Sashe 32
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amir yai murmushi tare da karb'ar takardar, sannan yace "ba damuwa Allah ya kaimu ranar," Insp Yahya ya dafa kafad'ar Amir, sannan yace "karfa ka ji haushina domin wannan karon ba ni na shigar da 'karar ba, me gayya me aiki ne shugaban 'kasa wato uban yarinyar da ka sace," har ya juya sai yaji Amir yai dariya, dariyar ta sakashi juyowa domin yaga me yake wa dariyar, Amir ya kalleshi yace "in kana tunanin ina tare da damuwa to wallahi ka daina, domin ni a shirye nake da ko ina za'aje domin yin wannan case d'in na dad'e da shiryawa hakan, kasan dalili? Insp yai shiru, Amir yace saboda a koda yaushe nasara a hannunmu take saboda Allah na tare da mu," Amira ta taho da gudu ta rungume Amir tare da manna mishi kiss a kumatu tace "da kyau namiji, na gode wa Allah da mijina ya zama jarumi kamar matarshi, ya daina tsayawa lusaran 'yan sanda irin wannan abun ta nuna Insp Yahya suna fad'a mishi magana son rai."
Shi d'an sa'ko dama yana mi'ka takarda ya fice ya shige mota yana jiran Insp Yahya, Insp saboda 'kunci da ba'kin cikin maganar da suka dan'kara mishi da ya juyo zai fita sai da ya bige da bango suka kuwa kwashe mishi da dariya.
Suna kan hanya yana tunani, can yana zancen zuci be san ya fito fili ba, fad'i yake "wai ni take cewa lusari, banda ina 'kaunarta da tuni na koya mata hankali wallahi."
_(topha masu karatu kunji wata sabuwa kuma, ni Bk na mato kan Insp Yahya ashe algungumin Amira yake so ba ni ba)_😳🤔😰
Wanda aka had'osu tare da Insp d'in ya kalle shi yace "yallab'ai kai da wa kake ta magana kai kad'ai, naga kamar tunda ka fito daga gidan can ranka a b'ace yake lafiya?" Insp Yahya yace "bakomai, dama tun kafin muzo nan ina tare da damuwa kan fad'an da muka yi da wata budurwata," mutumin nan yace "ayya ashe lamari ne na so, to Allah ya dai-daita ku," Insp Yahya yace "ameen."
Haka aka sake shiga kotu nan ma su Amir ne suka yi nasara, haka sukaita d'aga 'kara daga wannan kotun zuwa waccan haka akaita korar 'karar, da suka ga ba nasara sai kawai suka ha'kura, tare da tunanin wata mafitar kuma.
Amir da Amira na zaune suna maganar komawarsu makaranta sai suka ji sallamar yaro, bayan ya shigo ya gaishe su, sannan ya mi'ka wa Amir wasi'ka yace "wai gashi inji Dadyn Amir da Amira yace a baka kuma gobe kuje Abuja yana son ganinku akwai maganar da zaku yi, dukkansu sai da gabansu ya fad'i jin wanda aka ambata, Amir ya karb'i takardar ya sallami yaron, sedai ya kasa bud'ewa ya karanta ya k'urawa wasi'kar ido sai jujjuyata kawai yake.
_Wata sabuwa inji 'yan caca, to me Dad ya rubuto kuma?🤔_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 135 to 140
Dukkanin su sun ji tsoro da fargaba a ransu musamman ma Amir da takardar ke hannunsa amma ya kasa karantawa sai faman kallonta kawai yake yi.
Amira ce tai ta maza ta zare takardar daga hannunsa ta bud'e ta fara karantawa, kawai Amir ji yayi tana fad'in "tab' Allah ba inda zamu je, ni nasan akwai abinda Dad ya shirya tunda har yake neman mu," Amir wanda jikinshi yai sanyi tun d'azu ya kalleta yace "me Dad d'in yace?" Amira tace "cewa yai wai muyi ha'kuri da dukkanin abinda ya faru, shi komai ya wuce a wajen shi, amma in har muna so auren mu ya cigaba to dole sai mun zo ya yi wata muhimmiyar magana da mu, kuma gobe yake so mu taho da sassafe, gaskiya Amir kar muje ni ina jin tsoro kaga haka yai min wayau lokacin da ina 'karama aka rabani da kai, sannan lokacin da muka je 'kauye ma ranar da muka kunna wayoyinmu cewa yai komai ya wuce muna ina, ashe so suke a gano inda muke a kama mu, ni gaskiya ban yarda muje ba."
