Sashe 50
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka rayuwarsu ta cigaba da kasancewa gwanin ban sha'awa, koda yaushe Amir suna waya da iyayenshi, kuma tun a waya ya basu kyakkyawan labari game da bayyanar Amira gareshi da kuma maida aurensu, hakan yasa sukace suma suna nan tafe kwanan nan zasu zo suga surikarsu daga nan su koma tare dasu Abuja gabad'aya.
Bayan sati d'aya da dawowar auren su Amir suka shirya domin suje su gaishe da su Dad, sedai sunyi dana sanin zuwansu gidan, domin Dad korar kare yai musu tare da kashedin kar su sake zuwar mishi gida yai musu kaca-kaca, yace Amir shine sanadin duk wani halin da yake ciki, da be rab'eshi ba da duk hakan be faru dashi ba, wanda yasa har suka koma gida Amira na kuka, shi kuwa Amir idanunshi sunyi ja kamar me ciwon ido saboda tsananin b'acin rai.
Amira taso ta fad'awa Dad d'inta ko Amir d'an waye, Amir shi ya kwab'eta tare da hanata.
Bayan sun koma gida Amira taci kuka kamar me, shi kuwa Amir ba kukan sai tsabar jan ido da zafi da zuciyarshi ke mishi.
Komawa kusa da ita yayi ya fara rarrashinta, da 'kyar ya samu tai shiru sai ajiyar zuciya take yi.
Tun daga wannan ranar su Amir suka fita harkar su Dad d'in suma, basu sake bi ta kansu ba.
*BAYAN WATA UKU*
Amir ne zaune yana chat a waya, sai ga Amira ta fito daga cikin d'aki itama ta zauna kusa dashi takai hannunta tana 'ko'karin le'ka wayar taga me yake yi, sai yai sauri ya kawar da wayar tare da cewa "matsa karki gane min sirri," ai kuwa Amira ta dage tana 'ko'karin saita 'kwace wayar daga hannunshi tana fad'in "bani wayar nan in gani da waye kake chat?"
Amir ya tashi yana b'ob'b'oyewa suka fara zagaye d'akin Amira ta dage sai ta 'kwaci waya daga hannunshi suna cikin wannan yanayin suka ji sallamar su Abba da Umma, bayansu kuma wasu daga cikin masu tsaron lafiyarsu ne ke take musu baya.
Amira ce ta kwasa da gudu taje ta rungume Umma tana masu oyoyo, shi kuma Amir yaje ya rungume Abban shi, sannan suka je suka zazzauna kan kujeru.
Nan suka gaggaisa, sannan aka cika musu gabansu da kayan ciye-ciye kala-kala.
Amir dake lafe cikin jikin Abba yace "Abba yanzu ashe kun taho shine ko ku fad'a mana muje mu taroku."
Umma tace "to in banda kai da abunka yaron kirki ba gashi yanzu kaji dad'in ganinmu ba, dama so muke muyi muku bazata shiyasa muka zo ba tare da mun sanar daku ba."
Amir ya kalli Umma sannan ya kalli Amira dake lafe itama a jikin Umma, sai ya tashi yaje kusa da Umman yana 'ko'karin d'aga Amira daga jikin Umma yana cewa "dallah tashi nima in kwanta ai ba Ummanki bace ke kad'ai."
Amira ta 'kara ri'ke Umma tamau tana fad'in "wallahi bazan d'agata ba ai ba Ummanka bace kai kad'ai."
Abba da Umma sai dariya sukeyi, can sai Abba ya taso yace "ku tsaya wallahi in kuka b'allamin mata ba 'kyaleku zanyi ba duk sai na kulleku," dukkansu suka sa dariya.
Abba ya zauna gefen matarshi sannan yace wa Amir ya 'kyalesu yazo wajenshi ya zauna, haka kuwa akayi ya tafi kusa da Dad d'inshi ya zauna, suka cigaba da hira abinsu cikin jin dad'i, iyayen Amir sunyi farin ciki sosai da ganin yaran nasu cikin kwanciyar hankali, da kuma samun suruka me kirki, haka itama Amira da ka kalleta kasan tana cikin farin cikin samun iyayen miji nagartattu, kuma masu kirki da sau'kin kai.
