Sashe 48
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amir ya saki salati tare da dafe kai yace "ba can zasu tafi ba, Nura da mahaifinsa damfarar Dad suke son yi," nan ya kwashe komai ya fad'a mata, sannan yace "bari ma kiji, wayarsa ya d'auko ya kira lambar Dad bayan minti biyu aka d'auka, Amir yace "hello Dad kana ina ne?"
Nura ya she'ke da dariya sannan yace Dad da tsohuwar matarka suna wajenmu, duk shirinka baka isa ka wargaza namu ba Amir," ana gama fad'in haka aka kashe wayar.
Amir ya kalli Mum yace "kinji ko, to yanzu duk ku fito daga gidan nan muje gidana ku zauna kar kuma su turo ai muku wani abu," saboda sanin halin mai gidan sai suka kasa yarda da abinda Amir yace, haka yaita ro'konsu amma suka 'ki binshi.
Hakan yasa yaiwa bataliyar masu tsaronshi waya kan suzo, yai musu kwatancen unguwar, cikin 'kan'kanin lokaci kuwa suka 'karaso, ya basu umurni kan su kula da mutanen gidan nan kamar yanda zasu kula da shi, sannan ya cewa su Mum da Uncle kar suji tsoro mutanenshi ne.
Amir ya juyo ya fito daga gidan, kai tsaye wucewa mtn office yai kai tsaye domin a binciko mishi daga inda aka kira lambar.
Bayan an kira lambar sai suka sake d'auka wannan karon Insp Yahya ne ya d'aga yana fad'a mishi matarshi da sirikinshi suna sume, kuma sun riga da sun saka hannu da yatsan Dad a sumen yanzu duk abinda ya mallaka a duniya ya zama ba nashi ba, kuma yanzu zasu ba'kunci lahira, sannan ya 'karashe da fad'in " idan ka isa kazo ka taimakesu."
Cikin sauri aka gama tantance inda suke Amir ya karb'i addreshin wajen ya tafi.
Gudu kawai yake a mota yana jin tsoro kar su kashe mishi Amirar shi.
Cikin minti talatin ya 'karaso wajen kuma ya shiga ciki da gudu yana 'kwalawa su Amira kira.
Cikin wani 'katon kango ne, yana shiga can ciki yaga Amira da Dad an d'aure su, cikin sauri ya nufi inda suke, lallab'owa ta baya aka yi aka buga mishi wani abu a baya, take anan ya zube 'kasa, kuma lokaci guda suka kewaye shi, bayan sun mishi dukan tsiya sannan shima aka d'aure shi.
Dad ya kalli Baban Nura yace "yanzu duk irin yardar da nai maka amma shine ka saka min da wannan abun ko, da ikon Allah 'karshenka ba zaiyi kyau ba."
Baban Nura ya she'ke da dariya sannan yace "ai kai ka jawa kanka, ka tsani talaka, sannan kana tsoron had'a komai da talaka, ai na dad'e ina jiran zuwan wannan ranar, duk 'kulawa da 'kaunar da nake maka ba taka bace ta dukiyarka ce, amma wai kai me wayau ka katange komai to muma ga irin namu wayon nan mun nuna maka, albishir biyu yanzu zanyi maka, na farko duk wasu kadarori da suke mallakinka yanzu sun zama namu ni da d'ana hatta gidan da kake ciki mun siyar, abu na biyu kuma shine yanzu zamu 'kara muku gudu zuwa lahira domin barinku a raye zai iya zama mana barazana a cikin sabuwar rayuwar da zamu yi, kuma kaga kaima mun taimaka maka shan takaicin rayuwa cikin talauci, naso dai in barka a raye kaji irin yanda rayuwar talauci take, amma na sanka farin sani sam baka yafiya akan komai."
Insp Yahya ya kalli Baba yace "ni Baba Amir d'in can nake so ku barni in kashe shi da kaina."
Baba da Nura suka she'ke da dariya, sannan suka had'a baki wajen cewa "an baka," sannan su duka ukun harda tarin 'kattan dake cike a wajen suka sake kwashewa da dariya, wurin sai amsawa yake yi.
