Sashe 24
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dad yace ‘’ku baza yaranku a fita neman su nan ma zansa a bincike su, duk yanda ake ciki zamu yi waya,‘’ suna gama waya Dad ya sake kiran shugaban 'yan sanda na nan Abuja yai mishi bayanin komai tare da bashi umurnin a bincika ko ina duk wanda aka gani cikinsu a kamo shi a kawo su gareshi, bayan ya gama wayar yaita gwada ta Amira amma sam tak'i shiga, wurgi ya yi da wayar kan tiles d'in falon ai kuwa ta tararratse, yana fad'in ‘’ta kashe wayarta balle insa a gano inda take, wallahi na kama Amira sai ta raina kanta, sai na ajiye tsananin k'aunar da nake yi mata a raina na hukuntata dai-dai da abinda ta aikata a gareni, na saki jiki tana karatu ashe ta maida mu wawaye tana can tabi d'an iska, haka yaita surutu shi kad'ai cikin tsantsar b'acin rai idanunshi sunyi mugun ja saboda b'acin rai, ya kalli 'kaninshi ya cigaba da fad'in Amira na so ta zubar mana da mutuncin gida, wai ta rasa wanda zata so sai makashi mai yin kisa kuma har ta bishi su gudu, ita da na tura tai karatu itace da bin d'an iska makashin mutane har rayuka biyu, to wallahi idona idon saurayin nan nata koh, wallahi sai na b'atar dashi, sai na wulak'anta rayuwarshi kamar yanda ya hure wa 'yata kunne, ita kuma koh hmmmm,‘’ ya juya cikin tsananin fushi ya shiga d'akin shi.
Ko'ina an baza yara neman su Amir amma sam ba labarinsu, hakan ya k'ara wa Dad shiga cikin damuwa, kuma kullum cikin gwada lambar wayar Amira yake yi ko Allah zai sa a dace wata rana a samu, a haka har aka kai wajen wata d'aya ana bincike amma sam babu su ba labarin su, hakan yasa Dad yasa aka turo mishi Insp Yahya har gida domin yai ganawa ta musamman da shi.
……………………… ……………………
Bangaren su Amira da Amir kuwa hankalinsu kwance yake a k'auyen nan ba abinda ke damun su, soyayyar su kuwa kullum dad'a nunkuwa take, kullum suka gama taya iyayen gidan su aiki zama suke cikin gida ko a waje jikin bishiya suita hirar su, abu d'aya ne kad'ai ya fara damun Amira, yanda ta lura da 'yan matan k'auyen ke nuna soyayyar su a kan Amir, har cincirindo wasu suke yi kawai dan su ganshi.
Yau ma zaune suke a waje da yamma suna hirar su me dad'i, Amira ta kalli Amir tace " son da nake maka abu ne me matu'kar muhimmanci a rayuwata, rasaka kuma tamkar rasa rayuwata ne, shin kana jin shau'kin son da nake maka kuwa Amir d'ina, tunda nake ban tab'a son wani d'a namiji ba sai kai, kuma zuciyata ba zata tab'a d'aukar wani ba bayan kai."
Amir ya ce "Amira ki kwantar da hankalinki ni naki ne har abada haka kema tawa ce har k'arshen numfashi, gamu kuma a tare muna rayuwa waje d'aya, kawai addu'a zamui ta yi Allah ya bamu ikon mallakar juna matsayin ma'aurata."
Amira tayi murmushi sannan ta amsa da "ameen. "
To da yake 'kauyen da suke ciki suna dad'ewa kafin su samu wuta shiyasa wayoyinsu kwata kwata babu caji, suna,cikin wannan hirar cikin ikon Allah sai ga wuta an kawo gaba d'aya 'kauyen ya kaure da 'kara kasancewar sun dad' basu ga k'yallowarta ba, hakan yasa su Amir ma suka katse hirar da suke yi suka shiga ciki domin su saka caji.