*BAYAN SATI 'DAYA*
Su Abba ne zaune gabad'ayansu suna hira.
Abba ya kalli su Amira da Amir yace "ya kamata fa ku kaimu wajen iyayen Amira domin muyi musu godiya."
Amira da Amir nan take suka canza fuska, Umma ta kallesu tace "ya haka daga yi muku maganar zuwa gaisawa da iyayenku na nan kano duk kun canza fuska?"
Amira ta mi'ke tsaye sannan tace "gaskiya ni Abba ba inda zanje, tunda su suka zab'i barinmu me zamu je muyi musu," tana gama fad'in haka ta juya ta shige cikin d'aki abinta, su Abba da Umma kuwa suka bita da idanu suna mamakin abubuwan da take fad'i.
Abba ya juyo da kallonshi kan Amir yace "Amir wai meke faruwa ne, kai mana bayani, wani abun ya faru ne tsakaninka da surukanka?"
Amir ya gyara zama sannan yai murmushi, yace "Abba bafa wani abu bane Amira ta zafafa shi haka," nan Amir ya kwashe duk abubuwan da suka faru tun daga farko har 'karshe ya fad'a musu.
Sun dad'e suna jinjina wannan lamari sosai, suna kuma mamakin irin tsanar da Dad ke gwada wa Amir haka, sannan sun jinjina tsananin ha'kuri da Amir yayi.
Umma cikin fushi tace " wannan wane irin mutum ne haka, gaskiya baida imani, kuma babu inda zamuje saboda zuwa wajenshi baida amfani, me zai kaimu gun mutumin da yaci zarafin d'anmu haka, an fad'a mishi kai d'in 'kas'kantaccen mutum ne, dama ance rashin sani yafi dare duhu, wallahi da yasan kai waye da ko da kud'i akace kallon banza wannan yai maka bazai yi maka ba."
Abba ya kalleta yai murmushi, sannan yace "yi ha'kuri my love, ya kamata kiyi tunani kiy nazari ki gani koma menene mahaifin Amira yai mana ya kula da d'anmu a baya, kuma bayan haka Allah ya riga da ya had'amu tunda ga 'yarsu tana auren d'anmu, kinga kuwa an had'u had'uwar da babu ranar rabuwa, ni kaina abinda aka yiwa Amir naji ciwonshi a raina fiye da tunaninki, amma dole in muna so Allah ya yafe mana muma mu zamto masu afuwa akoda yaushe, kuma karmu ri'ka manta alkhairin mutum komai 'kan'kantarsa."
Abba ya numfasa sannan ya cigaba da cewa "Amir kiramin matarka," Amir ya tashi yaje ya kira Amira suka dawo cikin falon tare.
Abba ya kalli Amira yace "Daughter kiyi ha'kuri kinji akan d'an wannan abun banaso ki 'kara tayar da hankalinki balle har ki furta makamancin haka, gobe in Allah ya kaimu zamu je gidanku insha Allah domin mu gaisa da iyayenki."
Da ace Amira zata iya yiwa Abba musu to tabbas akan wannan maganar yau da tayi mishi, amma bata tab'a iya jayayya dashi saboda darajarshi da kimarshi a idanunta, shiyasa ba yanda ta iya, kanta na sunkuye tace "to Abba Allah ya kaimu."
Amir yai wani dogon numfashi sannan yace "lallai mun gode Allah Abba kaci sa'a," Amira ta harari Amir, shi kuma ya kwashe mata da dariya.
Washe gari dukkansu suka shirya suka tafi gidan su Dad.
Suna isowa suka tarar da kayan su Dad birjik a 'kofar gida ana watso musu, koda su Abba suka tambaya aka shaida musu wad'anda su Nura suka siyarwa da gidan ne suka gaji da d'aga musu 'kafa yau sukazo suke musu watsi da kaya.
Cikin gidan suka 'karasa dukkanin 'yan gidan suna tsaye a falo suna kallon sarautar Allah, Dad kuwa kuka yake da idanunshi, wai yau shi ake yiwa haka a rayuwa.
