Sashe 8
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amira ta harare shi tare da kai mishi duka da hannu ya goce tare da yi mata dariya harda kashe ido d'aya, Amira ta kalle shi tace " ka daina yi min irin wannan wasan bana so, da ka fad'a min gaskiya kana son ganina ne ai zan taho gareka ba sai ka tsoratani da rashin lafiya ba," ganin ranta ya b'aci da yawa yasa ya taso ya duk'a a gabanta yana bata hak'uri amma ta kauda kanta, plet d'in wak'ar d'an kuka ya saka sannan ya kunna mik'ewa tsaye ya yi, wak'ar cikin film d'in na d'an kuka yake rera mata _(abinda nai kiy hak'uri na yi nadama)_ yana rawa a gabanta yana had'a hannaye tare da kakkantarewa tamkar yanda ake yi a cikin wak'ar, duk yanda taso kartai dariya saida ya sata dariya sosai har saida wak'ar ta k'are sannan ya hak'ura da rawar, zama ya yi a gabanta ya tasa ta kamar tv yana kallo, ta kalle shi tace " wallahi ka bani dariya," Amir yace haka nake fatan ki kasance a koda yaushe."
Amira ta sake kallon shi sannan tace " ya k'arfin jikin?" Amir yace " na ji sauk'i nan ne kawai yake min ciwo ya nuna saitin zuciyarsa da hannu, share shi ta yi, tare da mik'ewa zata tafi shima ya tashi yace " naga kin mik'e ina zaki je?"
Amira tace zan tafi gida mana, Amir ya b'ata rai sannan yace " dan Allah karki tafi, idan muna tare wallahi bana so mu rabu koda na minti d'aya ne kuwa," Amira ta kalle shi tace " meyasa?" Amir yace " nima tambayar da nake ta wa kaina kenan, meyasa nake jin hakan a tare dake, yanzu dai abar wannan maganar wannan ne karonki na farko zuwa gida na saboda haka da kaina zan shiga kicin in miki girki, me kike so a dafa miki?" Amira tace " tab' bazan ci kwamacalarka ba bakina ya b'aci, in girki kake so bari in shiga in girka maka," Amir ya kafe kan shi zai yi mata girki haka nan ta hak'ura ta k'yale shi, ya shiga kicin yana aiki a yayin da ya hanata taimaka mishi da komai, bayan wani d'an tak'aitaccen lokaci Amir ya kammala abinda yake girkawa, ya zubo mata sannan ya zuba mata lemo, cikin fargabar yanda bakinta zai b'aci ta kai cokali d'aya bakinta tare da fara yamutsa fuska, a hankali kuma sai ta ware tare da kallon shi, bata ankara ba ta tayar da girkin Amir tas, bayan ta gama ta sha lemo kad'an sannan ta kalle shi tace " ka bani mamaki matuk'a, wallahi ka iya girki, matarka ta huta."
Amir yai karaf yace " to ai kece matar," d'agowa ta yi tare da wurga mishi wani irin kallo mai kama da harara da kuma tuhuma, shima kallonta ya yi tare da rik'e bakin katob'arar da ya yi, a ganinshi ba yanzu bane lokacin bayyana mata abinda ke ranshi, kallonta ya sake yi sannan ya turo baki kamar k'aramin yaro yace " maida wuk'ar wannan fushi da harara haka, to wasa nake yi, 'yar daba kawai, wannan kallon da kike min 'yan daba kad'ai ke yin irin shi," sannan ya murgud'a mata baki.
Girgiza kai Amira ta yi, tare da yin murmushi, a zuciyarta take fad'in tabbas Amir yai gaskiya da yace zai sakata ta manta da duk wata damuwa gashi kuwa ta tabbatar, harga Allah zama da shi yana sata cikin farin ciki a koda yaushe, tana jin dad'in kasancewa tare da shi sosai.
Amira ta duba agogo, sannan ta d'ago ta kalle shi tace " lokaci ya tafi zan koma gida, tun da safe da ka sani na fito ba shiri gashi yanzu har biyu ta yi," Amir ya kalle ta yace " dan Allah karki tafi, ki zauna da zuciyar da take muradin kasancewa da ke a koda yaushe."
Amira ta kalle shi tace " wallahi kana bani mamaki ka fiye rigima sai kace mace, jiya fa muna tare yauma gamu a tare, da yaushe ne bama kasancewa da juna."
Amir yace " shikenan bari in zo in kai ki," Amira tace " a'a ka barshi nafi so ka huta ka k'ara wartsakewa," Amir yace " taya za'ai in wartsake kina tafiya ki barni ni kad'ai, dan Allah karki tafi, wallahi bana so kina yin nesa da ni," kallon shi Amira ta yi sannan tace " wai da gaske kake dama, kai in nace zan zauna sai ka yarda?"