Suna saka caji Amira ta kunna ta-ta wayar, tana kunnawa ta koma kusa da Amir ta zauna suka ci gaba da hira, sedai bata dad'e da zama ba wayarta ta fara ringing, tashi ta yi domin zuwa ta duba taga ko waye ya kira ta, Dad d'inta ne ke kira, cikin sauri ta d'aga tare da karawa a kunne se dai ta kasa cewa komai, ji tayi yace " My Daughter karki damu nasan duk abinda ke faruwa, saboda haka ki kwantar da hankalinki yanzu kina ina ne?"
Amira cikin murna da farin cikin mahaifinta be d'auki zafi ba kan lamarin tace "Dad muna…………" Amir ne yai saurin karb'e wayar daga hannunta tare da kashewa gaba d'aya.
Amira ta kalle shi tace " Amir Dad d'ina ne fa," Amir yace "haba Amira so kike azo a kama mu, ko kin dena sona ne yanzu kin amince a kasheni?"
Amira tace "no babu wannan ranar har abada, kawai dai tunani nayi akan b'oyon da muke ta yi sam bashi da amfani," Amir yace "amma Amira ki gane mana kuma kiyi tunani kinsan Dad yana da zafi sosai in har ba abinda suka shirya a kanmu be kamata ace yai saurin saukowa ba haka har yana neman inda muke, kuma be yi miki fad'a ba fa sai tambaya da yake yi wai kina ina, in kika fad' inda muke Amira kama ni za'ai kuma nasan daga ranar ba zamu sake ganin juna ba dan kasheni zasu yi."
Amira tace " Amir ka kwantar da hankalinka, Dad yana 'kaunata sosai, kuma na tabbatar 'kaunar da yake min zaisa ya amince in auri wanda nake so, ka kwantar da hankalinka a yanayin da na jishi ba zai bamu matsala ba insha Allah."
Amir kam ba don ya gamsu da bayananta ba ya amince dasu, domin shi ya tabbatar suna zuwa zasu raba su, amma saboda baya so ya cigaba da jayayya da ita a kan magana da mahaifinta sai ya amince da abinda tace tare da mi'ka mata wayar ya koma inda yake zaune da ya zauna tare da zuba mata idanu.
Amira ta karb'i wayar ta kunna, tana 'ko'karin kiran Dadyn sai ga kiransa ya sake shigowa, Amira ta d'aga sannan cikin sanyin murya wadda take bayyanar da aji tausayin mutum tace "Dad muna magana d'azu ta yanke," Dad yace ba damuwa fad'a min kuna ina ne gobe zan turo a d'auke ku?"
Amira tace " muna zaria cikin 'kauyen…………" da yake wayar da suke yi ba caji tayi ba suka sake d'auke wutar su, Amira tace " wayyo Allah Amir sun sake d'aukewa kuma, ko taka ta yi caji ka d'an ara min in kira Dad?" Amir wanda yai mugun jin dad'in d'aukewar wutar yace " ai ni tawa wayar ma ta'ki kawowa kwata kwata, 'kila saboda dad'ewar da tayi ba caji ne."
Amira tace " to Allah sa su dawo da ita, sai yanzu hankalina ya fara kwanciya nake jin k'arfin guiwar yiwuwar aurenmu da kai Amir," Amir yai murmushi sannan yace " Allah ya tabbatar mana da alkhairi," Amira tace " Ameen, amma ya naga yanayinka ya canza?"
Amir yace "ka jita, to na canza da me, bakomai fa," nan dai suka ci gaba da hira har lokacin sallar magrib ya yi, suka tashi suka fita tsakar gida domin yin alwala su gabatar da sallar su.
Da dare Amira ta kasa bacci zuciyarta na nazarin maganar Amir, har Amir yai bacci ma amma ita idanunta biyu, tunani take yi itama yanda mahaifint ke 'kaunar karatun ta yaji bata makaranta kuma yai saurin saukowa haka, lallai akwai wata a k'asa, ta sake tuno abinda aka yi mata kan Amir tun suna 'kanana, hakan yasa tai amanna da zancen Amir cikin zuciyarta.
*BAYAN KWANA BIYU*
Dad ne zaune shi da Insp Yahya a d'aki na musamman suna tattaunawa kan maganar su Amira, bayan sun gama magana Dad ya bashi lambar Amir da Amira tare da bada umurnin suita kira duk ranar da suka yi sa'a suka samu lambar d'aya daga ciki to kawai suyi 'ko'karin binciko inda suke.
