Sashe 19
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amira tace " ina saurarenka," Amir yace " _tunda naga wasik'arki kuma naga Dad yak'i bari muyi sallama nasan tabbas ba zaki dawo ba naci kuka kamar me, amma ina ganin wannan kud'in sai tunanin biyoki kano yazo raina, amma na fara tunanin be kamata na rik'a yawo da kud'in a haka ba, hakan yasa na saka jakar kud'in cikin gana masgo d'ina na saka kayana tare da kinkimar jakar na fito, Allah ya taimakeni babu kowa me gadi ma baya nan maybe ya zagaya baya, hakan yasa na runtuma a guje duk da gudun ba sauri sosai saboda jakata dake rinjayata, dama kafin na fito daga cikin gidan na zaro dubu biyar a cikin kud'in nasa a aljihu, ina fitowa na tari adai-daita sahu sai tasha, ina zuwa naci sa'a saura mutum d'aya ta cika na biya kud'i sannan na shiga, ba yanda ba'ayi ba kan in bada jakar a samin a baya nak'i yarda, a haka aka ja motar jakar na k'afata har muka iso kano, tunani na fara yi kan ina zan dosa ni da bansan kowa ba gashi kano akwai girma ta ina zan fara nemanta, ina cikin wannan tunanin na hango wani dattijon Arzik'i cikin tashar wanda ke zaune cikin wata kwarab'ab'b'iyar mota yana cin tuwo, k'arasawa nai kusa dashi sannan na gaishe shi, bayan mun gama gaisawa yace min "yaro ina zaka je kai kad'ai haka ina iyayenka, ko kai Almajiri ne, koda yake jikinka be nuna ba," nan na fad'a mishi cewa iyayena ne da 'yar uwata nake nema a nan garin, tare da ciro hotunanmu duka ina nuna mishi, bayan ya duba yace " yaro gaskiya ban san inda suke ba kuma bansan inda za'a gansu ba, kuma kasan kano da girma, amma zan taimake ka, in ka yarda zaka zauna da ni to zan taimaka maka insha Allah za'a gansu wata rana, ba ko tunani nace na yarda zan bishi, ya siya min tuwo naci sannan ya d'aukeni ya kaini shagon wani gida yace nan ne makwancinsa domin shima ba d'an garin nan bane d'an zaria ne, neman kud'i ya kawoshi nan, mota yake ja duk ta tsufa ma kuma beda halin da zai dawo da iyalinsa nan, bayan kwana biyu na yanke shawarar rik'a bin Baba in zama kwandastan shi, wata k'ila ko ta sanadin haka Allah yasa in ganki, a haka na cigaba da rayuwa kullum bayan mun fita sai na nemeki haka ma in mun dawo, ban tab'a tunanin tab'a kud'in nan ba saboda komai nakeso Baba yana min, bayan shekara biyar lokacin shekarata sha shida kenan jikin Baba yai tsanani har saida ya koma gida, komawar da be sake dawowa ba sai labarin mutuwarshi naji wanda ya sani kuka sosai, rayuwa tai tsanani hakan yasa dole na fara tab'a kud'in nan ina biyan kud'in shago, sannan na cigaba da zuwa makarantar da Baba ya sani, da cigaba da biyawa kaina kud'in makaranta, Baba yana d'aya daga cikin mutanen da har in mutu bazan iya mantawa dasu ba, a haka har na girma nakai shekara Ashirin da bakwai ina nemanki a lokacin ne na shiga makarantar da kike aka yi sa'a kuma daga shigana Allah ya had'a mu a kan hanya, sedai tun a ranar na fahimci kece Amira ta saboda har lokacin kina tare da 'yan kunnayen da na siya miki da wannan zoben da yai miki d'as a yanzu a hannu, shaida ta gaba itace sunanki da sunan Dad su suka k'ara tabbatar min da kece, kafin had'uwata dake na siya gida duk a cikin kud'in nan, sannan kuma na fara sana'a yanzu kasuwancin gida da filaye nake yi._
Amir ya numfasa sannan ya cigaba da fad'in " taya zan manta da masoyiyata tun ta yarinta wadda take sona da gaske kuma ta zama silar canzawar rayuwata."
Amira wadda idanunta suka yi ja kuma suka kunbura saboda kuka tace " amma meyasa da ka gano nice ka b'oye kanka gareni, kuma ka canza sunanka daga Amir zuwa Ameeru?"
Amir yace " zan baki amsa yanzu ma kuwa amma kafin in fad'a miki inaso ki fad'amin gaskiya me ya faru bayan dawowarku nan, kuma tunda kuka dawo garin nan kin koma Abuja, kuma meyasa kike karatu anan bayan su su Dad sun koma Abujan da zama?"
