Sashe 39
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amira da Nura sun dad'e suna hira kuma ba hirar kowa suke ba illah ta Amir, labari take ta bashi tun farkon had'uwarsu har zuwa yanzu, bayan ta gama bashi tace "a halin da ake ciki a yanzu rasashi da nayi ji nake kamar na rasa wani b'angare ne na jikina, kuma zuciyata na bani cewa nima ina gaf da binshi," Nura ya kalleta harda guntun hawayenshi irin na tausayi, yace "gaskiya na tausaya muku, kuma duk duniya babu inda na tab'a jin labarin cikakkun masoya irinku, nima ina ji a jikina kamar yanda kike ji har yanzu Amir na raye be mutu ba, zan tayaki Addu'a Allah ya bayyana miki shi, amma ina fatan zaki d'aukeni a matsayin aboki kuma d'an uwa sannan abokin shawararki?"
Amira ta numfasa sannan tace "ba damuwa, Nura yaji dad'i sosai, yai mata godiya, suna cikin magana sai ga su Dad sun fito, sunji dad'in yanda suka gansu, ga dukkan alamu abinda suka 'kudurta zai tabbata nan bada dad'ewa ba.
Nan suka yi sallama da Amira Dad ya bisu a motarsu domin rakasu har inda sukace zasu biya domin duba wani, suna cikin tafiya kamar ance Dad ya kalli gefen ti-ti ya hango wani yaro sak Amir cikin farar shadda ga sojoji da 'yan sanda da kuma masu ba'ka'ken kaya duk sun kewaye shi, cikin zaro idanu tare da jin fad'uwar gaba matsananci ya 'kwala mishi kira yace "Amir," cikin sauri kuwa Amir ya waigo amma be hango wanda ya kira sunanshi ba saboda motarsu ta riga da ta wuce, tunani ya shiga yi anya Amir ne kuwa, Amir fa'kiri ne baida komai, amma in ba shi bane meyasa ya waigo lokacin da na kira sunansa.
Haladu ya kalli Dad yace "lafiya ya naga yanayinka ya canza, wancan waye shi d'in?" Dad yace "shine annobar da ya rusamin farin cikin gidana gabad'aya ban tab'a tsammanin yana raye ba," Haladu yace in kuwa hakane to tabbas yana da kyau kayi gaggawar canza gari dan kuwa tunda har yana raye bazai tab'a barin Amira ba, wa ya sani ma ko d'an shan jini ne yarinya duk tabi ta 'karmashe ta lalace."
Babu abinda Dad ya 'kara cewa, har ya rakasu inda zasu sauka sukayi sallama ya juyo shi da masu tsaronsa, a hanyarsa ta dawowa ma saida ya sake duba wajen amma sedai kash baya nan, da wannan tunanin suka 'karasa gida tare da yanke shawarar cikin satin nan zai koma kano shi da iyalansa da zama.
Bayan tafiyar Dad Haladu ya kalli yaronsa Nura yace "my son ya kukayi da yarinyar ina fatan kun daidaita kanku?" Nura yace "Dad akwai matsala gaskiya, shawo kanta ta soni zaiyi matuk'ar wahala saboda akwai wanda ta ajiye a ranta kuma take zaman jira, Haladu yace "haba my son kaifa namiji ne kuma jajirtacce akan komai, meyasa zakai saurin karaya akan haka."
Nura yace "ba damuwa nasan yanda zanyi na shawo kanta ayi auren, amma na tabbatar ba zata soni ba."
Haladu yace "ai dama burinmu kenan ayi auren d'an baba," Nura yace "but Dad ni ina sonta fa, ba fatana muyi aure mu rabu ba," Haladu yai murmushi, sannan ya dafa kafad'ar Nura yace "kai yarone Nura, ba zaka gane komai ba sai nan gaba, kaidai yi 'ko'kari ka shawo kanta ayi auren.
…………………………………
*BAYAN SATI 'DAYA*
Abba ne zaune a falo matarsa na gasa mishi 'kafa da kuma goshinsa da yaji rauni.
Amir ne ya fad'o gidan a guje yana runtumawa mahaifinsa kira, ya 'karaso kusa dashi ya zube a 'kasa yana kuka yace "Abba kaga irinta ko, taya za'ai ace kana shugaban 'kasa kace baka son masu tsaro, kuma bayan kasan ba zaka rasa ma'kiya ba da 'yan adawa, yanzu gashi nan ana neman ranka, Abba ko so kake mu rasaka?"
