Sashe 33
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amira ta zaunar da shi sannan ta fad'a jikinshi ta fashe da wani irin kuka, shima kukan yake tare da 'kara rungumeta yana fad'in "wallahi Amira banso na rasaki, a ina zanga iyayena in kawosu kar a rabani da ke," ya sake fashewa da kuka kamar 'karamin yaro.
Amira tana rungume dashi itama tace "abinda na gudar mana kenan tun farko Amir d'ina shiyasa nace kar mu zo, ni nasan so ake kawai a rabamu shiyasa aka b'ullo da wannan maganar.
Amir ya sake 'kan'kameta kai kace saceta za'ai, yace "Amira 'kaunarki itace bugun numfashina, sonki shine *Mahad'in rayuwata* ana rabamu numfashina zai tsaya ya daina aiki, dan Allah karki yarda a rabamu, Amira bansan iyayena ba ta ina zan fara."
Amira cikin kuka itama tace "Amir d'ina babu mai rabamu sai Allah, shi kad'ai zai iya rabamu domin shi ya nufemu da had'uwa, to me zaisa ka damu tunda muna da tabbas akan yana tare da mu."
A ranar dai haka suka kwana ba bacci musamman Amir, gwara Amira rashin baccin Amir d'in shi ya dakatar da nata, dan har ta fara baccin, minti biyar da farawarta ta farka ta ganshi a kan dadduma yana addu'a yana rusa kuka, dole ta ha'kura da baccin, kuma tai 'ko'karin danne nata damuwar domin kwantar mishi da hankali.
haka Amira ta kwantar da Amir a jikinta kan cinyarta taita rarrashinsa, har Allah yasa bacci yai awon gaba da shi, Amira ta 'kura mishi ido, wani irin tausayinshi yana 'kara ratsa zuciyarta, tunani take yi, ita kanta ta san Amir na yi mata so na ban mamaki, tasan a yanzu tashin hankalinsa da kuma damuwarsa da dalilin kukansa shine ina zaiga iyayensa kar a rabamu, duk duniya babu abinda yake tsoro sama da duk wani abinda zai rabamu, hawayen idanunta ta share tana cigaba da kallonsa, 'kaunarsa na 'kara ratsa ko'ina na jikinta.
Haka Amira ta kwana a zaune bata runtsa ba, ta kasa koda 'kwa'k'kwaran motsi saboda kar baccin Amir d'inta ya yanke.
Sai da Asuba ta tashe shi suka yi Alwala sukai sallah a tare, bayan sun idar tare da yin doguwar addu'a, sannan Amira ta kwanta, Amir kuwa yana zaune kan dadduma zai fara sana'ar tasa wato tunani sai tai sauri ta sa hannunta ta jawoshi ya kwanta kusa da ita, fuskarsu tana fuskantar juna, Amira tace kai bacci karna sake ganinka kayi tunani banso, yanda ta b'ata rai da yanayin yanda tai maganar yasa Amir yin murmushi, Amira tace "yauwa ko kai fa, nafi so fara'arka ta dawo dan baka kyau sam in ba walwala a fuskarka," suka koma bacci abinsu.
Washe gari wajen 'karfe goma suka tashi, suka tarar har an shigo musu da abin karyawa, Wanka suka yi da wanke baki, sai da suka shirya tsaf sannan suka zauna karyawa.
Bayan sun gama karyawa Amir yace su sauka suje su gaishe da su Dad, tace "to," suka mi'ke lokaci d'aya a tare, Amira taji dad'i a ranta yanda taga Amir na daraja iyayenta duk da kora da halin da suka yi mishi jiya, kuma taji dad'i yanda taga ya fara sakin ranshi.
Sun taki sa'a kuwa suna falo dukkansu, suka bisu d'aya bayan d'aya suka gaishe da su.
Bayan sun gama gaisawa Dad yai gyaran murya sannan yace "Amir kayi ha'kuri kar kaji haushina kan hukuncin da na yanke a kanka, matsayinmu na iyaye wajibi ne muyi bincike kanka kuma mu san wani naka, in kayi tunani kai kanka gata nai maka, kuma kaga nima mutuncina be zube ba matsayina na shugaban 'kasa, kasan zab'e ya kusa 'yan adawa kad'an suke jira su b'ataka a idon jama'a."
