Sashe 47
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nura ya amsa da "to," suna gama wayar Nura ya kira wayar Mahaifinshi, bayan ya d'aga sun gaisa sai yace "Baba ina kyautata zaton ranar da muka dad'e muna jira ne yau tazo, domin yanzu Dad d'in Amira ya kirani yace in yi maza inje yana son ganina."
Baban Nura yace "Allah mun gode maka, to me kake jira har yanzu baka tafi ba?"
Nura yace "ai yanzu zan tafi Baba, sai na dawo duk yanda ake ciki zaka ji," daga nan suka yi sallama ya fito ya tafi.
Duk wayar nan da yake a cikin gida ya yita, amma duk a tunaninsa Amira bacci take yi shiyasa ya saki jikinsa yai wayarshi hankali kwance.
Bayan fitarsa Amira dake lab'e ta gama jin komai ta kira Amir ta fad'a mishi duk abinda taji da kunnenta, dama Amir ya fad'a mata duk maganar da taji Nura yayi ta kira ta fad'a mishi.
Nura ne zaune gaban Dad, yana matu'kar martaba Dad da 'kas'kantar da kai a gabanshi kamar mutumin arzi'ki.
Bayan sun gaisa Dad ya kwaso wasu takardu dake gefenshi ya kalli Nura tare da mi'ka mishi takardun nan yace "ungo ri'ke nan, bayan Nura ya karb'a Dad ya cigaba da fad'in wad'annan takardun dukkanin kadarorina ne da na mallaka, na dam'ka su a hannunka ne ba dan komai ba sai dan na riga da na mallakawa Amira su, sedai bana so ta ri'ke a hannunta sai nan gaba tukun in ta 'kara girma da hankali, dan haka ka cigaba da juyawa tare da kulawa dasu har ranar da Allah zai hukunta ta karb'a."
Nura yace "amma Daddy a ganina ya kamata Amira tazo ayi komai a gabanta daga nan kuma mu sassaka hannu."
Dad yai murmushi sannan yace "karka damu Nura na yarda da kai, ban tab'a tunanin cikin talakawa akwai masu amana irinka ba, na baka kamfanina ka juya tsakani da Allah, sannan na d'auki yarinya na baka itama ka ri'keta da hannu biyu, tare da bata duk wata kulawa, abinda yasa ma har aka kai tsawon wannan lokacin ban baka ba dama saboda in gwadaka ne, dan haka karka damu na yarda dakai, fatana ka nunka duk wata kulawa da kake yiwa 'yata kuma ka ri'ke amana ka kuma cika al'kawari."
Bayan sun gama magana Nura yai godiya harda hawayen drama sannan suka yi sallama ya wuce gidan Babanshi kai tsaye.
Da isarshi ya kwashe duk yanda suka yi da mahaifin Amira ya fad'awa Babanshi.
Zama suka yi suka dudduba takardun, a ciki babu na kamfanin da aka baiwa Nura, babu na mahaifinsa, sannan babu na gidan Dad wanda yake ciki da kuma na su Amira.
Nura yace "wallahi suma sai ya bada su, lallai ba zamu bar mishi komai ba sai mun yashe shi, wai harda ce mana talakwa a cikin maganarshi be san kalmar taban haushi ba, amma kwanan nan kalmar zata fara aiki a kanshi muga kuma 'karyar 'kin talaka," suka she'ke da dariya harda tafawarsu, nan suka cigaba da tsara mugayen shirinsu akan su Amira.
Washe gari Nura ya dawo daga aiki bayan sun rabu da Amir kamar kullum sai ya wuce gida.
Yana zaune wayarshi tai 'kara, yana dubawa yaga ashe mahaifinsa ne, yana d'agawa yaji mahaifinsa ya fara fad'a, "Nura ashe kai wawan yaro ne da ina cewa na haifi yaro me wayau, baka san wannan yaron da na ganku tare dashi a bakin ti-ti shine tsohon mijin Amira ba?" to in baka sani ba yanzu ka sani ai, shashasha kana nema ka rusa komai," yana gama fad'in haka ya kashe wayarsa, shi kuwa Nura wanda tun d'azu yake a tsaye, ya fara kai kawo yana nazarin wannan maganar, ganin duk wannan bazai fish she shi ba yasa ya zari makulli ya fice daga gidan.
