Sashe 11
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan ta gama girkin ta zuba a kula tana jira sai ya tashi su ci tare kamar yanda suka saba.
Amira ta ci gaba da gyara ko'ina na gidan, sannan ta turare ko ina, a tak'aice dai ranar dukkan su ba wanda ya lek'a makaranta, ta fad'a band'aki ta shek'a wanka sannan ta fito, bayan tai wanka ta shirya cikin riga da siket na atamfa wad'anda suka yi matuk'ar yi mata kyau, kuma sun karb'i jikinta sosai, hakan yasa kyawunta ya k'ara fitowa fili ya k'ara bayyana.
Falon ta dawo ta tarar Amir ya tashi amma har lokacin yana kwance, cikin hanzari ta k'arasa kusa da shi ta daga kanshi ta zauna sannan ta maida kanshi jikinta ta kwantar kamar yanda suke a d'azu ta kalle shi tace " sannu Amir ya jikin, Allah k'ara sauk'i, yanzu me ke damunka, ko zamu tafi asibiti ne?"
Amir binta kawai yake da kallo yana mamakinta, gashi dai a haka ta damu da shi amma kuma bata son shi, kallonta ya yi sannan yace " ba sai mun je asibiti ba zazzab'in ya sauka mura ce kawai sai ciwon kai, suma a hankali zasu warware, amma Amira ni maganin dukkanin wata cuta tawa tana wajenki, soyayyarki nake nema kin hana ni ban san dalilin ki na yi min hakan ba."
Amira tace " yanzu dai mu bar wannan maganar har sai kaji Sauk'i," ta zuba musu abinci suka ci, bayan sun gama ta zuba mishi ruwan wanka yaje ya watsa ruwa, bayan ya gama ta bashi t.shet d'inta da jeans yasa duk sun matse shi amma haka nan zai saka tunda nashi sun yi datti, se dai kayan sun yi mishi kyau sosai.
Tun daga ranar kayanta yake sakawa har Allah ya bashi lafiya, yau kwanan shi uku kenan a gidan, tattali kam da gata ya sha shi, hakan ya k'ara sa mishi son mallakar Amira matsayin matar aure.
Yau lahadi ba makaranta, Amir ne zaune gaban Amira ya k'ureta da idanu, kallon shi tayi tace " yallab'ai lafiya kake kallona haka?" Amir ya numfasa sannan yace " Amira bana gajiya da kallon wannan kyakkyawar fuskar, Amira ina sonki k'aunarki ta kama zuciyata, dan Allah ki amince da ni,"
Amira ta share shi tare da kawar da kai, Amir ya taso daga inda yake zaune ya tsugunna a gabanta yana zubar da hawaye sannan ya dafata yace " Amira wallahi in na rasaki mutuwa zan yi, ki taimake ni so nake in mallake ki matsayin matar aure mu yi rayuwa dake ta har abada, ki karb'i tayin soyayyata."
A fusace Amira ta juyo ta sake d'aga hannu ta wanka mishi mari wanda ya fi ukun da tai mishi a baya zafi, sannan sai ta fara kuka itama, zamowa tai daga kan kujera ta tsugunna a gabanshi sannan ta kalli Amir wanda yake dafe da kuncin shi har yanzu yana binta da kallo.
Kama kwalar rigar shi tai kamar zata yi dambe da shi tana jijjiga shi tace " kasan kana sona meyasa zaka b'ata lokaci wajen fad'a min, meyasa ka d'auki tsawon lokaci kafin ka sanar min iyeeeee, kasan iya tsawon lokacin da na d'auka ina jiran zuwan wannan ranar da zaka furta kana sona, to in baka sani ba ka sani tun had'uwar farko yanayin kallonka ya tabbatar min da kana sona, kuma nima tun ranar na kamu da k'aunarka, amma shine zaka tsaya jamin aji, kana turo da sak'onni a b'oye yanzu da ka rasani fa wani ya aureni kasa mun yi asarar juna," jijjiga shi take yi da k'arfi, can sai ta kwantar da kanta a k'irjin shi tana ci gaba da kuka, cikin kukan ta cigaba da fad'in na d'auki alk'awarin hora duk wanda na gano shine me turo min da sak'onni duk da dama zuciyata ta dad'e tana bani cewa kai ne, na so in hukunta ka amma saboda k'aunar da nake maka tai min yawa shi ya hanani yin hukunci a gareka."