Amir yace "wallahi ko kad'an banga laifinka ba Dad, kowane uba hukuncin da ka yanke shi zai yanke, kuma muna 'kara baka ha'kuri kan abinda suka faru a baya dan Allah ka yafe mana, kuma nagode da damar da ka bani, kuma daga yanzu ma zan fara 'ko'karin nemansu insha Allah."
Dad yace "ai tuni na yafe muku yarona, Allah ya taimakeka, duk taimakon da kake nema kar kaji nauyin tambayata ko ka sanar da Amira ta fad'a min, Allah yai muku albarka," dukkansu suka ce "Ameen."
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 140 to 145
Suna gama magana yai sallama da su kan zai tafi ya fara bincike akan asalin nashi, Amira ce ta d'ago kai cikin sauri ta kalle shi tana mamaki, domin ta san ita basu yi wannan maganar ba a d'aki, yanzu ya 'kir'kiro da ita, suna had'a idanu ya fakaici idanun mutane yai mata murmushi tare da gwalo a lokaci d'aya.
Tashi yai dukkansu suka yi mishi fatan alkhairi, ya kama hanya ya fice daga gidan.
Yana fita ya d'auki hanya Amira itama ta haye sama ta d'auki wayarta tare da antaya wa lambarsa kira, har ya fita daga gidan gaba d'aya ya fara tafiya yana tunani da mamakin bataliyar security da aka 'karo, yasan ba akan komai bane sai a kansu shi da Amira, yana cikin wannan tunanin ne yaji wayarsa tana bada sautin 'kara me d'an karen dad'i, murmushi yayi domin yasan me kiran tunda ita kad'ai ya sakawa wannan ringing tone d'in, ciro wayar yayi, sannan ya d'aga tare da karata a kunne.
Kafin yai magana ta balbale shi da fad'a, " yaushe muka yi maganar zaka fita daga zuwan mu zaka fita wani yawonka da sunan yin bincike, in ba yawo ba ina zaka je wa zaka tambaya, to wallahi kar kaga kai mijina ne zan iya hukuntaka, kuma ko yanzu ba 'kyaleka zanyi ba, ba zaka ci abincina ba, kuma ba zaka ga walwalata ba, kuma sai kayi tsallen kwad'o," tana gama fad'in haka ta katse wayar, Amir ya kwashe da dariya domin shi maganarta dariya suka bashi, ya maida wayarsa aljihu ya cigaba da tafiyar shi.
Yana cikin tafiya yaji message ya shigo, yana dubawa yaga Amira ce, cikin sauri ya duba.
_Na duba harabar gidan naga motata tana nan baka fita da ita ba, ka dawo ka d'auka banson tafiyar 'kasa malam ko cemaka aka yi bana kishinka, kuma wallahi ka ri'ke min amanar kanka, duk macen da ta kalleka ka mareta ni na saka._
Amir ya ci dariya kamar me, sannan ya dawo dolen shi tunda basa musa wa junan su, ya d'auki motar ya tafi, yana cikin tafiya yana tuno da diramar matarshi shi kad'ai yana dariya.
A haka ya kasance cikin walwala da farin ciki har Allah ya kawo shi inda zai zo.
Ya bud'e 'kofa zai fito ya sake jin wani 'karar message d'in, ya fito da wayar ya duba
_Duk da ina fushi da kai ban isa hana zuciyata kewa da tunaninka ba, nayi kewarka mijina._
_'Kalubalenku mata ma'aurata, ni abinda ke d'auremin kai da wasu matan auren shine dan girman Allah in baki samar wa da mijinki farin ciki ba a lokacin da yake cikin gida da kuma idan ya fito wa kike so ta bashi? anya kina iya nunawa mijinki kin damu dashi, kina gwada mishi so da 'kauna kuwa koda ace kina fushi dashi ne? to ai bari kuji hikimar yin hakan shine in har kina yin hakan to wallahi tunaninki a ransa ba zai tab'a barinsa ba, ko mata dubu ya aura sai kin fita daban a cikinsu, saboda kulawarki takice ke d'aya babu kishiyar da zata kama 'kafarki, ga dai Amir nan ya fito kamar zararre a mota sai dariya yake, wacece sanadi? matarsa, to da a 'kasa ya taho yasin d'auka za'ai mahaukaci ne, haka ya kamata ki zauta shi ya zama baida wani sauran tunani sai naki, Allah yasa mu dace._
Amir ya dakata da fitowa daga motar ya fara bata amsa kamar haka.