Nura zaune yake gaban Babansa yana yi mishi tambayoyi, "Baba wanene mijin Amira da kace ka ganmu tare dashi?"
Baba yace "d'azu na ganku tare dashi," nan ya shiga koro mishi bayanin siffar Amir da kuma kayan da ya saka.
Lallai a yanzu Nura bashi da hujjar 'karyata zancen mahaifinshi ko ya musa mishi.
Nura yai murmushi sannan yace "ka kwantar da hankalinka Baba, dama na dad'e ina zargin wani abu game dashi, sannan ina sane nai saurin sabawa dashi domin in fahimci ko shi wanene saboda in d'auki mataki a kanshi da wuri, karka wani damu inada aboki d'an abokin nan naka Baba, babban d'an sanda ne shi yanzu a garin nan, ba wanda ya isa ya ja damu muddin muna tare dashi, zamu had'a hannu dashi, bari ma ka gani."
Wayarsa ya zaro yai kira har ta katse ba'a d'aga ba, sai a kira na biyu aka d'aga, bayan sun gaisa Nura yace "daga jin muryar babu tambaya Insp Yahya ne kafi 'karfin mugu?" yai maganar da sigar tambaya tare da yin shiru yana jiran amsa
Muje zuwa
*🅱K CE*😘💋
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*'YAN UWANA INA MAI TUNATAR DAMU KAN CEWA KAR MU SIYAR DA 'YANCINMU, KAR MU ZAB'I MUGAYEN SHUWAGABANNI DA ZASUITA KASHEMU, BABA BUHARI BA MUGU BANE, BA AZZALUMI BANE, KUMA BA MACI AMANAR 'KASA BANE, MUTUM NE SHI NA KWARAI ME YA'KI DA ZALUNCI DA KUMA AZZALUMAI, DUK MU FITO 'KWANMU DA 'KWAR'KWATARMU MU SAKE ZAB'ARSHI A MATSAYIN SHUGABAN 'KASA, KAR IDONMU YA RUFE MU MANTA ABUBUWAN DA SUKA FARU A SHEKARUN BAYA LOKACIN MULKIN GOOD LUCK, YANDA AKA MAIDA RAYUKAN BAYI KAMAR KIYASHI, BABU KWANCIYAR HANKALI, YARA SUKA DAINA ZUWA MAKARANTA, DUK KARMU MANTA HAKAN, DAN HAKA ZAB'I YA RAGE GAREMU, KO MU ZAB'I SHUGABA NAGARI MU RAYU CIKIN WALWALA, KO MU ZAB'I MUGAYE KUMA B'ARAYI SUITA KASHEMU KUMA SUNA KWASHE DUKIYARMU.*
PAGE 200 to 205
Insp Yahya yai dariya sannan yace "ni ne mana kana tunanin banda lambarka ne Nura, gabad'aya ka b'oye ina ka shige ne tun bayan da kuka tashi daga garinmu?"
Nura yai dariya, sannan yace "yanzu haka ina kano mun dawo nan da zama," Insp Yahya yace "nima ai ina kano, a wace unguwa kake?"
Nan dai Insp Yahya yaiwa Nura kwatancen inda yake ba tare da wani b'ata lokaci ba ya shirya ya tafi.
Nura na isa station suka sake sabuwar gaisuwa da Insp Yahya, sannan ya kwashe duk abinda ke faruwa ya fad'a mishi.
Insp Yahya ya numfasa sannan yace "kaima kayi wauta da kai saurin amince mishi, amma ba wani abu, hukuma mu a hannunmu take, amma sedai in ka yarda duk abinda kuka samu rabawa dai-dai zamu yi, ka amince?"