Amir kam farin ciki ba'a magana, ko a haka Amira ta tsaya ya san tana k'aunarsa, kusan ma zai iya cewa lokaci d'aya suka kamu da k'aunar juna, d'agota ya yi sannan ya share mata hawayen dake fuskarta, itama ta share mishi na shi, sannan suka kalli juna suka sakarwa junan su murmushi, Amir yace " ai ko a haka aka barni na horu wallahi, amma meyasa kika mareni?" Amira ta kalle shi tace " ladan k'in fad'a min sirrin zuciyarka da ka yi da wuri har sai da k'aunarka ta gama galabaitar da tawa zuciyar sannan ka fad'a min, Allah naji haushin rashin sanar min da ka k'i yi kan lokaci, kuma har kana ikirarin kana k'aunata amma ka iya b'oyewa tsawon lokuta, bayan ni nasan zuciya babu abinda ya kaita tonon asiri, tuni ta bankad'eka na gane kana k'aunata ta yanayin tattalinka, kulawarka, damuwarka a kaina, kawai na zuba maka ido ne ka gama kewaye kewayen ka."
Amir yai murmishi, sannan yace " amma fa gaskiya na maru," Amira tai murmushi itama sannan tace " shine salon naka tukuicin soyayyar," dukkan su suka kwashe da dariya sannan suka rungume juna.
_ina barar addu'arku masoya Allah ya d'orar min da lafiya.👏_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie) ```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛 ```
*MASOYANA INA GODIYA SOSAI DA 'DUMBIN K'AUNAR DA KUKA NUNA A GARENI, ALLAH YA SAKA MUKU DA ALKHAIRI ALLAH YA BIYAKU DA GIDAN ALJANNA FIRDAUSI, NAGODE SOSAI WALLAHI.*
*🇸🇦Zaman amana writer's*
*Tauraronku na haskawa a ko'ina, Allah yai muku baiwa wanda ku da mak'iya se dai kallo, lallai zaman amana alkhairi ce naga nasarorinta cikin rubutu da marubuta, ni fa bance kunfi kowa ba 'yan uwana, amma fa tabbas kunfi wasu wasu kuma sun fiku, dama haka rayuwar take kafi wani wani ya fika, tabbas kuna haskawa ku ake yayi a ko'ina, Allah ya k'ara muku basirar da se dai a kwaikwaya a wajenku, d'aukakar da zata sa a daraja girman matsayinku, d'an karen zak'in hannun da zai sa mutane su mato kan k'aunar novel's d'in ku👏a cigaba da basu mamakin mutanena🤜🤛😍😍😍😍😍*
*Har ila yau marubutan gidan sun sake kawo muku k'ayataccen labarai, RAYUWAR SAUDAT daga marubuciya RAHEENAT M. ABBAKAR, sai MARYAMA CEE daga marubuciya MARYAM KWARE, dukkanin su yanzu aka fara ba'a yi nisa ba karku sake a baku labari wallahi ku da kanku sai kun gode min da wannan albishir d'in muddin kuka karanta su.*
*Dawo masoyiya Tawan dawo wallahi na tuba, laifin da nai ki zamto yafewa wallahi na tuba🙏😩😰*
PAGE 50 to 55
Tun daga wannan ranar Amir da Amira so da k'auna tare da shak'uwa me k'arfi suka k'ara k'ulluwa a tsakanin su.
Yau Litinin, kuma yau ma kamar kullum tare suka shigo cikin makarantar a motar Amira wanda Amir ya tuk'o su, shi kuma tashi tana gidan Amiran sai in zai koma gida yake hawa, wata rana ma har motar canje suke yi, ya d'auki ta-ta itama ta d'auki tashi.
Suna shigowa cikin harabar makarantar sai ya yi fakin a inda ake faka motoci a makarantar, bayan ya kammala suka fito a tare rik'e da hannun juna suka jero zuwa ajin su.
Se dai a hanyar da zata sada su da ajin nasu wasu cincirindon 'yan iskan maza ne sun kai su goma suna zaune duk d'alibar da tazo wucewa sai sun tab'a jikinta, ko sun ci zarafinta da kalaman su, wasu su wuce suna kuka wasu kuma su yi musu Allah ya isa su ruga da gudu, wad'annan bayin Allahn sun yi k'aurin suna wajen rashin ji, shiyasa ma aka rasa me tanka musu suna ta iya shegen su ana kallo, kuma dukkanin su 'ya'yan manya ne ma'ana ''ya'yan masu kud'i ne.