Abba yai murmushi sannan yace "haba Amir kwantar da hankalinka mana, bafa su sami galaba a kaina ba, wad'annan raunikan da na ji duk wajen ceton raina ne ba su suka jimin ba, kayi shiru ka daina kuka Allah ya kub'utar dani daga sharrinsu, kuma a baya ma na shiga had'arurrukan da suka fi wad'annan."
Amir yace "gaskiya Dad in har kana son farin cikinmu to karka 'kara fita kai kad'ai, dan ni wallahi a kanka na fara jin shugaban 'kasa yace wai baya son masu tsaronshi na binshi a baya duk inda zai tafi, dan haka dan Allah Dad ka janye wannan ra'ayin naka, kaga ka sakamu kuka ni da Umma ka gani ko tunda na shigo naga tana ta faman kuka."
Abba Ahmad ya kalli Umma ya yafitota da hannu, cikin sauri kuwa ta rarrafo zuwa gareshi ya rungumeta da hannunshi na dama, sannan ya yafito Amir shima da hannu yai mishi kamar yanda yaiwa Umma da d'ayan hannun, sannan ya kallesu duka yace "ku kwantar da hankalinku, in dai akan wannan ne kuke kuka to bakwa 'kara zubar da hawayenku a karo na biyu domin kuwa na amince da bu'katarku dan haka ku share hawayenku," Amir ya sharewa Ummansa, itama ta share mishi, sannan suka sharewa Abba shima wanda yake kukan farin cikin samun iyali nagartattu.
Amir ya mi'ke tsaye sannan ya ajiye wayarshi yace bari yaje ya watsa ruwa ya fito, Amir na shiga ya cire kayanshi sannan ya d'aura tawul ya shiga wanka, bayan ya fito ya shirya tsaf agogo ne kad'ai bai d'aura ba, sai ya shiga duba agogon da zai shiga da kayansa, laluben shi ya kaishi har kan wata drower wadda tunda ya shigo d'akin be tab'a bi ta kanta ba, yana bud'ewa yaga hotuna birjik na yara ne guda biyu, d'aya yaro ne sosai dan bazai wuce shekara d'aya da wata uku ba, d'ayan kuma wani yaron ne a kusa dashi d'an shekara biyar, da yaron nan dan shekara d'aya da rabi da yaron nan d'an shekara biyar kamarsu har ta b'aci, banda d'aya ya girmi d'aya da cewa za'ai 'yan biyu ne su.
Abinda ya d'aurewa Amir kai shine yaron nan d'an shekara biyar kamarsu d'aya sak da Amir, sedai yasan tabbas ba shi bane wannan, to ina su Umma suka samo yaro mai kama dashi, kodai shine wanda ya b'ace suke nema, kardai ace su Umma iyayena ne? hotunan ya d'iba da sauri tare da yin falo domin samo tarin amsoshin dake ranshi.
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*INA BU'KATAR ADDU'A DAGA GAREKU MASOYANA ALLAH YA BANI LAFIYA 'DORARRA*👏👏👏👏👏
PAGE 165 to 170
Amir ya fito daga d'akinshi cikin sauri tare da nufo iyayensa hannunshi ri'ke da hotunan da ya gani.
Zama yai kusa da Abbanshi sannan ya nuna mishi hotunan yace "Abba su waye wad'annan?" Abba Ahmad ya gyara zama tare da karb'ar hotunan yana kalla yace "yarana ne wad'anda na rasa, ya nuna mishi babban yace wannan shine Ammar, d'ayan kuma wato 'karamin sunanshi Bilal, shine wanda ya b'ata, babban kuma ya mutu ne."
Amir kuka yake sosai yana kallonsu, daga Ahamd har Khadija sunji tsoron halin da Amir ya shiga cikin 'kan'kanin lokaci daga tambayar hoto, nan suka shiga rarrashinsa domin yai shiru suji dalilin yin kukansa.
Amir ta kallesu yace "indai hotunan nan da na gani hoton 'ya'yanku ne to tabbas nine d'anku wanda ya b'ata nine d'anku wanda kuka dad'e kuna nema."