Nura bai yi wata-wata ba yace ya amince, Insp yace "nuna min hoton yaron in gani, kamata yayi mu fara kamashi kafin ya tona mana asiri," Nura ya d'auko wayarshi ya fito da hoton Amir sannan ya bawa Insp ya gani.
Insp Yahya na duba hoto ya mi'ke tsaye cikin sauri tare da zaro ido yace "Amir!! wannan ai Amir ne," Nura shima ya mi'ke tsaye, sannan yace ka sanshi ne?"
Insp yace " 'kwarai nasan Amir farin sani," nan dai ya bashi labarin duk abinda ya faru a tsakaninshi da su Amir, sannan ya cigaba da cewa "kuma in dai a kanshi da matarshi kake magana to ni bama sai kun bani ko si-si ba zan tayaku, saboda na dad'e ina neman hanyar da zan tozarta rayuwar Amir fiye da tunaninka, amma yanzu abinda za'ai dole tsarin ya canza saboda Amir mugun wayau ne dashi, kawo kunnenka kaji."
Nan da nan suka gama kitsa mugun 'kullin su, sannan suka tashi suka fito daga station d'in, suka shiga motar Nura yaja suka tafi.
Shi kuwa Amir tunda ya sami labarin Nura sun ganoshi ya b'uya, amma yasan gabad'ayan shirinsa ya rushe.
Amir zaune yake kan kujera yana tunanin abinda ya kamata yayi, tabbas yasan dai-dai wannan lokacin komai zai iya faruwa da Amira, cikin sauri ya d'auki wayarshi ya kira Amira tare da shaida mata tai maza ta fito daga gidan nan yanzu zai taho da mota ya d'auketa.
Amira cikin sauri ta shiga cikin d'aki domin d'auko mayafinta ta fita ta bar gidan kamar yanda masoyinta Amir yai mata umurni akai, sedai kash tana fitowa falon ta tarar da wasu samudawan 'katti sun cika mata falo, babbansu yana kan kujera hankalinsa kwance, a yayinda sauran kuma suke tsaye suna zazzare idanu, dukkansu kamanninsu bata nuna ta mutanen arzi'ki ne, kuma gaba d'ayansu ba'ka'ke 'kirin siffarsu duk babu me kyan gani, koda yake dama wanda ya rasa imani ai kalarsa da siffarsa bazatai dai-dai da ta mumini ba.
Babban ne ya kalli Amira sannan yace "sannu Amira, ashe ma kinsan da zuwanmu har kin shirya sai tafiya kawai ko?"
Amira cikin rawar murya tace "su waye ku, kuma me kuka zo yi nan?"
Babban ba tare da ya bata amsa ba ya kalli 'kattin dake tsatstsaye yai musu alama da kai da su kamata.
Cikin sauri suka kamata d'aya daga ciki ya sab'ata a wuya tana wuntsil-wuntsil a haka suka fice da ita daga gidan, har suka shiga motoci bata daina kurma ihu ba hakan yasa ogansu ya d'aga hannunsa mai kama da guduma ya mauje ta nan ta fad'a kan kafad'ar 'katon dake kusa da ita a sume.
Bayan tafiyarsu da minti goma sai ga Amir ya 'karaso da sauri ya shiga cikin gidan ya bincika ko ina amma bai ga Amira ba, dawowa falo yayi yana dube-dube can ya hango kwalin taba kuma shi iya saninshi yasan Nura baya sha, dan yasha gwadashi akan haka amma koda wasa bai tab'a gwadawa ba, shidai barshi da tantiranci da neman mata kamar d'an akuya, ganin kwalin tabar da Amir yayi ya tabbatar mishi da cewa an rigashi zuwa an tafi da Amira.
Amir ya dafe kai yana tunani, can kuma ko me ya tuno sai ya fice daga gidan cikin sauri.
Motar shi ya fad'a ya tasheta sai gidan Dad, yana zuwa kowa na cikin gidan sai kallonsa sukeyi cike da mamaki suna yi mishi tambayoyi, sai Amir yace "yanzu ba lokacin tattauna wannan maganar bane, ina Dad yake?"