Wata ta wuce kenan sun gama yi mata cin zarafi sannan sai ga su Amira suma sun zo wucewa, nan take suka fara fad'in "ga wata had'ad'd'iyar nan ta taho, gaskiya ta had'u," shugaban tantiran yace "ni wallahi har naji ina sonta," duk su Amir na jinsu har ya motsa hannu Amira ta k'ara rik'e shi, ya kalleta ta girgiza mishi kai, suka cigaba da tafiya, d'aya daga cikin su ya k'ara d'aga murya yace "komai ya ji gaba da baya, gashi daga ganin wannan d'an k'aramin bakin naki to haka can ma yake k'arami," habawa Amir ya fizge hannun shi daga na Amira ya nufo inda suke tare da rufe su da duka musamman ma wanda ya furta wannan kalmar.
Yanda Amir d'in ke dukan kanshi kasan a zuciye yake, dukan su yake da tokari gashi in dai k'arfi ne kam Allah ya hore mishi musamman akan Amira, dama kuma mutum ko rago ne in yaga za'a ci zarafin abinda yake so zama jarumi yake yi, hmm so kenan.
Amira taga Amir yana ta bugun wannan gayen ba ji ba gani yama dena dukan wad'ancan wanda ya furta wad'annan maganganun yake ta bugu sauran duk sun tsere yana niyyar yin kisa, gashi wajen har an cika amma an kasa janye shi daga wajen, da an jashi zai sake jawosu su dawo tare suna rike dashi d'in yana kai duka.
Wani malamin su Amiran duk ya rud'e shima ya kalli Amira dake hawaye hankalinta a tashe yace " dan Allah ki dakatar dashi ke kad'ai ce zaki iya, in ba haka ba zai yi kisa."
Amira ta kutsa cikin wajen tai mishi magana amma ina bai san tana yi ba, sai ta d'aga hannu ta daddage ta sharara mishi kyakkyawan mari lafiyayye guda d'aya, ba shiri ya d'ago rik'e da kumatun yana kallonta, yace " ni kika mara akan wad'annan 'yan iskan, to na barki da su, zanje in yi rayuwata ni kad'ai ba tare da ke ba, saboda muddin muna tare babu wanda zai tab'aki in k'yale, ya nuna wa 'yan iskan hannu wad'anda suka yi jina jina sannan yace ku kuma ku sani muddin ina numfashina kuma ko muna tare da Amira ko bama tare bazan ragawa duk wanda yai k'ok'arin ci mata mutunci ba," yana gama fad'in haka ya juya yai tafiyarsa.
Amira ta ci gaba da gyara ko'ina na gidan, sannan ta turare ko ina, a tak'aice dai ranar dukkan su ba wanda ya lek'a makaranta, ta fad'a band'aki ta shek'a wanka sannan ta fito, bayan tai wanka ta shirya cikin riga da siket na atamfa wad'anda suka yi matuk'ar yi mata kyau, kuma sun karb'i jikinta sosai, hakan yasa kyawunta ya k'ara fitowa fili ya k'ara bayyana.
Falon ta dawo ta tarar Amir ya tashi amma har lokacin yana kwance, cikin hanzari ta k'arasa kusa da shi ta daga kanshi ta zauna sannan ta maida kanshi jikinta ta kwantar kamar yanda suke a d'azu ta kalle shi tace " sannu Amir ya jikin, Allah k'ara sauk'i, yanzu me ke damunka, ko zamu tafi asibiti ne?"
Amir binta kawai yake da kallo yana mamakinta, gashi dai a haka ta damu da shi amma kuma bata son shi, kallonta ya yi sannan yace " ba sai mun je asibiti ba zazzab'in ya sauka mura ce kawai sai ciwon kai, suma a hankali zasu warware, amma Amira ni maganin dukkanin wata cuta tawa tana wajenki, soyayyarki nake nema kin hana ni ban san dalilin ki na yi min hakan ba."
Amira tace " yanzu dai mu bar wannan maganar har sai kaji Sauk'i," ta zuba musu abinci suka ci, bayan sun gama ta zuba mishi ruwan wanka yaje ya watsa ruwa, bayan ya gama ta bashi t.shet d'inta da jeans yasa duk sun matse shi amma haka nan zai saka tunda nashi sun yi datti, se dai kayan sun yi mishi kyau sosai.
Tun daga ranar kayanta yake sakawa har Allah ya bashi lafiya, yau kwanan shi uku kenan a gidan, tattali kam da gata ya sha shi, hakan ya k'ara sa mishi son mallakar Amira matsayin matar aure.