Amir yace " wallahi da gaske nake yi bana so kina yin nesa da ni, kuma duk abinda nake fad'a miki sak'o ne daga zuciyata zuwa ga taki zuciyar."
Amira tace " ka k'ware wajen iya tsara kalamai, da kallon k'urulla da kake yiwa mutane da kuma kalamanka da za'ai gasa a kansu ina tsammanin kai zaka zo na d'aya," Amir yai murmushi karo na farko da ya ji dad'i a ranshi sanadin Amira ta yaba mishi."
Sallama suka yi da shi ya shaida mata yana nan zuwa anjima zai zo su sha hira, tace ya bari sai gobe in Allah ya kaimu lokacin jikin ya k'ara warwarewa, Amir yace " wallahi sai nazo anjima ko zaki kwana kina rok'ona kar nazo ehe," haka ta fito tana dariya ta barshi yana mita tana jiyo shi wai bata so yazo.
Haka suke kasancewa a koda yaushe suna tare, bayan kwana biyu da yamma wajen k'arfe hud'u Amir ya faka motar shi k'ofar gidan Amira, hon ya danna ba tare da ya shiga ba sai gata ta fito, to dama yanzu sun saba kullum zasu fita da yamma suje wurin shak'atawa da sauran wurare dai na jin dad'i da more rayuwa, to duk in zasu yi irin wannan fitar basu cika zuwa a mota ba, da yake daga gidan Amira ba nisa zuwa wajen.
Fitowa Amir ya yi shim daga mota suka d'auki hanya, kowa ya gansu tamkar miji da mata, sun zuba anko kamar had'in baki kayan da Amir yasa shadda ce milk, itama atamfar da ta saka milk d'in yafi yawa a jiki, sun sha anko sunyi kyau sosai, duk inda suka gifta su kawai ake kallo, suna cikin tafiya sai Amira ta hango fura da nono, to ita dama tana masifar son fura da nono, kuma duk inda ta gani bata wucewa sai ta tsaya ta siya, hakan yasa Amira ta nuna wa Amir tace ya jirata taje ta siyo ta dawo, da yake can tsallake ne, dole sai an tsallaka ti-ti sannan za'a k'araso inda me furar take Amir yace " a'a babu inda zaki je, ki jirani in siyo miki in dawo, Amira tace to tsaya ka karb'i kud'in ya harareta sannan yace " kaji son a sani, ai ko banda kud'i a aljihuna ko rigar jikina sai na siyar na se miki abinda kike buk'ata wallahi," Amira tace " ai kuwa duk ranar da kai haka ban jerawa da kai babu riga," juyawa ya yi yana dariya ya tsallaka ti-ti domin siyo mata abinda ta buk'ata, ya juyo zai dawo ya hango wasu maza kewaye da ita, da alamu magana take gaggaya musu, da gudu Amir ya tafi wajen su, wani ne ya d'aga hannu zai mari Amiran a dai-dai Amir ya k'araso kawai ji ya yi an rik'e mishi hannu ta baya Amir be sakin mishi hannu ba saida ya karya, nan fa Allah ya bashi sa'a yai musu shegen duka, yana cikin dukan su 'yan sanda suka k'araso wajen ciki kuwa harda Insp Yahya (kafi k'arfin mugu), kallon kallo suka yi tsakanin Amir da Insp Yahya, can sai Yahya ya baiwa jami'an umurnin su tafi da su station gaba d'aya, haka kuwa aka yi, aka sa su a mota sai station.
Dukkan su a tsugunne suke gaban Insp Yahya yana kallon su d'aya bayan d'aya, sai da yaji duk abinda ya faru, kuma dama tun a can ya yi bincike an tabbatar mishi da cewa Amir ne ya hau dukan su saboda kawai sun kula Amira.
Dukkan su cikin sel aka gark'ama su, Amira tana ta faman rok'on sa akan cewa ya yi hak'uri dan Allah ba zai sake ba, Insp Yahya ya kalleta yace " ai bazan iya sakin d'aya in bar d'aya ba, se dai in duka zakiy belin su to," Amira tace "eh na yarda a bani belin d'in su gabad'aya," saka wa ya yi a fito da su, sannan suka saka hannu d'aya bayan d'aya kan in suka sake sai an hukunta su hukunci mai tsanani, ya sallame su, amma banda Amir da Amira.
Bayan sauran sun tafi Insp Yahya ya kalli Amir yace " wai kai menene alak'arka da wannan yarinyar ne," Amir kai tsaye yace " sonta nake kuma aurenta zan yi, Insp Yahya yace " ai naga alama tun kafin ka fad'i, to wannan dalilin ne yasa ka shek'e samarinta har biyu?" Amir yace " yallab'ai kawai dan na yi soyayya da Amira sai ya zama laifi har ana tuhumata da aikata kisa, kenan duk wanda ya yi soyayya da ita tuhumar kisa zaku yi mishi, kiji fa abinda d'an sandan nan ke fad'i Amira, " ya juya yana yi wa Amira magana.