_ku biyoni muje_🏃♀
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie) ```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah) ```🤜🤛
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S kullum fa burgeni kuke wallahi, Allah ya k'ara d'aukaka mini ku, ya k'ara muku basira, ya k'ara mana k'aunar juna, a cigaba da basu mamakin kawai😉😘*
*MUMCYN MU ALLAH YA K'ARA 'DORAR DA LAFIYARSA GAREKI, TAWAN ALLAH YA K'ARAWA MUMMY LAFIYA👏😭😭😭*
*MY NAMECY BILKISU (QUEEN BK) ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA👏😭*
*MY LISSA Amir yace yaji sak'on gaisuwar ki amma be amsawa saboda kin b'ata mishi rai,😏 sannan yace in mik'a gaisuwa da ga magoya bayansa QUEEN RUQEEY HABIBTY, da MAMAN LABYB MAMIE NAH TA KAINA, da BABYNAH HAUWA, da MY HEENAT, yace duk wata k'auna taku da kuke gwada mishi yana gani kuma yana godiya, sannan yana so yasan iya adadin 'yan team d'insa duk da yasan masoyanshi sunfi yawa Lissa ce kad'ai bata sonshi kuma yace a fad'amata yana mata i hate you😂😂😂😂😂*
PAGE 80 to 85
Amira ta kalle shi tace _" bayan tahowarmu abun be dameni ba sosai sai da naga anyi sati d'aya biyu har wata shiru ba'a ma maganar komawarmu gida, koda na jewa da Dad d'ina da maganar komawarmu sai naji sab'anin haka yana fad'in ai a nan zamu cigaba da zama yanzu haka ma makaranta yake so ya sakani in cigaba da karatuna, dama shi ya yi haka ne dan ya rabamu tunda mun k'i maida hankali a karatu amma in kwantar da hankalina yana kula da kai da kuma karatunka, a ranar ma fad'ar halin da na shiga b'ata baki ne, anan na cigaba da karatuna har na girma, ana fara shirin sakani jami'a Dad d'ina ya koma Abuja da 'yan uwana da zama sakamakon tsayar da shi da aka yi na zama takarar shugaban k'asa kuma cikin ikon Allah ya samu nasara, ranar da na fara zuwa gida shima bikin murnar samun kujerar mahaifina ne, da naje ba irin neman da ban maka ba aka tabbatar mun da cewa ai tun ranar da muka tafi kaima ka gudu basu san inda ka shiga ba, na ci kuka na gode Allah amma har lokacin gani nake yi duk daren dad'ewa zamu had'u shiyasa duk na koma garin Abuja sai na fita neman labari a kanka amma shiru, duk tsawon wannan shekarun na kasa cireka a raina Amir koda na kwana d'aya ne, kullum sai na d'auko hotonmu na kalla ina kuka ina tuna rayuwar da muka yi a baya, se dai duk in na tunaka a raina ina ji a cikin zuciyata tana tabbatar mun cewa tabbas wata rana zamu had'u kuma in har Allah ya had'amu banda wani miji sai kai, ko cikin k'awayena a ko'ina nake in aka yi maganar aure sai ka fad'o raina domin da kai kad'ai na saba, kaine ma namiji na farko da ya tab'a shigowa cikin rayuwata, kullum tunanina zan ganka, sam Dad baya son ina kai ziyara gida saboda kar mu had'u dakai, shi burinshi kar na dawo sai na gama karatu gaba d'aya tukun, kasan dai yanda na shak'u da kai kuma nake sonka, shiyasa na dad'e tunanin ka na tab'amin zuciya."_
Amira ta cigaba da fad'in "kaji abinda ya faru bayan barinmu garin."
Amir ya numfasa sannan ya kalleta yace " to nima zuciyata ta tabbatar min da cewa saboda ni kuka tafi kuka canza gari kuka yi nesa dani, domin na dad'e da sanin cewa Dad baya sona tare dake, hakan ne yasa na canza suna daga Ameeru na koma Amir kuma bayan na ganoki na cigaba da b'oye miki kaina, burina muyi aure tukun kafin ki gano ko ni waye kar kizo ki gano kuma Mahaifin ki ya hanani mallakar ki matsayin mata."