Baba ya baiwa Nura umurnin kashe su Amiran, sedai Amir na ganin inda Nura ya tunkara hannunsa ri'ke da bindigar Insp Yahya sai yai wani irin tashi yana a d'auren yaje da gudu ya bangaji Nura suka fad'i 'kasa a tare.
Kiciniyar 'kwace bindigar Amir yakeyi daga hannun Nura cikin ikon Allah ya samu d'aurin hannunshi ya kwance ya 'kwace bindigar sannan ya kwance su Amira da Dad yana cikin kwancesu Insp Yahya ya ciro bindigar jami'in dake kusa dashi ya saita Amir da ita tare da harbin Amir d'in a hannu, Amir yai wani irin razanannen 'kara, tare da dafe wajen ya kalli su Dad yace su gudu zai biyosu daga baya, Amira taja ta tsaya tana ri'ke da hannunshi mai ciwon tana kuka tana fad'in "taya zan tafi in barka a irin wannan halin, ni ba inda zanje ko mutuwar ne ma gwara a kashemu tare," Amir ya dafata, sannan yace "ki kwantar da hankalinki Amira Insha Allah rabuwarmu ba yanzu ba, zan dawo gareki nai miki al'kawari."
Cikin sauri kuwa Dad ya jata da gudu suka fice daga wurin nace ashe Dad ansan darajar rai hahaha,😂 a yayin da su Nura sukace a kamosu, duk wanda ya taho da niyyar fita daga wajen zuwa kamosu Amira sai Amir ya barshi kwance, haka akai ta d'auki ba dad'i.
Sai da ya kashe rabinsu duk yabi ya gaji li'kis, sannan Allah ya basu sa'a a kanshi suka far mishi, saida suka tabbatar da baya numfashi sannan suka fice sukai tafiyarsu suka barshi a nan wajen.
Tunkarar gidan Dad suka yi, a haukarsu wai shine su bisu har gida su kashe su, sedai daga nesa suka hango security's ta ko'ina, hakan ya tabbatar musu da cewa in suka 'karasa lallai za'a kamasu, ba shiri suka juya.
Amira ce ta kalli mahaifinta sannan tace "gaskiya Dad be kamata ba ace Amir ya shiga irin wannan halin ta dalilinmu kuma mu taho mu 'kyale shi, ya kamata mu kai mishi taimako koda da jami'an tsaro ne su taimaka mishi."
Uncle yace "gaskiyarki Amira, bawan Allahn nan ya jefa rayuwarshi cikin had'ari domin kawai ya bamu kulawa da kariya ta ko'ina, be kamata mu 'kyaleshi a haka ba, ya kamata mu sanar da 'yan sanda."
Dad ya kasa magana saboda tsabar firgici da mamaki dake tare dashi har yanzu, ishara kawai yai musu da hannu akan Uncle d'in shi da Amira suje.
Cikin sauri kuwa Amira da Uncle suka shiga mota suka fice harda wasu daga cikin securityn cikin gidan.