Amir ya d'auko wayarsa ya nuna mishi hotunansa lokacin yana 'karami da wanda ya d'auka shi kad'ai da wanda suka d'auka tare da Amira, bayan ya nuna musu na cikin waya sai ya shiga d'aki jikinsa na rawa ya kwaso mishi duk hotunan da ya nuna mishi a waya ya nuna musu a zahiri, Khadija ce ta mi'ke tsaye cikin sauri ta fizge hoton dake hannun Amir ta duba, haba kawai sai ga Khadija a 'kasa anyi suman farin ciki ne zamuce ko na firgicin ganin abinda bata yi tsammani ba.
Cikin hanzari suka watsa mata ruwan sanyi ta dawo hayyacinta amma har yanzu kuka take, ta rungume Amir gam kamar wadda za'a sake rabata dashi tana cigaba da kuka tare da godewa Allah da 'karfinta, Abba kanshi da yake namiji saida yai kukan farin ciki, Amir yace "Abba ashe dama kune iyayena ban sani ba Allah ya fad'o dani hannunku," Abba ya kalleshi yace "dama mu jinka muke kamar d'anda muka haifa tun ranar da muka fara ganinka," Amir yace "ina godewa Allah mahalicci da ya bayyanamin ku, kuma ya zab'amin ku a matsayin iyayena."
Umma kuwa ta kasa cewa komai banda kallonshi da take yi tare da cigaba da zubar da hawaye, fuskarta kuwa tana d'auke da farin ciki mara misaltuwa, Amir ya kalleta yace "Ummana bakice komai ba," Umma tace "Allah na gode maka da ka dawo da yarona gareni na sake ganinshi kafin ka d'auki raina," tana gama fad'in haka ta sake saka kuka me had'e da dariya, a ranar dai sai suka koma kamar zararru saboda tsabar farin cikin ganin yaron da suka rabu dashi tun yana 'karami, tun bashida wayau.
Bayan sun gama koke kokensu da murnar had'uwa da juna sai Amir ya kalli mahaifinshi yace Abba me ya faru har na b'ace daga gareku, kuma ina d'an'uwana Ammar?"
Abba yai shiru na wasu lokuta, sannan ya numfasa yace "My Son bana son tuno dukkanin abubuwan da suka wuce a baya, amma ya zama wajibi in fad'a maka komai, Abba ya sake numfasawa, sannan ya cigaba da fad'in "labarina ni da mahaifiyarka labari ne me tsawo, amma zan gajarta maka shi in baka shi a ta'kaice."
Amir yace "to Abba fara bani labarin ina saurarenka," Abba ya gyara zama sannan yace.
Amira ta numfasa sannan tace "ba damuwa, Nura yaji dad'i sosai, yai mata godiya, suna cikin magana sai ga su Dad sun fito, sunji dad'in yanda suka gansu, ga dukkan alamu abinda suka 'kudurta zai tabbata nan bada dad'ewa ba.
Nan suka yi sallama da Amira Dad ya bisu a motarsu domin rakasu har inda sukace zasu biya domin duba wani, suna cikin tafiya kamar ance Dad ya kalli gefen ti-ti ya hango wani yaro sak Amir cikin farar shadda ga sojoji da 'yan sanda da kuma masu ba'ka'ken kaya duk sun kewaye shi, cikin zaro idanu tare da jin fad'uwar gaba matsananci ya 'kwala mishi kira yace "Amir," cikin sauri kuwa Amir ya waigo amma be hango wanda ya kira sunanshi ba saboda motarsu ta riga da ta wuce, tunani ya shiga yi anya Amir ne kuwa, Amir fa'kiri ne baida komai, amma in ba shi bane meyasa ya waigo lokacin da na kira sunansa.
Haladu ya kalli Dad yace "lafiya ya naga yanayinka ya canza, wancan waye shi d'in?" Dad yace "shine annobar da ya rusamin farin cikin gidana gabad'aya ban tab'a tsammanin yana raye ba," Haladu yace in kuwa hakane to tabbas yana da kyau kayi gaggawar canza gari dan kuwa tunda har yana raye bazai tab'a barin Amira ba, wa ya sani ma ko d'an shan jini ne yarinya duk tabi ta 'karmashe ta lalace."
