tace " Sani dan Allah fad'amin a mafarki nake ganin komai ko, ai ba gaskiya bane ko?" Sani yai shiru tare da duk'ar da kai yana cigaba da kuka.
Matsawa tai kusa da Abdul ta kalle shi cikin kuka tare da nuna inda gawar take tace " jiya fa muna tare dashi, mun dad'e tare muna wasan gudu yau kuma ace ya mutu," Preety ce tazo ta rik'eta tare da fad'in Amira dan Allah kiyi shiru kar kije kiy sab'o," Amira ta juyo da kallonta gun Preety tace " yace yau zai fad'a min wata magana shine zai mutu kafin ya fad'a min ko," k'arasawa tai wajen Suhaima wadda babu abinda take yi sai kuka kamar ranta zai fita, saboda itama taji mutuwar Sadeeq domin ta dad'e tana k'aunarshi.
Amira ta kalli Suhaima tace " kema kin yarda ya mutu kenan ko, ni wallahi ban yarda ba wasa yake mana kuma zai tashi bari kiga, tashi ta yi ta nufi kan gawar tana jijjiga shi tana fad'in Sadeeq dan Allah ka tashi, kar kai min haka duk duniya banda amini sama da kai ka tashi ta kwanta a jikinshi tare da cigaba da kuka.
Amir wanda shigowar shi kenan cikin makarantar ake fad'a mishi abinda ke faruwa, k'arasawa yai inda gawar take jikin shi a sanyaye ya dafata, d'agowa ta yi, tana ganin Amir ne sai ta mik'e ta fad'a jikinshi tare da cigaba da kuka me ban tausayi, shima hawaye kawai yake ta faman zubarwa, k'ok'arin janta yake su bar cikin taron jama'an ya samu ya maidata gida, se dai luuuuu tayi zata zame daga jikin shi tai k'asa.
Da sauri ya tare ta, sannan aka samo ruwa tana kan jikin shi aka yarfa mata, cikin ikon Allah kuwa ta farfad'o da sunan Sadeeq a bakinta, kuka take yi musu tana fad'in a kaita wajen Sadeeq.
Abdul ne ya kalli Amir yace "gaskiya ya kamata ka kaita gida Amir," 'yan sanda da malaman makarantar ma abinda suka ce kenan a kaita gida.
Hakan kuwa aka yi, ya d'auketa ya saka ta cikin motar ta da tazo da ita suka tafi.
Iyayen Sadeeq ne suka k'araso cike da rud'u, firgici, da tashin hankali, sunyi kuka kamar me, amma ya zasu yi Allah ya basu shi kuma ya karb'i abinsa.
Bayan 'yan sanda sun gama binciken su da suke yi shima likita ya gama aune aunen sa, sannan babban jami'in 'yan sandan ya bawa iyayen Sadeeq umurni kan su tafi da shi ai mishi sallah, kuma insha Allah zasu ji sakamakon bincike akan gawar da suka yi, sannan dole a cikin d'aliban makarantar nan suma akwai yiwuwar a tattauna da su.
Iyayen Sadeeq suka ce ba inda zasu matsa daga nan sai an fad'a musu abinda yai silar mutuwar d'an su.