Amir ya numfasa sannan yai 'ko'karin b'oye tashi damuwar, yace "Amira ki kwantar da hankalinki, duk abinda kike bana so ki ri'ka manta matsayin su Dad a wajenki, kuma ai dama ko basu neme mu ba wata rana mu dole mu neme su, ni bansan iyayena ba tun ina yaro har na girma kuma har yanzu ina tunanin ina suke a wani hali suke ciki ban sani ba, Amira dole muje muji dalilin kiran da mahaifinki ke mana, saboda rashin zuwan ma wani 'karin laifi ne da zamu yi a wajen shi, dan haka ko da cutar da mu zaisa ayi ya zama wajibi a garemu muyi masa biyayya mu bi abinda yace, ni ba fatana ku kasance a haka ke da mahaifinki ba, fushin iyaye baya haifar da komai wallahi sai lalacewar rayuwar mutum, kuma ni ba zan so rayuwarki ta lalace ba ta sanadina, kullum tunanina dama taya zan shirya ki da mahaifinki, kiyi ha'kuri ki amince muje kinji?"
Amira ta numfasa tare da goge hawayen da ke idanunta, sannan tace "ko ada bana iya yiwa maganarka musu balle a yanzu da ka zama miji a gareni, Allah ya kaimu goben, kuma ina godiya a gareka da kyakkyawar tunatar da ni da kayi kan darajar iyayena, tabbas so kan makantar yakan sa kayi kuskure ko ka manta da komai, amma in kai sa'ar masoyi na gaske kuma nagari koda yaushe 'ko'karinsa yaga ya saka a hanya, saboda ranshi zai sosu a duk lokacin da aka nuna ka akace yau kai ne ka aikata ba dai-dai ba, wallahi ina alfahari da kai, kuma ka 'kara shiga raina fiye da ko yaushe."
Nan da nan suka saki ransu tare da cigaba da hirarsu cikin nishad'i da walwala.
*WASHE GARI*
Washe gari kamar yanda aka umurcesu da sassafe suka tashi suka shirya, sun sha ankon shadda, Amir riga da wando da malum-malum, Amira kuma doguwar riga ce a jikinta tasha aiki me d'an karen kyau da tsada, bayan sun gama shiryawa suka d'auki hanya, kuma da yake basu da wadatattun kud'i a hannunsu na tafiya a jirgi sai suka tafi a motar Amira wadda ita kad'ai ce ta rage musu a yanzu, domin sun yar da ta Amir lokacin da suke gudun cetan ransu, yanzu in za'a kashe su basu san inda motar take ba.
Sun d'auki awanni anata tafiya har Allah ya kawo su garin Abuja lafiya, da yake motar tasu ce ba ta haya ba kai tsaye gidan shugaban 'kasa wato Dad mahaifin Amira suka wuce.
Suna shigowa cikin unguwar tun daga nesa suke ganin adon furanni da busa da kad'e-kad'e kai kace gidan saraki, ana bud'e gate kuwa zasu kutsa da motarsu aka fara antayo musu fulawoyi har zuwa inda zasu faka motarsu, cikin sauri aka bud'e musu mota suka fito, sakin baki suka yi suna kallon yanda aka k'awata harabar gidan da kyawawan ado, mahaifiyar Amira da Dad d'inta da su Uncle kai har da sistern ta d'iyar Uncle d'in suna tsaye a bakin 'kofar da zata sadaka da shiga ciki, da gudu Amira ta 'karasa wajen Dad d'inta ta rungume shi tana kuka tare da fad'in "Dad dan Allah kayi ha'kuri ka ya......" kafin ta 'karasa Dad ya rufe mata baki tare da d'agota ya share mata hawaye, sannan yace " na yafe miki Doughter nah, kinsan ina sonki bana iya yin fushi dake," ya kama hannunta sannan ya yafito Amir da ya zuba musu idanu da hannu, yana zuwa shima ya ri'ke mishi hannu suka yi musu barka da zuwa sannan suka yi musu jagora har cikin babban falon gidan.