Muje zuwa
*🅱K CE*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*INA 'KARA TUNATAR DA MU CEWA BABU FA WANDA ALLAH ZAI HALITTA YACE BAZAI FUSKANCI JARABAWAR UBANGIJI BA, KARMU MANTA ALLAH MUKA RO'KA DA YA ZAB'AR MANA SHUGABA NA GARI A WANCAN SHEKARUN, SAI ALLAH YA ZAB'A MANA BABA BUHARI, TO KO DA ALLAH YA BAMU SHI A TUNANINMU ALLAH BA ZAI JARABCEMU BA TA WANI B'ANGAREN? WALLAHI ALLAH KO DA TSAYAR DA BAMA BAMAI KAD'AI DA BABA BUHARI YAI 'KO'KARIN YI KAD'AI MUKA TUNA YA ISA MU GODEWA ALLAH KUMA MUSAN CEWA LALLAI BA ZALUNCI NE YA KAWO BABA BUHARI CIKIN RAYUWARMU BA, KARMU MANTA KAFIN BUHARI YACI ZAB'E A BAYA A LOKACIN DA GOODLUCK KE MULKARMU BABA BUHARI YASHA ZUBAR DA HAWAYENSA YASHA YIN KUKA KAN HALIN DA 'YAN 'KASA KE CIKI, KAFIN YACI MA KENAN DA YACI KUMA BURINSHI YAGA MUN SAMU CIGABA A RAYUWARMU, KAR MU ZAMA BUTULU A RAYUWA ANATA MAGANAR ABINCI YAI TSADA BAFA RASAWA MUKAI GABA D'AYA BA, KUMA KOWANE TSANANI YANADA IYAKA NA D'AN LOKACI NE KUMA SAI ANSHA WUYA AKE SHAN DAD'I, INACE A BAYA MULKIN GOOD LUCK GA KUD'IN AKWAI GA ABINCIN AMMA BAYA CIYUWA, NA CEFANE MA BASA SAMUWA SABODA FARGABAR KA FITA WAJEN NEMA A HARBEKA KO ASA BOM YA TAYAR DAKAI, KARMU MANTA CEWA ANSHA SAKA BOM A MASALLATAI MUSAN CEWA TABBAS IN MUNA CIGABA DA BARI SHUGABANNI AZZALUMAI NA MULKARMU TO ZA'A WAYI GARI BABU RABINMU SUN KASHE, MUYI TUNANI SOSAI WALLAHI KAR MU BARI 'YAN CANJI NA WANI LOKACI DA ZASU 'KARE SU BARMU DA SHAN WAHALAR SHEKARU SU RUD'EMU, MUYI TUNANI DUK MAI SHIRYA GASKIYA BAZAI BAKA CIN HANCI DAN KA ZABESHI BA, HALIN MUTUM JARINSA HALIN MUTUM KE BAYYANAR DA CANCANTARSA WAJEN JAMA'A, NIDAI NACE INSHA ALLAH 4+4 SAI MAI GASKIYA.*
PAGE 205 to 210
Kai tsaye su Amira wucewa can wajen da abun ya faru sukayi, saboda Uncle yace ba sai sun kira jami'an tsaro ba tunda suna tare da security sun wadatar, kuma jami'an tsaron ma da akwai mugaye da munafukai a ciki wad'anda zasu iya tseguntawa Insp Yahya in sukaji bai mutu ba suzo su 'karasashi, da wannan shawarar ta Uncle sukai amfani sukayi watsi da maganar neman 'yan sanda, cikin 'kan'kanin lokaci Allah ya kaisu wajen, basu tarar da kowa ba a wajen sai Amir yashe a wajen kwance cikin jini, babu b'ata lokaci suka d'aukeshi suka yi asibitin da ake duba iyalen Dad da shi.
Suna zuwa babu wani b'ata lokaci aka shiga dashi emergency cikin sauri saboda ganin harda harbi.
Sai da aka kammala mishi komai aka kuma tabbatar musu da yana raye kuma insha Allah nan da wasu lokuta zai farfad'o sannan hankalinsu ya kwanta musamman ma Amira wadda ta kasa zaune ta kasa tsaye, banda kuka babu abinda takeyi, ita zuciyarta kawai bata takeyi Amir d'inta ya rasu, saida taji bayanin Doctor d'in sannan hankalinta ya kwanta.
Amira cikin sauri ta fad'a d'akin da aka maida Amir, Uncle da Doctor suka bita da ido, Doctor yace "hala wancan majinyacin mijinta ne?" Uncle yace "eh Doctor," Doctor yace "haba shiyasa naga gabad'aya bata cikin hayyacinta," dukkansu sukayi murmushi, sannan ya umurci Uncle da ya bishi office akwai magungunan da za'a nemo da ya tashi a bashi koda ruwan tea ne sai a bashi magungunan yasha, Amira na shiga d'akin ta 'karasa kusa da bakin gadon da yake kwance, kara kanta tayi dai-dai saitin 'kirjinsa ta tabbatar da abinda likita ya fad'a musu sannan ta numfasa kuma ta yarda da ranshi, sai ta samu waje ta zauna.