Amira tace "duk da haka wannan dalilin be isa saka ka cigaba da b'oye min kanka ba, kai da kanka kace kaga abubuwan da ka siya a tare dani duk da cewa ko da nake yarinya ma na wuce da ajinsu balle da girmana, amma soyayyar da nake maka tasa nake kallon su a gagarumar kyauta mafi tsada a duniya, kasan wahalar da nake kan sha har yanzu wajen nemanka kuwa domin saida zuciyata ta bani nan kano ka taho saboda na rubuta maka inda zamu taho a wasik'a, kasan mutane nawa na kasa su cigaba da bincikamin labarin duk wani mutum me suna Ameeru kuwa? kasan iya adadin maza nawa nabi masu irin sunanka ina bibiyarsu domin gano wanene kai a cikinsu? haba Amir meyasa da ka gano nice ka b'ata lokaci wajen sanar da ni kaine Amir d'ina? haba Amir ya zaka min haka."
Amir ya dafa Amira sannan yace kiyi hak'uri Amira, harga Allah zuciyata bata yi tunanin har wannan tsawon lokacin ina cikin ranki ba saboda mutanen da nazo na tarar dasu a tare dake musamman Sadeeq da Abdul, kuma dukkanin su na hango alamun k'aunarki a cikin ransu, hakan yasa na bari tukun sai na farfad'o da soyayyata da wasu suke k'ok'arin k'waceta daga gareni, kinji dalili wallahi banyi tunanin har zuwa yanzu ina ranki ba haka saboda ganinsu a tare dake, amma gani a gabanki guiwoyina a k'asa ina rok'on ki dan Allah ki amince ki taimaka ki sake shigowa rayuwata, wallahi a yanzu ke kad'ai ce abar da na rasa a rayuwata."
Amira tace " wallahi duk cikin su babu wanda na tab'a jin sonshi a raina, shak'uwa ce kawai da sabo amma ban tab'a sonsu ba kamar 'yan uwa na d'aukesu kuma abokan shawara."
"Dama wannan shine dalilin da yasa ka bisu d'aya bayan d'aya ka kashe su?" maganar da su Amir da Amira suka ji anyi kenan daga bayansu, koda suka juyo dukkansu ba wanda suka gani sai Insp Yahya, jingine da jikin k'ofa yana hard'e da hannayen shi.
Amir ya numfasa sannan ya cigaba da fad'in " taya zan manta da masoyiyata tun ta yarinta wadda take sona da gaske kuma ta zama silar canzawar rayuwata."
Amira wadda idanunta suka yi ja kuma suka kunbura saboda kuka tace " amma meyasa da ka gano nice ka b'oye kanka gareni, kuma ka canza sunanka daga Amir zuwa Ameeru?"
Amir yace " zan baki amsa yanzu ma kuwa amma kafin in fad'a miki inaso ki fad'amin gaskiya me ya faru bayan dawowarku nan, kuma tunda kuka dawo garin nan kin koma Abuja, kuma meyasa kike karatu anan bayan su su Dad sun koma Abujan da zama?"
_ku biyoni muje_🏃♀
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie) ```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah) ```🤜🤛
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S kullum fa burgeni kuke wallahi, Allah ya k'ara d'aukaka mini ku, ya k'ara muku basira, ya k'ara mana k'aunar juna, a cigaba da basu mamakin kawai😉😘*
*MUMCYN MU ALLAH YA K'ARA 'DORAR DA LAFIYARSA GAREKI, TAWAN ALLAH YA K'ARAWA MUMMY LAFIYA👏😭😭😭*
*MY NAMECY BILKISU (QUEEN BK) ALLAH YA KARA MIKI LAFIYA👏😭*
*MY LISSA Amir yace yaji sak'on gaisuwar ki amma be amsawa saboda kin b'ata mishi rai,😏 sannan yace in mik'a gaisuwa da ga magoya bayansa QUEEN RUQEEY HABIBTY, da MAMAN LABYB MAMIE NAH TA KAINA, da BABYNAH HAUWA, da MY HEENAT, yace duk wata k'auna taku da kuke gwada mishi yana gani kuma yana godiya, sannan yana so yasan iya adadin 'yan team d'insa duk da yasan masoyanshi sunfi yawa Lissa ce kad'ai bata sonshi kuma yace a fad'amata yana mata i hate you😂😂😂😂😂*
PAGE 80 to 85