Insp Yahya yace " ai yanzu da wuya su d'aga kowace lamba musamman lambar da babu suna, ni a tunanina kamata yai a cikin wad'anda suke shiri kuma suke waya cikin d'alibai mu samu d'aya daga cikin su a sashi yaita kira har a samu su d'aga koda mutum uku ne dole za'a samu mutum d'aya a cikinsu wanda zasu d'aga wayar shi."
Dad yace " lallai na yarda da maganar da kwamishina ya yi a kanka, kaje ka aiwatar da duk abinda ya kamata daga yau, da zarar kun samu wayar ta shiga kafin ku binciko inda suke ku sanar dani a gabana nake so a kama su domin inga mai k'arfin halin iya d'auke min 'ya."
Nan dai suka yi sallama Dad ya bashi ma'kudan kud'i, Insp Yahya ya fito ya tafi.
Yau Alhamis, 'karfe takwas dai-dai na safe Amir da Amira suna zaune cikin d'aki, gama karyawarsu kenan, sun fitar da kayan abincin Amira ta wanke ta dawo suka zauna suna hira, suna cikin hirar ne aka kawo wuta, suka sa caji sannan suka tashi suka tafi d'ebo ruwa.
kasancewar sun tarar da layi yasa suka dad'e a wajen sai da suka yi wajen kusan awa guda sannan layi yazo kansu suka d'iba suka juyo zuwa gida, se dai suna shawo kwanar gidan suka hango su Umma a 'kofar gida, cikin sauri suka k'araso wajen su suna tambayar su me suke yi a tsaye a 'kofar gida, Umma cikin farin ciki tace " albishirinku yarana bayan fitarku aka kira wayar Amira naji k'aran ya'ki 'karewa nazo naita daddangwalawa sai in na kara kuma inji shiru ban sani ba ko kashewa nai ko d'auka har Allah ya bani sa'a aka jini sai na fad'a musu bakwa nan kun fita, sai suka fad'amin cewa kun b'ace ne suna nemanku, , ina jin haka na gane 'yan uwanku ne, shiyasa nai musu kwatancen nan suka taho, a ta'kaice dai yau Allah ya kawo iyayenku."
Amira ta d'ora hannaye a kai tare da runtuma kuka tana fad'in shikenan mun shiga uku," Amir yace " Amira tunda sun gane inda muke zo mu gudu tun kafin su zo su iskemu anan," Baba da Umma suna ta fad'in me yafaru meyasa bakwa farin ciki, ina sam basu sauraresu ba Amir ya kama hannun Amira ya jata zasu gudu amma se dai sun makaro, suna juyowa suka ga Dad da rundunar sojoji da 'yan sanda kewaye dasu kamar wad'anda zasu tafi ya'kar miliyoyin mutane.
Ko'ina an baza yara neman su Amir amma sam ba labarinsu, hakan ya k'ara wa Dad shiga cikin damuwa, kuma kullum cikin gwada lambar wayar Amira yake yi ko Allah zai sa a dace wata rana a samu, a haka har aka kai wajen wata d'aya ana bincike amma sam babu su ba labarin su, hakan yasa Dad yasa aka turo mishi Insp Yahya har gida domin yai ganawa ta musamman da shi.
……………………… ……………………
Bangaren su Amira da Amir kuwa hankalinsu kwance yake a k'auyen nan ba abinda ke damun su, soyayyar su kuwa kullum dad'a nunkuwa take, kullum suka gama taya iyayen gidan su aiki zama suke cikin gida ko a waje jikin bishiya suita hirar su, abu d'aya ne kad'ai ya fara damun Amira, yanda ta lura da 'yan matan k'auyen ke nuna soyayyar su a kan Amir, har cincirindo wasu suke yi kawai dan su ganshi.
Yau ma zaune suke a waje da yamma suna hirar su me dad'i, Amira ta kalli Amir tace " son da nake maka abu ne me matu'kar muhimmanci a rayuwata, rasaka kuma tamkar rasa rayuwata ne, shin kana jin shau'kin son da nake maka kuwa Amir d'ina, tunda nake ban tab'a son wani d'a namiji ba sai kai, kuma zuciyata ba zata tab'a d'aukar wani ba bayan kai."