Mum tace "basu dad'e da fita ba, sirikinshi Nura yazo ya d'auke shi yace akwai meeting d'in da zasu yi yanzu da wasu ba'ki da suka zo."
Baban Nura yace "Allah mun gode maka, to me kake jira har yanzu baka tafi ba?"
Nura yace "ai yanzu zan tafi Baba, sai na dawo duk yanda ake ciki zaka ji," daga nan suka yi sallama ya fito ya tafi.
Duk wayar nan da yake a cikin gida ya yita, amma duk a tunaninsa Amira bacci take yi shiyasa ya saki jikinsa yai wayarshi hankali kwance.
Bayan fitarsa Amira dake lab'e ta gama jin komai ta kira Amir ta fad'a mishi duk abinda taji da kunnenta, dama Amir ya fad'a mata duk maganar da taji Nura yayi ta kira ta fad'a mishi.
Nura ne zaune gaban Dad, yana matu'kar martaba Dad da 'kas'kantar da kai a gabanshi kamar mutumin arzi'ki.
Bayan sun gaisa Dad ya kwaso wasu takardu dake gefenshi ya kalli Nura tare da mi'ka mishi takardun nan yace "ungo ri'ke nan, bayan Nura ya karb'a Dad ya cigaba da fad'in wad'annan takardun dukkanin kadarorina ne da na mallaka, na dam'ka su a hannunka ne ba dan komai ba sai dan na riga da na mallakawa Amira su, sedai bana so ta ri'ke a hannunta sai nan gaba tukun in ta 'kara girma da hankali, dan haka ka cigaba da juyawa tare da kulawa dasu har ranar da Allah zai hukunta ta karb'a."
Nura yace "amma Daddy a ganina ya kamata Amira tazo ayi komai a gabanta daga nan kuma mu sassaka hannu."
Dad yai murmushi sannan yace "karka damu Nura na yarda da kai, ban tab'a tunanin cikin talakawa akwai masu amana irinka ba, na baka kamfanina ka juya tsakani da Allah, sannan na d'auki yarinya na baka itama ka ri'keta da hannu biyu, tare da bata duk wata kulawa, abinda yasa ma har aka kai tsawon wannan lokacin ban baka ba dama saboda in gwadaka ne, dan haka karka damu na yarda dakai, fatana ka nunka duk wata kulawa da kake yiwa 'yata kuma ka ri'ke amana ka kuma cika al'kawari."
Bayan sun gama magana Nura yai godiya harda hawayen drama sannan suka yi sallama ya wuce gidan Babanshi kai tsaye.
Da isarshi ya kwashe duk yanda suka yi da mahaifin Amira ya fad'awa Babanshi.
Zama suka yi suka dudduba takardun, a ciki babu na kamfanin da aka baiwa Nura, babu na mahaifinsa, sannan babu na gidan Dad wanda yake ciki da kuma na su Amira.
Nura yace "wallahi suma sai ya bada su, lallai ba zamu bar mishi komai ba sai mun yashe shi, wai harda ce mana talakwa a cikin maganarshi be san kalmar taban haushi ba, amma kwanan nan kalmar zata fara aiki a kanshi muga kuma 'karyar 'kin talaka," suka she'ke da dariya harda tafawarsu, nan suka cigaba da tsara mugayen shirinsu akan su Amira.
Washe gari Nura ya dawo daga aiki bayan sun rabu da Amir kamar kullum sai ya wuce gida.
Yana zaune wayarshi tai 'kara, yana dubawa yaga ashe mahaifinsa ne, yana d'agawa yaji mahaifinsa ya fara fad'a, "Nura ashe kai wawan yaro ne da ina cewa na haifi yaro me wayau, baka san wannan yaron da na ganku tare dashi a bakin ti-ti shine tsohon mijin Amira ba?" to in baka sani ba yanzu ka sani ai, shashasha kana nema ka rusa komai," yana gama fad'in haka ya kashe wayarsa, shi kuwa Nura wanda tun d'azu yake a tsaye, ya fara kai kawo yana nazarin wannan maganar, ganin duk wannan bazai fish she shi ba yasa ya zari makulli ya fice daga gidan.