Babu abinda Dad ya 'kara cewa, har ya rakasu inda zasu sauka sukayi sallama ya juyo shi da masu tsaronsa, a hanyarsa ta dawowa ma saida ya sake duba wajen amma sedai kash baya nan, da wannan tunanin suka 'karasa gida tare da yanke shawarar cikin satin nan zai koma kano shi da iyalansa da zama.
Bayan tafiyar Dad Haladu ya kalli yaronsa Nura yace "my son ya kukayi da yarinyar ina fatan kun daidaita kanku?" Nura yace "Dad akwai matsala gaskiya, shawo kanta ta soni zaiyi matuk'ar wahala saboda akwai wanda ta ajiye a ranta kuma take zaman jira, Haladu yace "haba my son kaifa namiji ne kuma jajirtacce akan komai, meyasa zakai saurin karaya akan haka."
Nura yace "ba damuwa nasan yanda zanyi na shawo kanta ayi auren, amma na tabbatar ba zata soni ba."
Haladu yace "ai dama burinmu kenan ayi auren d'an baba," Nura yace "but Dad ni ina sonta fa, ba fatana muyi aure mu rabu ba," Haladu yai murmushi, sannan ya dafa kafad'ar Nura yace "kai yarone Nura, ba zaka gane komai ba sai nan gaba, kaidai yi 'ko'kari ka shawo kanta ayi auren.
…………………………………
*BAYAN SATI 'DAYA*
Abba ne zaune a falo matarsa na gasa mishi 'kafa da kuma goshinsa da yaji rauni.
Amir ne ya fad'o gidan a guje yana runtumawa mahaifinsa kira, ya 'karaso kusa dashi ya zube a 'kasa yana kuka yace "Abba kaga irinta ko, taya za'ai ace kana shugaban 'kasa kace baka son masu tsaro, kuma bayan kasan ba zaka rasa ma'kiya ba da 'yan adawa, yanzu gashi nan ana neman ranka, Abba ko so kake mu rasaka?"
Abba yai murmushi sannan yace "haba Amir kwantar da hankalinka mana, bafa su sami galaba a kaina ba, wad'annan raunikan da na ji duk wajen ceton raina ne ba su suka jimin ba, kayi shiru ka daina kuka Allah ya kub'utar dani daga sharrinsu, kuma a baya ma na shiga had'arurrukan da suka fi wad'annan."
Amir yace "gaskiya Dad in har kana son farin cikinmu to karka 'kara fita kai kad'ai, dan ni wallahi a kanka na fara jin shugaban 'kasa yace wai baya son masu tsaronshi na binshi a baya duk inda zai tafi, dan haka dan Allah Dad ka janye wannan ra'ayin naka, kaga ka sakamu kuka ni da Umma ka gani ko tunda na shigo naga tana ta faman kuka."
Abba Ahmad ya kalli Umma ya yafitota da hannu, cikin sauri kuwa ta rarrafo zuwa gareshi ya rungumeta da hannunshi na dama, sannan ya yafito Amir shima da hannu yai mishi kamar yanda yaiwa Umma da d'ayan hannun, sannan ya kallesu duka yace "ku kwantar da hankalinku, in dai akan wannan ne kuke kuka to bakwa 'kara zubar da hawayenku a karo na biyu domin kuwa na amince da bu'katarku dan haka ku share hawayenku," Amir ya sharewa Ummansa, itama ta share mishi, sannan suka sharewa Abba shima wanda yake kukan farin cikin samun iyali nagartattu.
Amir ya mi'ke tsaye sannan ya ajiye wayarshi yace bari yaje ya watsa ruwa ya fito, Amir na shiga ya cire kayanshi sannan ya d'aura tawul ya shiga wanka, bayan ya fito ya shirya tsaf agogo ne kad'ai bai d'aura ba, sai ya shiga duba agogon da zai shiga da kayansa, laluben shi ya kaishi har kan wata drower wadda tunda ya shigo d'akin be tab'a bi ta kanta ba, yana bud'ewa yaga hotuna birjik na yara ne guda biyu, d'aya yaro ne sosai dan bazai wuce shekara d'aya da wata uku ba, d'ayan kuma wani yaron ne a kusa dashi d'an shekara biyar, da yaron nan dan shekara d'aya da rabi da yaron nan d'an shekara biyar kamarsu har ta b'aci, banda d'aya ya girmi d'aya da cewa za'ai 'yan biyu ne su.