Amir ya ce "Amira ki kwantar da hankalinki ni naki ne har abada haka kema tawa ce har k'arshen numfashi, gamu kuma a tare muna rayuwa waje d'aya, kawai addu'a zamui ta yi Allah ya bamu ikon mallakar juna matsayin ma'aurata."
Amira tayi murmushi sannan ta amsa da "ameen. "
To da yake 'kauyen da suke ciki suna dad'ewa kafin su samu wuta shiyasa wayoyinsu kwata kwata babu caji, suna,cikin wannan hirar cikin ikon Allah sai ga wuta an kawo gaba d'aya 'kauyen ya kaure da 'kara kasancewar sun dad' basu ga k'yallowarta ba, hakan yasa su Amir ma suka katse hirar da suke yi suka shiga ciki domin su saka caji.
Suna saka caji Amira ta kunna ta-ta wayar, tana kunnawa ta koma kusa da Amir ta zauna suka ci gaba da hira, sedai bata dad'e da zama ba wayarta ta fara ringing, tashi ta yi domin zuwa ta duba taga ko waye ya kira ta, Dad d'inta ne ke kira, cikin sauri ta d'aga tare da karawa a kunne se dai ta kasa cewa komai, ji tayi yace " My Daughter karki damu nasan duk abinda ke faruwa, saboda haka ki kwantar da hankalinki yanzu kina ina ne?"
Amira cikin murna da farin cikin mahaifinta be d'auki zafi ba kan lamarin tace "Dad muna…………" Amir ne yai saurin karb'e wayar daga hannunta tare da kashewa gaba d'aya.
Amira ta kalle shi tace " Amir Dad d'ina ne fa," Amir yace "haba Amira so kike azo a kama mu, ko kin dena sona ne yanzu kin amince a kasheni?"
Amira tace "no babu wannan ranar har abada, kawai dai tunani nayi akan b'oyon da muke ta yi sam bashi da amfani," Amir yace "amma Amira ki gane mana kuma kiyi tunani kinsan Dad yana da zafi sosai in har ba abinda suka shirya a kanmu be kamata ace yai saurin saukowa ba haka har yana neman inda muke, kuma be yi miki fad'a ba fa sai tambaya da yake yi wai kina ina, in kika fad' inda muke Amira kama ni za'ai kuma nasan daga ranar ba zamu sake ganin juna ba dan kasheni zasu yi."
Amira tace " Amir ka kwantar da hankalinka, Dad yana 'kaunata sosai, kuma na tabbatar 'kaunar da yake min zaisa ya amince in auri wanda nake so, ka kwantar da hankalinka a yanayin da na jishi ba zai bamu matsala ba insha Allah."
Amir kam ba don ya gamsu da bayananta ba ya amince dasu, domin shi ya tabbatar suna zuwa zasu raba su, amma saboda baya so ya cigaba da jayayya da ita a kan magana da mahaifinta sai ya amince da abinda tace tare da mi'ka mata wayar ya koma inda yake zaune da ya zauna tare da zuba mata idanu.
Amira ta karb'i wayar ta kunna, tana 'ko'karin kiran Dadyn sai ga kiransa ya sake shigowa, Amira ta d'aga sannan cikin sanyin murya wadda take bayyanar da aji tausayin mutum tace "Dad muna magana d'azu ta yanke," Dad yace ba damuwa fad'a min kuna ina ne gobe zan turo a d'auke ku?"
Amira tace " muna zaria cikin 'kauyen…………" da yake wayar da suke yi ba caji tayi ba suka sake d'auke wutar su, Amira tace " wayyo Allah Amir sun sake d'aukewa kuma, ko taka ta yi caji ka d'an ara min in kira Dad?" Amir wanda yai mugun jin dad'in d'aukewar wutar yace " ai ni tawa wayar ma ta'ki kawowa kwata kwata, 'kila saboda dad'ewar da tayi ba caji ne."