Dad kuwa in ka ganshi a wannan ranar zaka ce ba shi bane, saboda yanda yake ta bayyanar da farin cikinsa kamar wani abu bai tab'a faruwa ba.
Bayan an ci an sha, sannan suka dawo babban falo suka zauna, Dad yai gyaran murya sannan ya fara magana "abinda yasa na kira ku shine saboda in sanar da ku cewa komai ya wuce, kuma hatta aurenku mun yarda dashi, amma akwai sharad'i, saboda matsayina da kuma martabar gidan nan dole sai ka kawo mana iyayenka nan mun gansu, kuma daga yau har zuwa ranar da zaka gano inda iyayenka suke a nan gidan zaku cigaba da zama, in yaso in ka gabatar mana da su sai ka d'auki matarka ka tafi da ita ma duk inda zaka tafi da ita, rashin yin hakan zai sa da kai da wad'anda suka yi muku jagora wajen yin aure zan makaku a kotu a raba aurenka da 'yata kuma kasan tsab za'a raba d'in tunda ba mu muka d'aura ba kuma ba da yardarmu ba."
Mugun tashin hankali suka shiga daga shi har Amira, babu abinda zuciyarshi ke ayyana mishi game da wannan maganar illah anyi haka ne domin a rabashi da Amira, in ba haka ba ta ina zai fara neman iyayenshi.
Irin tunanin da yake itama Amira shi take yi, cikin sauri ta mi'ke tana fad'in "haba Dad, be kamata ka....." Dad ya d'aga mata hannu tare da fad'in "ya isa Doughter, ni mahaifinki ne, a baya mun barku kun yi yanda kuke so, a yanzu dole ku barmu muyi namu binciken a matsayinmu na iyaye, kuma na gama magana," ya mi'ke yai shigewarsa d'aki.
Uncle ya numfasa, sannan yace "gaskiya Amira ki rage yiwa mahaifinki musu a kan namiji da bashi da tabbas, kuma in kina canza halinki ta hanyar bijirewa maganar iyayenki to shi zaki jawa tsana a idanunmu, a yanzu kam ina goyon bayan maganarshi, sai kuje kuyi tunani, d'akinki shine masaukin ku an gyara ko ina, shikenan kowa ya tashi ya tafi an gama meeting d'in."
Haka kowa ya watse ya barsu a nan falon, shi kuwa Amir tunda yaji wannan maganar ya zama kamar gunki ya kasa motsi, babu abinda ke mishi yawo sai maganar Dad.
Amira ta matso inda yake zaune a 'kasan kafet, ta share mishi Hawayen da ke zubowa kan fuskarshi, sannan ta mi'ke tare da kama hannunshi ta jashi suka hau sama haka yaita binta kamar ra'kumi har suka shiga d'aki.
Shi d'an sa'ko dama yana mi'ka takarda ya fice ya shige mota yana jiran Insp Yahya, Insp saboda 'kunci da ba'kin cikin maganar da suka dan'kara mishi da ya juyo zai fita sai da ya bige da bango suka kuwa kwashe mishi da dariya.
Suna kan hanya yana tunani, can yana zancen zuci be san ya fito fili ba, fad'i yake "wai ni take cewa lusari, banda ina 'kaunarta da tuni na koya mata hankali wallahi."
_(topha masu karatu kunji wata sabuwa kuma, ni Bk na mato kan Insp Yahya ashe algungumin Amira yake so ba ni ba)_😳🤔😰
Wanda aka had'osu tare da Insp d'in ya kalle shi yace "yallab'ai kai da wa kake ta magana kai kad'ai, naga kamar tunda ka fito daga gidan can ranka a b'ace yake lafiya?" Insp Yahya yace "bakomai, dama tun kafin muzo nan ina tare da damuwa kan fad'an da muka yi da wata budurwata," mutumin nan yace "ayya ashe lamari ne na so, to Allah ya dai-daita ku," Insp Yahya yace "ameen."
Haka aka sake shiga kotu nan ma su Amir ne suka yi nasara, haka sukaita d'aga 'kara daga wannan kotun zuwa waccan haka akaita korar 'karar, da suka ga ba nasara sai kawai suka ha'kura, tare da tunanin wata mafitar kuma.