Suna cikin wannan yanayin su Abba suka yi sallama suka shigo, Dad ya d'aga kai ya kalli Abba ya zaro idanu tare da fad'in "Ahmad!!!! yau kaine a gidana, ya kalli gefen Abba inda Amir ke tsaye hannunshi cikin na Abban ya sake cewa "kar dai Amir d'anka ne?"
Abba yai Murmushi, sannan yace "Amir d'ana ne na cikina, ashe kaine mahaifin Amira, ikon Allah kenan," Dad ya fad'i 'kasa dab'as kan kafet, tare da dafe kai yace "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!! na cuci kaina," yana gama fad'in haka ya cigaba da kuka cike da jin kunya me yawa da takaici, had'e da nadama.
Muje zuwa
*🅱K CE*😘💋
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 215 to 220
Sam Dad ya kasa d'ago idanu ya kalli Abba balle Amir da 'yarshi Amira.
Amir ne ya kalli mahaifinsa yace "Abba kasan Dad ne dama?"
Abba ya kalli Amir yace "na sanshi abokina ne wanda acikin labarina da na baka na baka labari ni nai mishi jagora ya samu damar d'anewa kujerar shugaban 'kasa, saboda mutane suna sona kuma sunji dad'in mulkina shiyasa da sukaga dani a wajen tsayar da mahaifin Amira yasa shima ya samu karb'uwa sosai a wajen mutane, daga nan ni kuma na koma garinmu da zama ni da iyalina domin bana bu'katar cigaba da mulkin a lokacin."
Abba ya dakatar da wad'annan mutanen da suke yiwa su Dad watsi da kaya, yasa mutanenshi suka kwashe dukkanin kayan yace su kai sabon gidan da ya gina kwanan nan, wanda yake kusa da nashi da yake ciki a yanzu.
Bayan an gama kwashewa sun sanar dashi yai waya aje a shirya musu gidan a shirya komai yanda ya dace, su kuma yace su tashi gaba d'ayansu su tafi gidanshi idan sunje can a tattauna.
Dad tunda ya zauna a 'kasa ya kasa d'agowa, kanshi na sunkuye har yanzu, banda kuka da nadama babu abinda yake.
Abba ne ya taka yaje har inda Dad yake ya tsugunna, sannan ya kalleshi yace "abokina dan Allah ba dan ni ba ina ro'konka ka manta da komai, karka sashi a ranka, ka tashi muje, tashi," Abba ya kama mishi hannu Dad ya mi'ke suka fito daga gidan suka shisshiga motoci suka tayar suka d'auki hanyar gidan.
Kai tsaye gidan Abba suka wuce domin har yanzu basu 'karasa shiryawa su Dad kayansu ba a d'ayan gidan.
Kowa ya samu waje aka zazzauna a kujeru, aka ci aka sha amma banda Dad domin shi har yanzu kuka yake.
Bayan sati d'aya da dawowar auren su Amir suka shirya domin suje su gaishe da su Dad, sedai sunyi dana sanin zuwansu gidan, domin Dad korar kare yai musu tare da kashedin kar su sake zuwar mishi gida yai musu kaca-kaca, yace Amir shine sanadin duk wani halin da yake ciki, da be rab'eshi ba da duk hakan be faru dashi ba, wanda yasa har suka koma gida Amira na kuka, shi kuwa Amir idanunshi sunyi ja kamar me ciwon ido saboda tsananin b'acin rai.
Amira taso ta fad'awa Dad d'inta ko Amir d'an waye, Amir shi ya kwab'eta tare da hanata.
Bayan sun koma gida Amira taci kuka kamar me, shi kuwa Amir ba kukan sai tsabar jan ido da zafi da zuciyarshi ke mishi.
Komawa kusa da ita yayi ya fara rarrashinta, da 'kyar ya samu tai shiru sai ajiyar zuciya take yi.
Tun daga wannan ranar su Amir suka fita harkar su Dad d'in suma, basu sake bi ta kansu ba.
*BAYAN WATA UKU*
Amir ne zaune yana chat a waya, sai ga Amira ta fito daga cikin d'aki itama ta zauna kusa dashi takai hannunta tana 'ko'karin le'ka wayar taga me yake yi, sai yai sauri ya kawar da wayar tare da cewa "matsa karki gane min sirri," ai kuwa Amira ta dage tana 'ko'karin saita 'kwace wayar daga hannunshi tana fad'in "bani wayar nan in gani da waye kake chat?"