Amira ta kalle shi tace _" bayan tahowarmu abun be dameni ba sosai sai da naga anyi sati d'aya biyu har wata shiru ba'a ma maganar komawarmu gida, koda na jewa da Dad d'ina da maganar komawarmu sai naji sab'anin haka yana fad'in ai a nan zamu cigaba da zama yanzu haka ma makaranta yake so ya sakani in cigaba da karatuna, dama shi ya yi haka ne dan ya rabamu tunda mun k'i maida hankali a karatu amma in kwantar da hankalina yana kula da kai da kuma karatunka, a ranar ma fad'ar halin da na shiga b'ata baki ne, anan na cigaba da karatuna har na girma, ana fara shirin sakani jami'a Dad d'ina ya koma Abuja da 'yan uwana da zama sakamakon tsayar da shi da aka yi na zama takarar shugaban k'asa kuma cikin ikon Allah ya samu nasara, ranar da na fara zuwa gida shima bikin murnar samun kujerar mahaifina ne, da naje ba irin neman da ban maka ba aka tabbatar mun da cewa ai tun ranar da muka tafi kaima ka gudu basu san inda ka shiga ba, na ci kuka na gode Allah amma har lokacin gani nake yi duk daren dad'ewa zamu had'u shiyasa duk na koma garin Abuja sai na fita neman labari a kanka amma shiru, duk tsawon wannan shekarun na kasa cireka a raina Amir koda na kwana d'aya ne, kullum sai na d'auko hotonmu na kalla ina kuka ina tuna rayuwar da muka yi a baya, se dai duk in na tunaka a raina ina ji a cikin zuciyata tana tabbatar mun cewa tabbas wata rana zamu had'u kuma in har Allah ya had'amu banda wani miji sai kai, ko cikin k'awayena a ko'ina nake in aka yi maganar aure sai ka fad'o raina domin da kai kad'ai na saba, kaine ma namiji na farko da ya tab'a shigowa cikin rayuwata, kullum tunanina zan ganka, sam Dad baya son ina kai ziyara gida saboda kar mu had'u dakai, shi burinshi kar na dawo sai na gama karatu gaba d'aya tukun, kasan dai yanda na shak'u da kai kuma nake sonka, shiyasa na dad'e tunanin ka na tab'amin zuciya."_
Amira ta cigaba da fad'in "kaji abinda ya faru bayan barinmu garin."
Amir ya numfasa sannan ya kalleta yace " to nima zuciyata ta tabbatar min da cewa saboda ni kuka tafi kuka canza gari kuka yi nesa dani, domin na dad'e da sanin cewa Dad baya sona tare dake, hakan ne yasa na canza suna daga Ameeru na koma Amir kuma bayan na ganoki na cigaba da b'oye miki kaina, burina muyi aure tukun kafin ki gano ko ni waye kar kizo ki gano kuma Mahaifin ki ya hanani mallakar ki matsayin mata."
Amira tace "duk da haka wannan dalilin be isa saka ka cigaba da b'oye min kanka ba, kai da kanka kace kaga abubuwan da ka siya a tare dani duk da cewa ko da nake yarinya ma na wuce da ajinsu balle da girmana, amma soyayyar da nake maka tasa nake kallon su a gagarumar kyauta mafi tsada a duniya, kasan wahalar da nake kan sha har yanzu wajen nemanka kuwa domin saida zuciyata ta bani nan kano ka taho saboda na rubuta maka inda zamu taho a wasik'a, kasan mutane nawa na kasa su cigaba da bincikamin labarin duk wani mutum me suna Ameeru kuwa? kasan iya adadin maza nawa nabi masu irin sunanka ina bibiyarsu domin gano wanene kai a cikinsu? haba Amir meyasa da ka gano nice ka b'ata lokaci wajen sanar da ni kaine Amir d'ina? haba Amir ya zaka min haka."
Amir ya dafa Amira sannan yace kiyi hak'uri Amira, harga Allah zuciyata bata yi tunanin har wannan tsawon lokacin ina cikin ranki ba saboda mutanen da nazo na tarar dasu a tare dake musamman Sadeeq da Abdul, kuma dukkanin su na hango alamun k'aunarki a cikin ransu, hakan yasa na bari tukun sai na farfad'o da soyayyata da wasu suke k'ok'arin k'waceta daga gareni, kinji dalili wallahi banyi tunanin har zuwa yanzu ina ranki ba haka saboda ganinsu a tare dake, amma gani a gabanki guiwoyina a k'asa ina rok'on ki dan Allah ki amince ki taimaka ki sake shigowa rayuwata, wallahi a yanzu ke kad'ai ce abar da na rasa a rayuwata."
Amira tace " wallahi duk cikin su babu wanda na tab'a jin sonshi a raina, shak'uwa ce kawai da sabo amma ban tab'a sonsu ba kamar 'yan uwa na d'aukesu kuma abokan shawara."
"Dama wannan shine dalilin da yasa ka bisu d'aya bayan d'aya ka kashe su?" maganar da su Amir da Amira suka ji anyi kenan daga bayansu, koda suka juyo dukkansu ba wanda suka gani sai Insp Yahya, jingine da jikin k'ofa yana hard'e da hannayen shi.