Yau lahadi ba makaranta, Amir ne zaune gaban Amira ya k'ureta da idanu, kallon shi tayi tace " yallab'ai lafiya kake kallona haka?" Amir ya numfasa sannan yace " Amira bana gajiya da kallon wannan kyakkyawar fuskar, Amira ina sonki k'aunarki ta kama zuciyata, dan Allah ki amince da ni,"
Amira ta share shi tare da kawar da kai, Amir ya taso daga inda yake zaune ya tsugunna a gabanta yana zubar da hawaye sannan ya dafata yace " Amira wallahi in na rasaki mutuwa zan yi, ki taimake ni so nake in mallake ki matsayin matar aure mu yi rayuwa dake ta har abada, ki karb'i tayin soyayyata."
A fusace Amira ta juyo ta sake d'aga hannu ta wanka mishi mari wanda ya fi ukun da tai mishi a baya zafi, sannan sai ta fara kuka itama, zamowa tai daga kan kujera ta tsugunna a gabanshi sannan ta kalli Amir wanda yake dafe da kuncin shi har yanzu yana binta da kallo.
Kama kwalar rigar shi tai kamar zata yi dambe da shi tana jijjiga shi tace " kasan kana sona meyasa zaka b'ata lokaci wajen fad'a min, meyasa ka d'auki tsawon lokaci kafin ka sanar min iyeeeee, kasan iya tsawon lokacin da na d'auka ina jiran zuwan wannan ranar da zaka furta kana sona, to in baka sani ba ka sani tun had'uwar farko yanayin kallonka ya tabbatar min da kana sona, kuma nima tun ranar na kamu da k'aunarka, amma shine zaka tsaya jamin aji, kana turo da sak'onni a b'oye yanzu da ka rasani fa wani ya aureni kasa mun yi asarar juna," jijjiga shi take yi da k'arfi, can sai ta kwantar da kanta a k'irjin shi tana ci gaba da kuka, cikin kukan ta cigaba da fad'in na d'auki alk'awarin hora duk wanda na gano shine me turo min da sak'onni duk da dama zuciyata ta dad'e tana bani cewa kai ne, na so in hukunta ka amma saboda k'aunar da nake maka tai min yawa shi ya hanani yin hukunci a gareka."
Amir kam farin ciki ba'a magana, ko a haka Amira ta tsaya ya san tana k'aunarsa, kusan ma zai iya cewa lokaci d'aya suka kamu da k'aunar juna, d'agota ya yi sannan ya share mata hawayen dake fuskarta, itama ta share mishi na shi, sannan suka kalli juna suka sakarwa junan su murmushi, Amir yace " ai ko a haka aka barni na horu wallahi, amma meyasa kika mareni?" Amira ta kalle shi tace " ladan k'in fad'a min sirrin zuciyarka da ka yi da wuri har sai da k'aunarka ta gama galabaitar da tawa zuciyar sannan ka fad'a min, Allah naji haushin rashin sanar min da ka k'i yi kan lokaci, kuma har kana ikirarin kana k'aunata amma ka iya b'oyewa tsawon lokuta, bayan ni nasan zuciya babu abinda ya kaita tonon asiri, tuni ta bankad'eka na gane kana k'aunata ta yanayin tattalinka, kulawarka, damuwarka a kaina, kawai na zuba maka ido ne ka gama kewaye kewayen ka."
Amir yai murmishi, sannan yace " amma fa gaskiya na maru," Amira tai murmushi itama sannan tace " shine salon naka tukuicin soyayyar," dukkan su suka kwashe da dariya sannan suka rungume juna.
_ina barar addu'arku masoya Allah ya d'orar min da lafiya.👏_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie) ```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛 ```
*MASOYANA INA GODIYA SOSAI DA 'DUMBIN K'AUNAR DA KUKA NUNA A GARENI, ALLAH YA SAKA MUKU DA ALKHAIRI ALLAH YA BIYAKU DA GIDAN ALJANNA FIRDAUSI, NAGODE SOSAI WALLAHI.*
*🇸🇦Zaman amana writer's*
*Tauraronku na haskawa a ko'ina, Allah yai muku baiwa wanda ku da mak'iya se dai kallo, lallai zaman amana alkhairi ce naga nasarorinta cikin rubutu da marubuta, ni fa bance kunfi kowa ba 'yan uwana, amma fa tabbas kunfi wasu wasu kuma sun fiku, dama haka rayuwar take kafi wani wani ya fika, tabbas kuna haskawa ku ake yayi a ko'ina, Allah ya k'ara muku basirar da se dai a kwaikwaya a wajenku, d'aukakar da zata sa a daraja girman matsayinku, d'an karen zak'in hannun da zai sa mutane su mato kan k'aunar novel's d'in ku👏a cigaba da basu mamakin mutanena🤜🤛😍😍😍😍😍*
*Har ila yau marubutan gidan sun sake kawo muku k'ayataccen labarai, RAYUWAR SAUDAT daga marubuciya RAHEENAT M. ABBAKAR, sai MARYAMA CEE daga marubuciya MARYAM KWARE, dukkanin su yanzu aka fara ba'a yi nisa ba karku sake a baku labari wallahi ku da kanku sai kun gode min da wannan albishir d'in muddin kuka karanta su.*
*Dawo masoyiya Tawan dawo wallahi na tuba, laifin da nai ki zamto yafewa wallahi na tuba🙏😩😰*
PAGE 50 to 55
Tun daga wannan ranar Amir da Amira so da k'auna tare da shak'uwa me k'arfi suka k'ara k'ulluwa a tsakanin su.