Abinda ya d'aurewa Amir kai shine yaron nan d'an shekara biyar kamarsu d'aya sak da Amir, sedai yasan tabbas ba shi bane wannan, to ina su Umma suka samo yaro mai kama dashi, kodai shine wanda ya b'ace suke nema, kardai ace su Umma iyayena ne? hotunan ya d'iba da sauri tare da yin falo domin samo tarin amsoshin dake ranshi.
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*INA BU'KATAR ADDU'A DAGA GAREKU MASOYANA ALLAH YA BANI LAFIYA 'DORARRA*👏👏👏👏👏
PAGE 165 to 170
Amir ya fito daga d'akinshi cikin sauri tare da nufo iyayensa hannunshi ri'ke da hotunan da ya gani.
Zama yai kusa da Abbanshi sannan ya nuna mishi hotunan yace "Abba su waye wad'annan?" Abba Ahmad ya gyara zama tare da karb'ar hotunan yana kalla yace "yarana ne wad'anda na rasa, ya nuna mishi babban yace wannan shine Ammar, d'ayan kuma wato 'karamin sunanshi Bilal, shine wanda ya b'ata, babban kuma ya mutu ne."
Amir kuka yake sosai yana kallonsu, daga Ahamd har Khadija sunji tsoron halin da Amir ya shiga cikin 'kan'kanin lokaci daga tambayar hoto, nan suka shiga rarrashinsa domin yai shiru suji dalilin yin kukansa.
Amir ta kallesu yace "indai hotunan nan da na gani hoton 'ya'yanku ne to tabbas nine d'anku wanda ya b'ata nine d'anku wanda kuka dad'e kuna nema."
Amir ya d'auko wayarsa ya nuna mishi hotunansa lokacin yana 'karami da wanda ya d'auka shi kad'ai da wanda suka d'auka tare da Amira, bayan ya nuna musu na cikin waya sai ya shiga d'aki jikinsa na rawa ya kwaso mishi duk hotunan da ya nuna mishi a waya ya nuna musu a zahiri, Khadija ce ta mi'ke tsaye cikin sauri ta fizge hoton dake hannun Amir ta duba, haba kawai sai ga Khadija a 'kasa anyi suman farin ciki ne zamuce ko na firgicin ganin abinda bata yi tsammani ba.
Cikin hanzari suka watsa mata ruwan sanyi ta dawo hayyacinta amma har yanzu kuka take, ta rungume Amir gam kamar wadda za'a sake rabata dashi tana cigaba da kuka tare da godewa Allah da 'karfinta, Abba kanshi da yake namiji saida yai kukan farin ciki, Amir yace "Abba ashe dama kune iyayena ban sani ba Allah ya fad'o dani hannunku," Abba ya kalleshi yace "dama mu jinka muke kamar d'anda muka haifa tun ranar da muka fara ganinka," Amir yace "ina godewa Allah mahalicci da ya bayyanamin ku, kuma ya zab'amin ku a matsayin iyayena."
Umma kuwa ta kasa cewa komai banda kallonshi da take yi tare da cigaba da zubar da hawaye, fuskarta kuwa tana d'auke da farin ciki mara misaltuwa, Amir ya kalleta yace "Ummana bakice komai ba," Umma tace "Allah na gode maka da ka dawo da yarona gareni na sake ganinshi kafin ka d'auki raina," tana gama fad'in haka ta sake saka kuka me had'e da dariya, a ranar dai sai suka koma kamar zararru saboda tsabar farin cikin ganin yaron da suka rabu dashi tun yana 'karami, tun bashida wayau.
Bayan sun gama koke kokensu da murnar had'uwa da juna sai Amir ya kalli mahaifinshi yace Abba me ya faru har na b'ace daga gareku, kuma ina d'an'uwana Ammar?"
Abba yai shiru na wasu lokuta, sannan ya numfasa yace "My Son bana son tuno dukkanin abubuwan da suka wuce a baya, amma ya zama wajibi in fad'a maka komai, Abba ya sake numfasawa, sannan ya cigaba da fad'in "labarina ni da mahaifiyarka labari ne me tsawo, amma zan gajarta maka shi in baka shi a ta'kaice."
Amir yace "to Abba fara bani labarin ina saurarenka," Abba ya gyara zama sannan yace.