Amira ita kanta bata ji dad'in maganar da Insp ya fad'a wa Amir ba, ta kalli Insp tace " yallab'ai a tunani tunda an riga an gano mai laifin har an hukunta shi to be dace kana tuhumar wani daban ba kuma babu shaida ba komai, mun gode da taimakon da kai mana a yau," ta kalli Amir tace suje.
Amira ta sake kallon shi sannan tace " ya k'arfin jikin?" Amir yace " na ji sauk'i nan ne kawai yake min ciwo ya nuna saitin zuciyarsa da hannu, share shi ta yi, tare da mik'ewa zata tafi shima ya tashi yace " naga kin mik'e ina zaki je?"
Amira tace zan tafi gida mana, Amir ya b'ata rai sannan yace " dan Allah karki tafi, idan muna tare wallahi bana so mu rabu koda na minti d'aya ne kuwa," Amira ta kalle shi tace " meyasa?" Amir yace " nima tambayar da nake ta wa kaina kenan, meyasa nake jin hakan a tare dake, yanzu dai abar wannan maganar wannan ne karonki na farko zuwa gida na saboda haka da kaina zan shiga kicin in miki girki, me kike so a dafa miki?" Amira tace " tab' bazan ci kwamacalarka ba bakina ya b'aci, in girki kake so bari in shiga in girka maka," Amir ya kafe kan shi zai yi mata girki haka nan ta hak'ura ta k'yale shi, ya shiga kicin yana aiki a yayin da ya hanata taimaka mishi da komai, bayan wani d'an tak'aitaccen lokaci Amir ya kammala abinda yake girkawa, ya zubo mata sannan ya zuba mata lemo, cikin fargabar yanda bakinta zai b'aci ta kai cokali d'aya bakinta tare da fara yamutsa fuska, a hankali kuma sai ta ware tare da kallon shi, bata ankara ba ta tayar da girkin Amir tas, bayan ta gama ta sha lemo kad'an sannan ta kalle shi tace " ka bani mamaki matuk'a, wallahi ka iya girki, matarka ta huta."
Amir yai karaf yace " to ai kece matar," d'agowa ta yi tare da wurga mishi wani irin kallo mai kama da harara da kuma tuhuma, shima kallonta ya yi tare da rik'e bakin katob'arar da ya yi, a ganinshi ba yanzu bane lokacin bayyana mata abinda ke ranshi, kallonta ya sake yi sannan ya turo baki kamar k'aramin yaro yace " maida wuk'ar wannan fushi da harara haka, to wasa nake yi, 'yar daba kawai, wannan kallon da kike min 'yan daba kad'ai ke yin irin shi," sannan ya murgud'a mata baki.
Girgiza kai Amira ta yi, tare da yin murmushi, a zuciyarta take fad'in tabbas Amir yai gaskiya da yace zai sakata ta manta da duk wata damuwa gashi kuwa ta tabbatar, harga Allah zama da shi yana sata cikin farin ciki a koda yaushe, tana jin dad'in kasancewa tare da shi sosai.
Amira ta duba agogo, sannan ta d'ago ta kalle shi tace " lokaci ya tafi zan koma gida, tun da safe da ka sani na fito ba shiri gashi yanzu har biyu ta yi," Amir ya kalle ta yace " dan Allah karki tafi, ki zauna da zuciyar da take muradin kasancewa da ke a koda yaushe."
Amira ta kalle shi tace " wallahi kana bani mamaki ka fiye rigima sai kace mace, jiya fa muna tare yauma gamu a tare, da yaushe ne bama kasancewa da juna."
Amir yace " shikenan bari in zo in kai ki," Amira tace " a'a ka barshi nafi so ka huta ka k'ara wartsakewa," Amir yace " taya za'ai in wartsake kina tafiya ki barni ni kad'ai, dan Allah karki tafi, wallahi bana so kina yin nesa da ni," kallon shi Amira ta yi sannan tace " wai da gaske kake dama, kai in nace zan zauna sai ka yarda?"
Amir yace " wallahi da gaske nake yi bana so kina yin nesa da ni, kuma duk abinda nake fad'a miki sak'o ne daga zuciyata zuwa ga taki zuciyar."
Amira tace " ka k'ware wajen iya tsara kalamai, da kallon k'urulla da kake yiwa mutane da kuma kalamanka da za'ai gasa a kansu ina tsammanin kai zaka zo na d'aya," Amir yai murmushi karo na farko da ya ji dad'i a ranshi sanadin Amira ta yaba mishi."