Amir da Amira na zaune suna maganar komawarsu makaranta sai suka ji sallamar yaro, bayan ya shigo ya gaishe su, sannan ya mi'ka wa Amir wasi'ka yace "wai gashi inji Dadyn Amir da Amira yace a baka kuma gobe kuje Abuja yana son ganinku akwai maganar da zaku yi, dukkansu sai da gabansu ya fad'i jin wanda aka ambata, Amir ya karb'i takardar ya sallami yaron, sedai ya kasa bud'ewa ya karanta ya k'urawa wasi'kar ido sai jujjuyata kawai yake.
_Wata sabuwa inji 'yan caca, to me Dad ya rubuto kuma?🤔_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 135 to 140
Dukkanin su sun ji tsoro da fargaba a ransu musamman ma Amir da takardar ke hannunsa amma ya kasa karantawa sai faman kallonta kawai yake yi.
Amira ce tai ta maza ta zare takardar daga hannunsa ta bud'e ta fara karantawa, kawai Amir ji yayi tana fad'in "tab' Allah ba inda zamu je, ni nasan akwai abinda Dad ya shirya tunda har yake neman mu," Amir wanda jikinshi yai sanyi tun d'azu ya kalleta yace "me Dad d'in yace?" Amira tace "cewa yai wai muyi ha'kuri da dukkanin abinda ya faru, shi komai ya wuce a wajen shi, amma in har muna so auren mu ya cigaba to dole sai mun zo ya yi wata muhimmiyar magana da mu, kuma gobe yake so mu taho da sassafe, gaskiya Amir kar muje ni ina jin tsoro kaga haka yai min wayau lokacin da ina 'karama aka rabani da kai, sannan lokacin da muka je 'kauye ma ranar da muka kunna wayoyinmu cewa yai komai ya wuce muna ina, ashe so suke a gano inda muke a kama mu, ni gaskiya ban yarda muje ba."
Amir ya numfasa sannan yai 'ko'karin b'oye tashi damuwar, yace "Amira ki kwantar da hankalinki, duk abinda kike bana so ki ri'ka manta matsayin su Dad a wajenki, kuma ai dama ko basu neme mu ba wata rana mu dole mu neme su, ni bansan iyayena ba tun ina yaro har na girma kuma har yanzu ina tunanin ina suke a wani hali suke ciki ban sani ba, Amira dole muje muji dalilin kiran da mahaifinki ke mana, saboda rashin zuwan ma wani 'karin laifi ne da zamu yi a wajen shi, dan haka ko da cutar da mu zaisa ayi ya zama wajibi a garemu muyi masa biyayya mu bi abinda yace, ni ba fatana ku kasance a haka ke da mahaifinki ba, fushin iyaye baya haifar da komai wallahi sai lalacewar rayuwar mutum, kuma ni ba zan so rayuwarki ta lalace ba ta sanadina, kullum tunanina dama taya zan shirya ki da mahaifinki, kiyi ha'kuri ki amince muje kinji?"
Amira ta numfasa tare da goge hawayen da ke idanunta, sannan tace "ko ada bana iya yiwa maganarka musu balle a yanzu da ka zama miji a gareni, Allah ya kaimu goben, kuma ina godiya a gareka da kyakkyawar tunatar da ni da kayi kan darajar iyayena, tabbas so kan makantar yakan sa kayi kuskure ko ka manta da komai, amma in kai sa'ar masoyi na gaske kuma nagari koda yaushe 'ko'karinsa yaga ya saka a hanya, saboda ranshi zai sosu a duk lokacin da aka nuna ka akace yau kai ne ka aikata ba dai-dai ba, wallahi ina alfahari da kai, kuma ka 'kara shiga raina fiye da ko yaushe."
Nan da nan suka saki ransu tare da cigaba da hirarsu cikin nishad'i da walwala.
*WASHE GARI*
Washe gari kamar yanda aka umurcesu da sassafe suka tashi suka shirya, sun sha ankon shadda, Amir riga da wando da malum-malum, Amira kuma doguwar riga ce a jikinta tasha aiki me d'an karen kyau da tsada, bayan sun gama shiryawa suka d'auki hanya, kuma da yake basu da wadatattun kud'i a hannunsu na tafiya a jirgi sai suka tafi a motar Amira wadda ita kad'ai ce ta rage musu a yanzu, domin sun yar da ta Amir lokacin da suke gudun cetan ransu, yanzu in za'a kashe su basu san inda motar take ba.