Nura ya she'ke da dariya sannan yace Dad da tsohuwar matarka suna wajenmu, duk shirinka baka isa ka wargaza namu ba Amir," ana gama fad'in haka aka kashe wayar.
Amir ya kalli Mum yace "kinji ko, to yanzu duk ku fito daga gidan nan muje gidana ku zauna kar kuma su turo ai muku wani abu," saboda sanin halin mai gidan sai suka kasa yarda da abinda Amir yace, haka yaita ro'konsu amma suka 'ki binshi.
Hakan yasa yaiwa bataliyar masu tsaronshi waya kan suzo, yai musu kwatancen unguwar, cikin 'kan'kanin lokaci kuwa suka 'karaso, ya basu umurni kan su kula da mutanen gidan nan kamar yanda zasu kula da shi, sannan ya cewa su Mum da Uncle kar suji tsoro mutanenshi ne.
Amir ya juyo ya fito daga gidan, kai tsaye wucewa mtn office yai kai tsaye domin a binciko mishi daga inda aka kira lambar.
Bayan an kira lambar sai suka sake d'auka wannan karon Insp Yahya ne ya d'aga yana fad'a mishi matarshi da sirikinshi suna sume, kuma sun riga da sun saka hannu da yatsan Dad a sumen yanzu duk abinda ya mallaka a duniya ya zama ba nashi ba, kuma yanzu zasu ba'kunci lahira, sannan ya 'karashe da fad'in " idan ka isa kazo ka taimakesu."
Cikin sauri aka gama tantance inda suke Amir ya karb'i addreshin wajen ya tafi.
Gudu kawai yake a mota yana jin tsoro kar su kashe mishi Amirar shi.
Cikin minti talatin ya 'karaso wajen kuma ya shiga ciki da gudu yana 'kwalawa su Amira kira.
Cikin wani 'katon kango ne, yana shiga can ciki yaga Amira da Dad an d'aure su, cikin sauri ya nufi inda suke, lallab'owa ta baya aka yi aka buga mishi wani abu a baya, take anan ya zube 'kasa, kuma lokaci guda suka kewaye shi, bayan sun mishi dukan tsiya sannan shima aka d'aure shi.
Dad ya kalli Baban Nura yace "yanzu duk irin yardar da nai maka amma shine ka saka min da wannan abun ko, da ikon Allah 'karshenka ba zaiyi kyau ba."
Baban Nura ya she'ke da dariya sannan yace "ai kai ka jawa kanka, ka tsani talaka, sannan kana tsoron had'a komai da talaka, ai na dad'e ina jiran zuwan wannan ranar, duk 'kulawa da 'kaunar da nake maka ba taka bace ta dukiyarka ce, amma wai kai me wayau ka katange komai to muma ga irin namu wayon nan mun nuna maka, albishir biyu yanzu zanyi maka, na farko duk wasu kadarori da suke mallakinka yanzu sun zama namu ni da d'ana hatta gidan da kake ciki mun siyar, abu na biyu kuma shine yanzu zamu 'kara muku gudu zuwa lahira domin barinku a raye zai iya zama mana barazana a cikin sabuwar rayuwar da zamu yi, kuma kaga kaima mun taimaka maka shan takaicin rayuwa cikin talauci, naso dai in barka a raye kaji irin yanda rayuwar talauci take, amma na sanka farin sani sam baka yafiya akan komai."
Insp Yahya ya kalli Baba yace "ni Baba Amir d'in can nake so ku barni in kashe shi da kaina."
Baba da Nura suka she'ke da dariya, sannan suka had'a baki wajen cewa "an baka," sannan su duka ukun harda tarin 'kattan dake cike a wajen suka sake kwashewa da dariya, wurin sai amsawa yake yi.