Sallama suka yi da shi ya shaida mata yana nan zuwa anjima zai zo su sha hira, tace ya bari sai gobe in Allah ya kaimu lokacin jikin ya k'ara warwarewa, Amir yace " wallahi sai nazo anjima ko zaki kwana kina rok'ona kar nazo ehe," haka ta fito tana dariya ta barshi yana mita tana jiyo shi wai bata so yazo.
Haka suke kasancewa a koda yaushe suna tare, bayan kwana biyu da yamma wajen k'arfe hud'u Amir ya faka motar shi k'ofar gidan Amira, hon ya danna ba tare da ya shiga ba sai gata ta fito, to dama yanzu sun saba kullum zasu fita da yamma suje wurin shak'atawa da sauran wurare dai na jin dad'i da more rayuwa, to duk in zasu yi irin wannan fitar basu cika zuwa a mota ba, da yake daga gidan Amira ba nisa zuwa wajen.
Fitowa Amir ya yi shim daga mota suka d'auki hanya, kowa ya gansu tamkar miji da mata, sun zuba anko kamar had'in baki kayan da Amir yasa shadda ce milk, itama atamfar da ta saka milk d'in yafi yawa a jiki, sun sha anko sunyi kyau sosai, duk inda suka gifta su kawai ake kallo, suna cikin tafiya sai Amira ta hango fura da nono, to ita dama tana masifar son fura da nono, kuma duk inda ta gani bata wucewa sai ta tsaya ta siya, hakan yasa Amira ta nuna wa Amir tace ya jirata taje ta siyo ta dawo, da yake can tsallake ne, dole sai an tsallaka ti-ti sannan za'a k'araso inda me furar take Amir yace " a'a babu inda zaki je, ki jirani in siyo miki in dawo, Amira tace to tsaya ka karb'i kud'in ya harareta sannan yace " kaji son a sani, ai ko banda kud'i a aljihuna ko rigar jikina sai na siyar na se miki abinda kike buk'ata wallahi," Amira tace " ai kuwa duk ranar da kai haka ban jerawa da kai babu riga," juyawa ya yi yana dariya ya tsallaka ti-ti domin siyo mata abinda ta buk'ata, ya juyo zai dawo ya hango wasu maza kewaye da ita, da alamu magana take gaggaya musu, da gudu Amir ya tafi wajen su, wani ne ya d'aga hannu zai mari Amiran a dai-dai Amir ya k'araso kawai ji ya yi an rik'e mishi hannu ta baya Amir be sakin mishi hannu ba saida ya karya, nan fa Allah ya bashi sa'a yai musu shegen duka, yana cikin dukan su 'yan sanda suka k'araso wajen ciki kuwa harda Insp Yahya (kafi k'arfin mugu), kallon kallo suka yi tsakanin Amir da Insp Yahya, can sai Yahya ya baiwa jami'an umurnin su tafi da su station gaba d'aya, haka kuwa aka yi, aka sa su a mota sai station.
Dukkan su a tsugunne suke gaban Insp Yahya yana kallon su d'aya bayan d'aya, sai da yaji duk abinda ya faru, kuma dama tun a can ya yi bincike an tabbatar mishi da cewa Amir ne ya hau dukan su saboda kawai sun kula Amira.
Dukkan su cikin sel aka gark'ama su, Amira tana ta faman rok'on sa akan cewa ya yi hak'uri dan Allah ba zai sake ba, Insp Yahya ya kalleta yace " ai bazan iya sakin d'aya in bar d'aya ba, se dai in duka zakiy belin su to," Amira tace "eh na yarda a bani belin d'in su gabad'aya," saka wa ya yi a fito da su, sannan suka saka hannu d'aya bayan d'aya kan in suka sake sai an hukunta su hukunci mai tsanani, ya sallame su, amma banda Amir da Amira.
Bayan sauran sun tafi Insp Yahya ya kalli Amir yace " wai kai menene alak'arka da wannan yarinyar ne," Amir kai tsaye yace " sonta nake kuma aurenta zan yi, Insp Yahya yace " ai naga alama tun kafin ka fad'i, to wannan dalilin ne yasa ka shek'e samarinta har biyu?" Amir yace " yallab'ai kawai dan na yi soyayya da Amira sai ya zama laifi har ana tuhumata da aikata kisa, kenan duk wanda ya yi soyayya da ita tuhumar kisa zaku yi mishi, kiji fa abinda d'an sandan nan ke fad'i Amira, " ya juya yana yi wa Amira magana.
Amira ita kanta bata ji dad'in maganar da Insp ya fad'a wa Amir ba, ta kalli Insp tace " yallab'ai a tunani tunda an riga an gano mai laifin har an hukunta shi to be dace kana tuhumar wani daban ba kuma babu shaida ba komai, mun gode da taimakon da kai mana a yau," ta kalli Amir tace suje.