Amira tace " to Allah sa su dawo da ita, sai yanzu hankalina ya fara kwanciya nake jin k'arfin guiwar yiwuwar aurenmu da kai Amir," Amir yai murmushi sannan yace " Allah ya tabbatar mana da alkhairi," Amira tace " Ameen, amma ya naga yanayinka ya canza?"
Amir yace "ka jita, to na canza da me, bakomai fa," nan dai suka ci gaba da hira har lokacin sallar magrib ya yi, suka tashi suka fita tsakar gida domin yin alwala su gabatar da sallar su.
Da dare Amira ta kasa bacci zuciyarta na nazarin maganar Amir, har Amir yai bacci ma amma ita idanunta biyu, tunani take yi itama yanda mahaifint ke 'kaunar karatun ta yaji bata makaranta kuma yai saurin saukowa haka, lallai akwai wata a k'asa, ta sake tuno abinda aka yi mata kan Amir tun suna 'kanana, hakan yasa tai amanna da zancen Amir cikin zuciyarta.
*BAYAN KWANA BIYU*
Dad ne zaune shi da Insp Yahya a d'aki na musamman suna tattaunawa kan maganar su Amira, bayan sun gama magana Dad ya bashi lambar Amir da Amira tare da bada umurnin suita kira duk ranar da suka yi sa'a suka samu lambar d'aya daga ciki to kawai suyi 'ko'karin binciko inda suke.
Insp Yahya yace " ai yanzu da wuya su d'aga kowace lamba musamman lambar da babu suna, ni a tunanina kamata yai a cikin wad'anda suke shiri kuma suke waya cikin d'alibai mu samu d'aya daga cikin su a sashi yaita kira har a samu su d'aga koda mutum uku ne dole za'a samu mutum d'aya a cikinsu wanda zasu d'aga wayar shi."
Dad yace " lallai na yarda da maganar da kwamishina ya yi a kanka, kaje ka aiwatar da duk abinda ya kamata daga yau, da zarar kun samu wayar ta shiga kafin ku binciko inda suke ku sanar dani a gabana nake so a kama su domin inga mai k'arfin halin iya d'auke min 'ya."
Nan dai suka yi sallama Dad ya bashi ma'kudan kud'i, Insp Yahya ya fito ya tafi.
Yau Alhamis, 'karfe takwas dai-dai na safe Amir da Amira suna zaune cikin d'aki, gama karyawarsu kenan, sun fitar da kayan abincin Amira ta wanke ta dawo suka zauna suna hira, suna cikin hirar ne aka kawo wuta, suka sa caji sannan suka tashi suka tafi d'ebo ruwa.
kasancewar sun tarar da layi yasa suka dad'e a wajen sai da suka yi wajen kusan awa guda sannan layi yazo kansu suka d'iba suka juyo zuwa gida, se dai suna shawo kwanar gidan suka hango su Umma a 'kofar gida, cikin sauri suka k'araso wajen su suna tambayar su me suke yi a tsaye a 'kofar gida, Umma cikin farin ciki tace " albishirinku yarana bayan fitarku aka kira wayar Amira naji k'aran ya'ki 'karewa nazo naita daddangwalawa sai in na kara kuma inji shiru ban sani ba ko kashewa nai ko d'auka har Allah ya bani sa'a aka jini sai na fad'a musu bakwa nan kun fita, sai suka fad'amin cewa kun b'ace ne suna nemanku, , ina jin haka na gane 'yan uwanku ne, shiyasa nai musu kwatancen nan suka taho, a ta'kaice dai yau Allah ya kawo iyayenku."
Amira ta d'ora hannaye a kai tare da runtuma kuka tana fad'in shikenan mun shiga uku," Amir yace " Amira tunda sun gane inda muke zo mu gudu tun kafin su zo su iskemu anan," Baba da Umma suna ta fad'in me yafaru meyasa bakwa farin ciki, ina sam basu sauraresu ba Amir ya kama hannun Amira ya jata zasu gudu amma se dai sun makaro, suna juyowa suka ga Dad da rundunar sojoji da 'yan sanda kewaye dasu kamar wad'anda zasu tafi ya'kar miliyoyin mutane.