Amir ya tashi yana b'ob'b'oyewa suka fara zagaye d'akin Amira ta dage sai ta 'kwaci waya daga hannunshi suna cikin wannan yanayin suka ji sallamar su Abba da Umma, bayansu kuma wasu daga cikin masu tsaron lafiyarsu ne ke take musu baya.
Amira ce ta kwasa da gudu taje ta rungume Umma tana masu oyoyo, shi kuma Amir yaje ya rungume Abban shi, sannan suka je suka zazzauna kan kujeru.
Nan suka gaggaisa, sannan aka cika musu gabansu da kayan ciye-ciye kala-kala.
Amir dake lafe cikin jikin Abba yace "Abba yanzu ashe kun taho shine ko ku fad'a mana muje mu taroku."
Umma tace "to in banda kai da abunka yaron kirki ba gashi yanzu kaji dad'in ganinmu ba, dama so muke muyi muku bazata shiyasa muka zo ba tare da mun sanar daku ba."
Amir ya kalli Umma sannan ya kalli Amira dake lafe itama a jikin Umma, sai ya tashi yaje kusa da Umman yana 'ko'karin d'aga Amira daga jikin Umma yana cewa "dallah tashi nima in kwanta ai ba Ummanki bace ke kad'ai."
Amira ta 'kara ri'ke Umma tamau tana fad'in "wallahi bazan d'agata ba ai ba Ummanka bace kai kad'ai."
Abba da Umma sai dariya sukeyi, can sai Abba ya taso yace "ku tsaya wallahi in kuka b'allamin mata ba 'kyaleku zanyi ba duk sai na kulleku," dukkansu suka sa dariya.
Abba ya zauna gefen matarshi sannan yace wa Amir ya 'kyalesu yazo wajenshi ya zauna, haka kuwa akayi ya tafi kusa da Dad d'inshi ya zauna, suka cigaba da hira abinsu cikin jin dad'i, iyayen Amir sunyi farin ciki sosai da ganin yaran nasu cikin kwanciyar hankali, da kuma samun suruka me kirki, haka itama Amira da ka kalleta kasan tana cikin farin cikin samun iyayen miji nagartattu, kuma masu kirki da sau'kin kai.
*BAYAN SATI 'DAYA*
Su Abba ne zaune gabad'ayansu suna hira.
Abba ya kalli su Amira da Amir yace "ya kamata fa ku kaimu wajen iyayen Amira domin muyi musu godiya."
Amira da Amir nan take suka canza fuska, Umma ta kallesu tace "ya haka daga yi muku maganar zuwa gaisawa da iyayenku na nan kano duk kun canza fuska?"
Amira ta mi'ke tsaye sannan tace "gaskiya ni Abba ba inda zanje, tunda su suka zab'i barinmu me zamu je muyi musu," tana gama fad'in haka ta juya ta shige cikin d'aki abinta, su Abba da Umma kuwa suka bita da idanu suna mamakin abubuwan da take fad'i.
Abba ya juyo da kallonshi kan Amir yace "Amir wai meke faruwa ne, kai mana bayani, wani abun ya faru ne tsakaninka da surukanka?"
Amir ya gyara zama sannan yai murmushi, yace "Abba bafa wani abu bane Amira ta zafafa shi haka," nan Amir ya kwashe duk abubuwan da suka faru tun daga farko har 'karshe ya fad'a musu.
Sun dad'e suna jinjina wannan lamari sosai, suna kuma mamakin irin tsanar da Dad ke gwada wa Amir haka, sannan sun jinjina tsananin ha'kuri da Amir yayi.
Umma cikin fushi tace " wannan wane irin mutum ne haka, gaskiya baida imani, kuma babu inda zamuje saboda zuwa wajenshi baida amfani, me zai kaimu gun mutumin da yaci zarafin d'anmu haka, an fad'a mishi kai d'in 'kas'kantaccen mutum ne, dama ance rashin sani yafi dare duhu, wallahi da yasan kai waye da ko da kud'i akace kallon banza wannan yai maka bazai yi maka ba."