Nura zaune yake gaban Babansa yana yi mishi tambayoyi, "Baba wanene mijin Amira da kace ka ganmu tare dashi?"
Baba yace "d'azu na ganku tare dashi," nan ya shiga koro mishi bayanin siffar Amir da kuma kayan da ya saka.
Lallai a yanzu Nura bashi da hujjar 'karyata zancen mahaifinshi ko ya musa mishi.
Nura yai murmushi sannan yace "ka kwantar da hankalinka Baba, dama na dad'e ina zargin wani abu game dashi, sannan ina sane nai saurin sabawa dashi domin in fahimci ko shi wanene saboda in d'auki mataki a kanshi da wuri, karka wani damu inada aboki d'an abokin nan naka Baba, babban d'an sanda ne shi yanzu a garin nan, ba wanda ya isa ya ja damu muddin muna tare dashi, zamu had'a hannu dashi, bari ma ka gani."
Wayarsa ya zaro yai kira har ta katse ba'a d'aga ba, sai a kira na biyu aka d'aga, bayan sun gaisa Nura yace "daga jin muryar babu tambaya Insp Yahya ne kafi 'karfin mugu?" yai maganar da sigar tambaya tare da yin shiru yana jiran amsa
Muje zuwa
*🅱K CE*😘💋
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*'YAN UWANA INA MAI TUNATAR DAMU KAN CEWA KAR MU SIYAR DA 'YANCINMU, KAR MU ZAB'I MUGAYEN SHUWAGABANNI DA ZASUITA KASHEMU, BABA BUHARI BA MUGU BANE, BA AZZALUMI BANE, KUMA BA MACI AMANAR 'KASA BANE, MUTUM NE SHI NA KWARAI ME YA'KI DA ZALUNCI DA KUMA AZZALUMAI, DUK MU FITO 'KWANMU DA 'KWAR'KWATARMU MU SAKE ZAB'ARSHI A MATSAYIN SHUGABAN 'KASA, KAR IDONMU YA RUFE MU MANTA ABUBUWAN DA SUKA FARU A SHEKARUN BAYA LOKACIN MULKIN GOOD LUCK, YANDA AKA MAIDA RAYUKAN BAYI KAMAR KIYASHI, BABU KWANCIYAR HANKALI, YARA SUKA DAINA ZUWA MAKARANTA, DUK KARMU MANTA HAKAN, DAN HAKA ZAB'I YA RAGE GAREMU, KO MU ZAB'I SHUGABA NAGARI MU RAYU CIKIN WALWALA, KO MU ZAB'I MUGAYE KUMA B'ARAYI SUITA KASHEMU KUMA SUNA KWASHE DUKIYARMU.*
PAGE 200 to 205
Insp Yahya yai dariya sannan yace "ni ne mana kana tunanin banda lambarka ne Nura, gabad'aya ka b'oye ina ka shige ne tun bayan da kuka tashi daga garinmu?"
Nura yai dariya, sannan yace "yanzu haka ina kano mun dawo nan da zama," Insp Yahya yace "nima ai ina kano, a wace unguwa kake?"
Nan dai Insp Yahya yaiwa Nura kwatancen inda yake ba tare da wani b'ata lokaci ba ya shirya ya tafi.
Nura na isa station suka sake sabuwar gaisuwa da Insp Yahya, sannan ya kwashe duk abinda ke faruwa ya fad'a mishi.
Insp Yahya ya numfasa sannan yace "kaima kayi wauta da kai saurin amince mishi, amma ba wani abu, hukuma mu a hannunmu take, amma sedai in ka yarda duk abinda kuka samu rabawa dai-dai zamu yi, ka amince?"
Nura bai yi wata-wata ba yace ya amince, Insp yace "nuna min hoton yaron in gani, kamata yayi mu fara kamashi kafin ya tona mana asiri," Nura ya d'auko wayarshi ya fito da hoton Amir sannan ya bawa Insp ya gani.