Sun d'auki awanni anata tafiya har Allah ya kawo su garin Abuja lafiya, da yake motar tasu ce ba ta haya ba kai tsaye gidan shugaban 'kasa wato Dad mahaifin Amira suka wuce.
Suna shigowa cikin unguwar tun daga nesa suke ganin adon furanni da busa da kad'e-kad'e kai kace gidan saraki, ana bud'e gate kuwa zasu kutsa da motarsu aka fara antayo musu fulawoyi har zuwa inda zasu faka motarsu, cikin sauri aka bud'e musu mota suka fito, sakin baki suka yi suna kallon yanda aka k'awata harabar gidan da kyawawan ado, mahaifiyar Amira da Dad d'inta da su Uncle kai har da sistern ta d'iyar Uncle d'in suna tsaye a bakin 'kofar da zata sadaka da shiga ciki, da gudu Amira ta 'karasa wajen Dad d'inta ta rungume shi tana kuka tare da fad'in "Dad dan Allah kayi ha'kuri ka ya......" kafin ta 'karasa Dad ya rufe mata baki tare da d'agota ya share mata hawaye, sannan yace " na yafe miki Doughter nah, kinsan ina sonki bana iya yin fushi dake," ya kama hannunta sannan ya yafito Amir da ya zuba musu idanu da hannu, yana zuwa shima ya ri'ke mishi hannu suka yi musu barka da zuwa sannan suka yi musu jagora har cikin babban falon gidan.
Dad kuwa in ka ganshi a wannan ranar zaka ce ba shi bane, saboda yanda yake ta bayyanar da farin cikinsa kamar wani abu bai tab'a faruwa ba.
Bayan an ci an sha, sannan suka dawo babban falo suka zauna, Dad yai gyaran murya sannan ya fara magana "abinda yasa na kira ku shine saboda in sanar da ku cewa komai ya wuce, kuma hatta aurenku mun yarda dashi, amma akwai sharad'i, saboda matsayina da kuma martabar gidan nan dole sai ka kawo mana iyayenka nan mun gansu, kuma daga yau har zuwa ranar da zaka gano inda iyayenka suke a nan gidan zaku cigaba da zama, in yaso in ka gabatar mana da su sai ka d'auki matarka ka tafi da ita ma duk inda zaka tafi da ita, rashin yin hakan zai sa da kai da wad'anda suka yi muku jagora wajen yin aure zan makaku a kotu a raba aurenka da 'yata kuma kasan tsab za'a raba d'in tunda ba mu muka d'aura ba kuma ba da yardarmu ba."
Mugun tashin hankali suka shiga daga shi har Amira, babu abinda zuciyarshi ke ayyana mishi game da wannan maganar illah anyi haka ne domin a rabashi da Amira, in ba haka ba ta ina zai fara neman iyayenshi.
Irin tunanin da yake itama Amira shi take yi, cikin sauri ta mi'ke tana fad'in "haba Dad, be kamata ka....." Dad ya d'aga mata hannu tare da fad'in "ya isa Doughter, ni mahaifinki ne, a baya mun barku kun yi yanda kuke so, a yanzu dole ku barmu muyi namu binciken a matsayinmu na iyaye, kuma na gama magana," ya mi'ke yai shigewarsa d'aki.
Uncle ya numfasa, sannan yace "gaskiya Amira ki rage yiwa mahaifinki musu a kan namiji da bashi da tabbas, kuma in kina canza halinki ta hanyar bijirewa maganar iyayenki to shi zaki jawa tsana a idanunmu, a yanzu kam ina goyon bayan maganarshi, sai kuje kuyi tunani, d'akinki shine masaukin ku an gyara ko ina, shikenan kowa ya tashi ya tafi an gama meeting d'in."
Haka kowa ya watse ya barsu a nan falon, shi kuwa Amir tunda yaji wannan maganar ya zama kamar gunki ya kasa motsi, babu abinda ke mishi yawo sai maganar Dad.
Amira ta matso inda yake zaune a 'kasan kafet, ta share mishi Hawayen da ke zubowa kan fuskarshi, sannan ta mi'ke tare da kama hannunshi ta jashi suka hau sama haka yaita binta kamar ra'kumi har suka shiga d'aki.