Baba ya baiwa Nura umurnin kashe su Amiran, sedai Amir na ganin inda Nura ya tunkara hannunsa ri'ke da bindigar Insp Yahya sai yai wani irin tashi yana a d'auren yaje da gudu ya bangaji Nura suka fad'i 'kasa a tare.
Kiciniyar 'kwace bindigar Amir yakeyi daga hannun Nura cikin ikon Allah ya samu d'aurin hannunshi ya kwance ya 'kwace bindigar sannan ya kwance su Amira da Dad yana cikin kwancesu Insp Yahya ya ciro bindigar jami'in dake kusa dashi ya saita Amir da ita tare da harbin Amir d'in a hannu, Amir yai wani irin razanannen 'kara, tare da dafe wajen ya kalli su Dad yace su gudu zai biyosu daga baya, Amira taja ta tsaya tana ri'ke da hannunshi mai ciwon tana kuka tana fad'in "taya zan tafi in barka a irin wannan halin, ni ba inda zanje ko mutuwar ne ma gwara a kashemu tare," Amir ya dafata, sannan yace "ki kwantar da hankalinki Amira Insha Allah rabuwarmu ba yanzu ba, zan dawo gareki nai miki al'kawari."
Cikin sauri kuwa Dad ya jata da gudu suka fice daga wurin nace ashe Dad ansan darajar rai hahaha,😂 a yayin da su Nura sukace a kamosu, duk wanda ya taho da niyyar fita daga wajen zuwa kamosu Amira sai Amir ya barshi kwance, haka akai ta d'auki ba dad'i.
Sai da ya kashe rabinsu duk yabi ya gaji li'kis, sannan Allah ya basu sa'a a kanshi suka far mishi, saida suka tabbatar da baya numfashi sannan suka fice sukai tafiyarsu suka barshi a nan wajen.
Tunkarar gidan Dad suka yi, a haukarsu wai shine su bisu har gida su kashe su, sedai daga nesa suka hango security's ta ko'ina, hakan ya tabbatar musu da cewa in suka 'karasa lallai za'a kamasu, ba shiri suka juya.
Amira ce ta kalli mahaifinta sannan tace "gaskiya Dad be kamata ba ace Amir ya shiga irin wannan halin ta dalilinmu kuma mu taho mu 'kyale shi, ya kamata mu kai mishi taimako koda da jami'an tsaro ne su taimaka mishi."
Uncle yace "gaskiyarki Amira, bawan Allahn nan ya jefa rayuwarshi cikin had'ari domin kawai ya bamu kulawa da kariya ta ko'ina, be kamata mu 'kyaleshi a haka ba, ya kamata mu sanar da 'yan sanda."
Dad ya kasa magana saboda tsabar firgici da mamaki dake tare dashi har yanzu, ishara kawai yai musu da hannu akan Uncle d'in shi da Amira suje.
Cikin sauri kuwa Amira da Uncle suka shiga mota suka fice harda wasu daga cikin securityn cikin gidan.