Insp Yahya na duba hoto ya mi'ke tsaye cikin sauri tare da zaro ido yace "Amir!! wannan ai Amir ne," Nura shima ya mi'ke tsaye, sannan yace ka sanshi ne?"
Insp yace " 'kwarai nasan Amir farin sani," nan dai ya bashi labarin duk abinda ya faru a tsakaninshi da su Amir, sannan ya cigaba da cewa "kuma in dai a kanshi da matarshi kake magana to ni bama sai kun bani ko si-si ba zan tayaku, saboda na dad'e ina neman hanyar da zan tozarta rayuwar Amir fiye da tunaninka, amma yanzu abinda za'ai dole tsarin ya canza saboda Amir mugun wayau ne dashi, kawo kunnenka kaji."
Nan da nan suka gama kitsa mugun 'kullin su, sannan suka tashi suka fito daga station d'in, suka shiga motar Nura yaja suka tafi.
Shi kuwa Amir tunda ya sami labarin Nura sun ganoshi ya b'uya, amma yasan gabad'ayan shirinsa ya rushe.
Amir zaune yake kan kujera yana tunanin abinda ya kamata yayi, tabbas yasan dai-dai wannan lokacin komai zai iya faruwa da Amira, cikin sauri ya d'auki wayarshi ya kira Amira tare da shaida mata tai maza ta fito daga gidan nan yanzu zai taho da mota ya d'auketa.
Amira cikin sauri ta shiga cikin d'aki domin d'auko mayafinta ta fita ta bar gidan kamar yanda masoyinta Amir yai mata umurni akai, sedai kash tana fitowa falon ta tarar da wasu samudawan 'katti sun cika mata falo, babbansu yana kan kujera hankalinsa kwance, a yayinda sauran kuma suke tsaye suna zazzare idanu, dukkansu kamanninsu bata nuna ta mutanen arzi'ki ne, kuma gaba d'ayansu ba'ka'ke 'kirin siffarsu duk babu me kyan gani, koda yake dama wanda ya rasa imani ai kalarsa da siffarsa bazatai dai-dai da ta mumini ba.
Babban ne ya kalli Amira sannan yace "sannu Amira, ashe ma kinsan da zuwanmu har kin shirya sai tafiya kawai ko?"
Amira cikin rawar murya tace "su waye ku, kuma me kuka zo yi nan?"
Babban ba tare da ya bata amsa ba ya kalli 'kattin dake tsatstsaye yai musu alama da kai da su kamata.
Cikin sauri suka kamata d'aya daga ciki ya sab'ata a wuya tana wuntsil-wuntsil a haka suka fice da ita daga gidan, har suka shiga motoci bata daina kurma ihu ba hakan yasa ogansu ya d'aga hannunsa mai kama da guduma ya mauje ta nan ta fad'a kan kafad'ar 'katon dake kusa da ita a sume.
Bayan tafiyarsu da minti goma sai ga Amir ya 'karaso da sauri ya shiga cikin gidan ya bincika ko ina amma bai ga Amira ba, dawowa falo yayi yana dube-dube can ya hango kwalin taba kuma shi iya saninshi yasan Nura baya sha, dan yasha gwadashi akan haka amma koda wasa bai tab'a gwadawa ba, shidai barshi da tantiranci da neman mata kamar d'an akuya, ganin kwalin tabar da Amir yayi ya tabbatar mishi da cewa an rigashi zuwa an tafi da Amira.
Amir ya dafe kai yana tunani, can kuma ko me ya tuno sai ya fice daga gidan cikin sauri.
Motar shi ya fad'a ya tasheta sai gidan Dad, yana zuwa kowa na cikin gidan sai kallonsa sukeyi cike da mamaki suna yi mishi tambayoyi, sai Amir yace "yanzu ba lokacin tattauna wannan maganar bane, ina Dad yake?"
Mum tace "basu dad'e da fita ba, sirikinshi Nura yazo ya d'auke shi yace akwai meeting d'in da zasu yi yanzu da wasu ba'ki da suka zo."