_Amanarki na ri'ke Amirata, kuma kema kinsan duk halin da kike ciki dole nima in tsinci kaina a ciki, domin kuwa zuciyoyin mu a had'e suke, gangar jikina ne kawai bata tare dake, amma zuciyata tana wajenki, domin kuwa tunaninki take, ki kular min da kanki kinji, bazan dad'e ba zan dawo gareki ko zuciyata ta huta daga tunani da kuma kewarki, ina sonki,_
_daga mijinki AMIR._
Yana gama rubutawa ya tura mata, sannan ya fito daga motar, unguwar yake kallo, tare da 'karewa gidan da ya taso rayuwa a cikinsa, ba ko wane gida bane illah gidan da wannan mutumin ya ri'ke shi, yasan Allah yai mishi rasuwa, amma yazo tambayar ma'kwabtansa ne da abokansa ko Allah zaisa ya samu wanda ya san daga inda ya fito.
Amir ya fara da wani shago dake kusa da gidan, da sallamarsa ya 'karasa shagon, me shagon wani dattijo ne ya amsa mishi, dattijon nan abokin mari'kinshi ne, shiyasa yazo wajen shi ko yana da wani labari a kansa.
Bayan sun gaisa Amir yace "Baba ka gane ni kuwa?" Baba yace "a'a yaro, ban shaida ka ba," Amir yace "Amir ne yaron marigayi me can gidan," ya nuna mishi gidan da hannu.
'Dan tsohon nan ya zaro idanu, sannan yace "wai kana nufin Ameeru ne wannan a gabana?"
Amir yai murmushi, shi sam yama manta sunan shi Ameeru a da, yace " eh ni ne Baba," Baba yace "Allah mai iko, Ameeru kai ne ka zama kyakkyawan bature haka," Amir yai dariya, nan suka sake sabuwar gaisuwa, sannan Amir yai gyaran murya yace "Baba akwai abinda ke tafe dani wajenka," Baba yace "to ina jinka Ameeru, Amir yace "zuwa nayi inji ko kasan wani abu game da labarina, ina nufin inda mari'kina ya sameni, ko kuma ajiyata aka kawo mishi?"
Amira tana rungume dashi itama tace "abinda na gudar mana kenan tun farko Amir d'ina shiyasa nace kar mu zo, ni nasan so ake kawai a rabamu shiyasa aka b'ullo da wannan maganar.
Amir ya sake 'kan'kameta kai kace saceta za'ai, yace "Amira 'kaunarki itace bugun numfashina, sonki shine *Mahad'in rayuwata* ana rabamu numfashina zai tsaya ya daina aiki, dan Allah karki yarda a rabamu, Amira bansan iyayena ba ta ina zan fara."
Amira cikin kuka itama tace "Amir d'ina babu mai rabamu sai Allah, shi kad'ai zai iya rabamu domin shi ya nufemu da had'uwa, to me zaisa ka damu tunda muna da tabbas akan yana tare da mu."
A ranar dai haka suka kwana ba bacci musamman Amir, gwara Amira rashin baccin Amir d'in shi ya dakatar da nata, dan har ta fara baccin, minti biyar da farawarta ta farka ta ganshi a kan dadduma yana addu'a yana rusa kuka, dole ta ha'kura da baccin, kuma tai 'ko'karin danne nata damuwar domin kwantar mishi da hankali.
haka Amira ta kwantar da Amir a jikinta kan cinyarta taita rarrashinsa, har Allah yasa bacci yai awon gaba da shi, Amira ta 'kura mishi ido, wani irin tausayinshi yana 'kara ratsa zuciyarta, tunani take yi, ita kanta ta san Amir na yi mata so na ban mamaki, tasan a yanzu tashin hankalinsa da kuma damuwarsa da dalilin kukansa shine ina zaiga iyayensa kar a rabamu, duk duniya babu abinda yake tsoro sama da duk wani abinda zai rabamu, hawayen idanunta ta share tana cigaba da kallonsa, 'kaunarsa na 'kara ratsa ko'ina na jikinta.
Haka Amira ta kwana a zaune bata runtsa ba, ta kasa koda 'kwa'k'kwaran motsi saboda kar baccin Amir d'inta ya yanke.