Muje zuwa
*🅱K CE*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*INA 'KARA TUNATAR DA MU CEWA BABU FA WANDA ALLAH ZAI HALITTA YACE BAZAI FUSKANCI JARABAWAR UBANGIJI BA, KARMU MANTA ALLAH MUKA RO'KA DA YA ZAB'AR MANA SHUGABA NA GARI A WANCAN SHEKARUN, SAI ALLAH YA ZAB'A MANA BABA BUHARI, TO KO DA ALLAH YA BAMU SHI A TUNANINMU ALLAH BA ZAI JARABCEMU BA TA WANI B'ANGAREN? WALLAHI ALLAH KO DA TSAYAR DA BAMA BAMAI KAD'AI DA BABA BUHARI YAI 'KO'KARIN YI KAD'AI MUKA TUNA YA ISA MU GODEWA ALLAH KUMA MUSAN CEWA LALLAI BA ZALUNCI NE YA KAWO BABA BUHARI CIKIN RAYUWARMU BA, KARMU MANTA KAFIN BUHARI YACI ZAB'E A BAYA A LOKACIN DA GOODLUCK KE MULKARMU BABA BUHARI YASHA ZUBAR DA HAWAYENSA YASHA YIN KUKA KAN HALIN DA 'YAN 'KASA KE CIKI, KAFIN YACI MA KENAN DA YACI KUMA BURINSHI YAGA MUN SAMU CIGABA A RAYUWARMU, KAR MU ZAMA BUTULU A RAYUWA ANATA MAGANAR ABINCI YAI TSADA BAFA RASAWA MUKAI GABA D'AYA BA, KUMA KOWANE TSANANI YANADA IYAKA NA D'AN LOKACI NE KUMA SAI ANSHA WUYA AKE SHAN DAD'I, INACE A BAYA MULKIN GOOD LUCK GA KUD'IN AKWAI GA ABINCIN AMMA BAYA CIYUWA, NA CEFANE MA BASA SAMUWA SABODA FARGABAR KA FITA WAJEN NEMA A HARBEKA KO ASA BOM YA TAYAR DAKAI, KARMU MANTA CEWA ANSHA SAKA BOM A MASALLATAI MUSAN CEWA TABBAS IN MUNA CIGABA DA BARI SHUGABANNI AZZALUMAI NA MULKARMU TO ZA'A WAYI GARI BABU RABINMU SUN KASHE, MUYI TUNANI SOSAI WALLAHI KAR MU BARI 'YAN CANJI NA WANI LOKACI DA ZASU 'KARE SU BARMU DA SHAN WAHALAR SHEKARU SU RUD'EMU, MUYI TUNANI DUK MAI SHIRYA GASKIYA BAZAI BAKA CIN HANCI DAN KA ZABESHI BA, HALIN MUTUM JARINSA HALIN MUTUM KE BAYYANAR DA CANCANTARSA WAJEN JAMA'A, NIDAI NACE INSHA ALLAH 4+4 SAI MAI GASKIYA.*
PAGE 205 to 210
Kai tsaye su Amira wucewa can wajen da abun ya faru sukayi, saboda Uncle yace ba sai sun kira jami'an tsaro ba tunda suna tare da security sun wadatar, kuma jami'an tsaron ma da akwai mugaye da munafukai a ciki wad'anda zasu iya tseguntawa Insp Yahya in sukaji bai mutu ba suzo su 'karasashi, da wannan shawarar ta Uncle sukai amfani sukayi watsi da maganar neman 'yan sanda, cikin 'kan'kanin lokaci Allah ya kaisu wajen, basu tarar da kowa ba a wajen sai Amir yashe a wajen kwance cikin jini, babu b'ata lokaci suka d'aukeshi suka yi asibitin da ake duba iyalen Dad da shi.
Suna zuwa babu wani b'ata lokaci aka shiga dashi emergency cikin sauri saboda ganin harda harbi.
Sai da aka kammala mishi komai aka kuma tabbatar musu da yana raye kuma insha Allah nan da wasu lokuta zai farfad'o sannan hankalinsu ya kwanta musamman ma Amira wadda ta kasa zaune ta kasa tsaye, banda kuka babu abinda takeyi, ita zuciyarta kawai bata takeyi Amir d'inta ya rasu, saida taji bayanin Doctor d'in sannan hankalinta ya kwanta.
Amira cikin sauri ta fad'a d'akin da aka maida Amir, Uncle da Doctor suka bita da ido, Doctor yace "hala wancan majinyacin mijinta ne?" Uncle yace "eh Doctor," Doctor yace "haba shiyasa naga gabad'aya bata cikin hayyacinta," dukkansu sukayi murmushi, sannan ya umurci Uncle da ya bishi office akwai magungunan da za'a nemo da ya tashi a bashi koda ruwan tea ne sai a bashi magungunan yasha, Amira na shiga d'akin ta 'karasa kusa da bakin gadon da yake kwance, kara kanta tayi dai-dai saitin 'kirjinsa ta tabbatar da abinda likita ya fad'a musu sannan ta numfasa kuma ta yarda da ranshi, sai ta samu waje ta zauna.