Yau Litinin, kuma yau ma kamar kullum tare suka shigo cikin makarantar a motar Amira wanda Amir ya tuk'o su, shi kuma tashi tana gidan Amiran sai in zai koma gida yake hawa, wata rana ma har motar canje suke yi, ya d'auki ta-ta itama ta d'auki tashi.
Suna shigowa cikin harabar makarantar sai ya yi fakin a inda ake faka motoci a makarantar, bayan ya kammala suka fito a tare rik'e da hannun juna suka jero zuwa ajin su.
Se dai a hanyar da zata sada su da ajin nasu wasu cincirindon 'yan iskan maza ne sun kai su goma suna zaune duk d'alibar da tazo wucewa sai sun tab'a jikinta, ko sun ci zarafinta da kalaman su, wasu su wuce suna kuka wasu kuma su yi musu Allah ya isa su ruga da gudu, wad'annan bayin Allahn sun yi k'aurin suna wajen rashin ji, shiyasa ma aka rasa me tanka musu suna ta iya shegen su ana kallo, kuma dukkanin su 'ya'yan manya ne ma'ana ''ya'yan masu kud'i ne.
Wata ta wuce kenan sun gama yi mata cin zarafi sannan sai ga su Amira suma sun zo wucewa, nan take suka fara fad'in "ga wata had'ad'd'iyar nan ta taho, gaskiya ta had'u," shugaban tantiran yace "ni wallahi har naji ina sonta," duk su Amir na jinsu har ya motsa hannu Amira ta k'ara rik'e shi, ya kalleta ta girgiza mishi kai, suka cigaba da tafiya, d'aya daga cikin su ya k'ara d'aga murya yace "komai ya ji gaba da baya, gashi daga ganin wannan d'an k'aramin bakin naki to haka can ma yake k'arami," habawa Amir ya fizge hannun shi daga na Amira ya nufo inda suke tare da rufe su da duka musamman ma wanda ya furta wannan kalmar.
Yanda Amir d'in ke dukan kanshi kasan a zuciye yake, dukan su yake da tokari gashi in dai k'arfi ne kam Allah ya hore mishi musamman akan Amira, dama kuma mutum ko rago ne in yaga za'a ci zarafin abinda yake so zama jarumi yake yi, hmm so kenan.
Amira taga Amir yana ta bugun wannan gayen ba ji ba gani yama dena dukan wad'ancan wanda ya furta wad'annan maganganun yake ta bugu sauran duk sun tsere yana niyyar yin kisa, gashi wajen har an cika amma an kasa janye shi daga wajen, da an jashi zai sake jawosu su dawo tare suna rike dashi d'in yana kai duka.
Wani malamin su Amiran duk ya rud'e shima ya kalli Amira dake hawaye hankalinta a tashe yace " dan Allah ki dakatar dashi ke kad'ai ce zaki iya, in ba haka ba zai yi kisa."
Amira ta kutsa cikin wajen tai mishi magana amma ina bai san tana yi ba, sai ta d'aga hannu ta daddage ta sharara mishi kyakkyawan mari lafiyayye guda d'aya, ba shiri ya d'ago rik'e da kumatun yana kallonta, yace " ni kika mara akan wad'annan 'yan iskan, to na barki da su, zanje in yi rayuwata ni kad'ai ba tare da ke ba, saboda muddin muna tare babu wanda zai tab'aki in k'yale, ya nuna wa 'yan iskan hannu wad'anda suka yi jina jina sannan yace ku kuma ku sani muddin ina numfashina kuma ko muna tare da Amira ko bama tare bazan ragawa duk wanda yai k'ok'arin ci mata mutunci ba," yana gama fad'in haka ya juya yai tafiyarsa.