Sai da Asuba ta tashe shi suka yi Alwala sukai sallah a tare, bayan sun idar tare da yin doguwar addu'a, sannan Amira ta kwanta, Amir kuwa yana zaune kan dadduma zai fara sana'ar tasa wato tunani sai tai sauri ta sa hannunta ta jawoshi ya kwanta kusa da ita, fuskarsu tana fuskantar juna, Amira tace kai bacci karna sake ganinka kayi tunani banso, yanda ta b'ata rai da yanayin yanda tai maganar yasa Amir yin murmushi, Amira tace "yauwa ko kai fa, nafi so fara'arka ta dawo dan baka kyau sam in ba walwala a fuskarka," suka koma bacci abinsu.
Washe gari wajen 'karfe goma suka tashi, suka tarar har an shigo musu da abin karyawa, Wanka suka yi da wanke baki, sai da suka shirya tsaf sannan suka zauna karyawa.
Bayan sun gama karyawa Amir yace su sauka suje su gaishe da su Dad, tace "to," suka mi'ke lokaci d'aya a tare, Amira taji dad'i a ranta yanda taga Amir na daraja iyayenta duk da kora da halin da suka yi mishi jiya, kuma taji dad'i yanda taga ya fara sakin ranshi.
Sun taki sa'a kuwa suna falo dukkansu, suka bisu d'aya bayan d'aya suka gaishe da su.
Bayan sun gama gaisawa Dad yai gyaran murya sannan yace "Amir kayi ha'kuri kar kaji haushina kan hukuncin da na yanke a kanka, matsayinmu na iyaye wajibi ne muyi bincike kanka kuma mu san wani naka, in kayi tunani kai kanka gata nai maka, kuma kaga nima mutuncina be zube ba matsayina na shugaban 'kasa, kasan zab'e ya kusa 'yan adawa kad'an suke jira su b'ataka a idon jama'a."
Amir yace "wallahi ko kad'an banga laifinka ba Dad, kowane uba hukuncin da ka yanke shi zai yanke, kuma muna 'kara baka ha'kuri kan abinda suka faru a baya dan Allah ka yafe mana, kuma nagode da damar da ka bani, kuma daga yanzu ma zan fara 'ko'karin nemansu insha Allah."
Dad yace "ai tuni na yafe muku yarona, Allah ya taimakeka, duk taimakon da kake nema kar kaji nauyin tambayata ko ka sanar da Amira ta fad'a min, Allah yai muku albarka," dukkansu suka ce "Ameen."
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 140 to 145
Suna gama magana yai sallama da su kan zai tafi ya fara bincike akan asalin nashi, Amira ce ta d'ago kai cikin sauri ta kalle shi tana mamaki, domin ta san ita basu yi wannan maganar ba a d'aki, yanzu ya 'kir'kiro da ita, suna had'a idanu ya fakaici idanun mutane yai mata murmushi tare da gwalo a lokaci d'aya.
Tashi yai dukkansu suka yi mishi fatan alkhairi, ya kama hanya ya fice daga gidan.
Yana fita ya d'auki hanya Amira itama ta haye sama ta d'auki wayarta tare da antaya wa lambarsa kira, har ya fita daga gidan gaba d'aya ya fara tafiya yana tunani da mamakin bataliyar security da aka 'karo, yasan ba akan komai bane sai a kansu shi da Amira, yana cikin wannan tunanin ne yaji wayarsa tana bada sautin 'kara me d'an karen dad'i, murmushi yayi domin yasan me kiran tunda ita kad'ai ya sakawa wannan ringing tone d'in, ciro wayar yayi, sannan ya d'aga tare da karata a kunne.
Kafin yai magana ta balbale shi da fad'a, " yaushe muka yi maganar zaka fita daga zuwan mu zaka fita wani yawonka da sunan yin bincike, in ba yawo ba ina zaka je wa zaka tambaya, to wallahi kar kaga kai mijina ne zan iya hukuntaka, kuma ko yanzu ba 'kyaleka zanyi ba, ba zaka ci abincina ba, kuma ba zaka ga walwalata ba, kuma sai kayi tsallen kwad'o," tana gama fad'in haka ta katse wayar, Amir ya kwashe da dariya domin shi maganarta dariya suka bashi, ya maida wayarsa aljihu ya cigaba da tafiyar shi.
Yana cikin tafiya yaji message ya shigo, yana dubawa yaga Amira ce, cikin sauri ya duba.
_Na duba harabar gidan naga motata tana nan baka fita da ita ba, ka dawo ka d'auka banson tafiyar 'kasa malam ko cemaka aka yi bana kishinka, kuma wallahi ka ri'ke min amanar kanka, duk macen da ta kalleka ka mareta ni na saka._
Amir ya ci dariya kamar me, sannan ya dawo dolen shi tunda basa musa wa junan su, ya d'auki motar ya tafi, yana cikin tafiya yana tuno da diramar matarshi shi kad'ai yana dariya.
A haka ya kasance cikin walwala da farin ciki har Allah ya kawo shi inda zai zo.
Ya bud'e 'kofa zai fito ya sake jin wani 'karar message d'in, ya fito da wayar ya duba
_Duk da ina fushi da kai ban isa hana zuciyata kewa da tunaninka ba, nayi kewarka mijina._
_'Kalubalenku mata ma'aurata, ni abinda ke d'auremin kai da wasu matan auren shine dan girman Allah in baki samar wa da mijinki farin ciki ba a lokacin da yake cikin gida da kuma idan ya fito wa kike so ta bashi? anya kina iya nunawa mijinki kin damu dashi, kina gwada mishi so da 'kauna kuwa koda ace kina fushi dashi ne? to ai bari kuji hikimar yin hakan shine in har kina yin hakan to wallahi tunaninki a ransa ba zai tab'a barinsa ba, ko mata dubu ya aura sai kin fita daban a cikinsu, saboda kulawarki takice ke d'aya babu kishiyar da zata kama 'kafarki, ga dai Amir nan ya fito kamar zararre a mota sai dariya yake, wacece sanadi? matarsa, to da a 'kasa ya taho yasin d'auka za'ai mahaukaci ne, haka ya kamata ki zauta shi ya zama baida wani sauran tunani sai naki, Allah yasa mu dace._
Amir ya dakata da fitowa daga motar ya fara bata amsa kamar haka.
_Amanarki na ri'ke Amirata, kuma kema kinsan duk halin da kike ciki dole nima in tsinci kaina a ciki, domin kuwa zuciyoyin mu a had'e suke, gangar jikina ne kawai bata tare dake, amma zuciyata tana wajenki, domin kuwa tunaninki take, ki kular min da kanki kinji, bazan dad'e ba zan dawo gareki ko zuciyata ta huta daga tunani da kuma kewarki, ina sonki,_
_daga mijinki AMIR._
Yana gama rubutawa ya tura mata, sannan ya fito daga motar, unguwar yake kallo, tare da 'karewa gidan da ya taso rayuwa a cikinsa, ba ko wane gida bane illah gidan da wannan mutumin ya ri'ke shi, yasan Allah yai mishi rasuwa, amma yazo tambayar ma'kwabtansa ne da abokansa ko Allah zaisa ya samu wanda ya san daga inda ya fito.
Amir ya fara da wani shago dake kusa da gidan, da sallamarsa ya 'karasa shagon, me shagon wani dattijo ne ya amsa mishi, dattijon nan abokin mari'kinshi ne, shiyasa yazo wajen shi ko yana da wani labari a kansa.
Bayan sun gaisa Amir yace "Baba ka gane ni kuwa?" Baba yace "a'a yaro, ban shaida ka ba," Amir yace "Amir ne yaron marigayi me can gidan," ya nuna mishi gidan da hannu.
'Dan tsohon nan ya zaro idanu, sannan yace "wai kana nufin Ameeru ne wannan a gabana?"
Amir yai murmushi, shi sam yama manta sunan shi Ameeru a da, yace " eh ni ne Baba," Baba yace "Allah mai iko, Ameeru kai ne ka zama kyakkyawan bature haka," Amir yai dariya, nan suka sake sabuwar gaisuwa, sannan Amir yai gyaran murya yace "Baba akwai abinda ke tafe dani wajenka," Baba yace "to ina jinka Ameeru, Amir yace "zuwa nayi inji ko kasan wani abu game da labarina, ina nufin inda mari'kina ya sameni, ko kuma ajiyata aka kawo mishi?"