Abba ya kalleta yai murmushi, sannan yace "yi ha'kuri my love, ya kamata kiyi tunani kiy nazari ki gani koma menene mahaifin Amira yai mana ya kula da d'anmu a baya, kuma bayan haka Allah ya riga da ya had'amu tunda ga 'yarsu tana auren d'anmu, kinga kuwa an had'u had'uwar da babu ranar rabuwa, ni kaina abinda aka yiwa Amir naji ciwonshi a raina fiye da tunaninki, amma dole in muna so Allah ya yafe mana muma mu zamto masu afuwa akoda yaushe, kuma karmu ri'ka manta alkhairin mutum komai 'kan'kantarsa."
Abba ya numfasa sannan ya cigaba da cewa "Amir kiramin matarka," Amir ya tashi yaje ya kira Amira suka dawo cikin falon tare.
Abba ya kalli Amira yace "Daughter kiyi ha'kuri kinji akan d'an wannan abun banaso ki 'kara tayar da hankalinki balle har ki furta makamancin haka, gobe in Allah ya kaimu zamu je gidanku insha Allah domin mu gaisa da iyayenki."
Da ace Amira zata iya yiwa Abba musu to tabbas akan wannan maganar yau da tayi mishi, amma bata tab'a iya jayayya dashi saboda darajarshi da kimarshi a idanunta, shiyasa ba yanda ta iya, kanta na sunkuye tace "to Abba Allah ya kaimu."
Amir yai wani dogon numfashi sannan yace "lallai mun gode Allah Abba kaci sa'a," Amira ta harari Amir, shi kuma ya kwashe mata da dariya.
Washe gari dukkansu suka shirya suka tafi gidan su Dad.
Suna isowa suka tarar da kayan su Dad birjik a 'kofar gida ana watso musu, koda su Abba suka tambaya aka shaida musu wad'anda su Nura suka siyarwa da gidan ne suka gaji da d'aga musu 'kafa yau sukazo suke musu watsi da kaya.
Cikin gidan suka 'karasa dukkanin 'yan gidan suna tsaye a falo suna kallon sarautar Allah, Dad kuwa kuka yake da idanunshi, wai yau shi ake yiwa haka a rayuwa.
Suna cikin wannan yanayin su Abba suka yi sallama suka shigo, Dad ya d'aga kai ya kalli Abba ya zaro idanu tare da fad'in "Ahmad!!!! yau kaine a gidana, ya kalli gefen Abba inda Amir ke tsaye hannunshi cikin na Abban ya sake cewa "kar dai Amir d'anka ne?"
Abba yai Murmushi, sannan yace "Amir d'ana ne na cikina, ashe kaine mahaifin Amira, ikon Allah kenan," Dad ya fad'i 'kasa dab'as kan kafet, tare da dafe kai yace "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!! na cuci kaina," yana gama fad'in haka ya cigaba da kuka cike da jin kunya me yawa da takaici, had'e da nadama.
Muje zuwa
*🅱K CE*😘💋
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
PAGE 215 to 220
Sam Dad ya kasa d'ago idanu ya kalli Abba balle Amir da 'yarshi Amira.
Amir ne ya kalli mahaifinsa yace "Abba kasan Dad ne dama?"
Abba ya kalli Amir yace "na sanshi abokina ne wanda acikin labarina da na baka na baka labari ni nai mishi jagora ya samu damar d'anewa kujerar shugaban 'kasa, saboda mutane suna sona kuma sunji dad'in mulkina shiyasa da sukaga dani a wajen tsayar da mahaifin Amira yasa shima ya samu karb'uwa sosai a wajen mutane, daga nan ni kuma na koma garinmu da zama ni da iyalina domin bana bu'katar cigaba da mulkin a lokacin."
Abba ya dakatar da wad'annan mutanen da suke yiwa su Dad watsi da kaya, yasa mutanenshi suka kwashe dukkanin kayan yace su kai sabon gidan da ya gina kwanan nan, wanda yake kusa da nashi da yake ciki a yanzu.
Bayan an gama kwashewa sun sanar dashi yai waya aje a shirya musu gidan a shirya komai yanda ya dace, su kuma yace su tashi gaba d'ayansu su tafi gidanshi idan sunje can a tattauna.
Dad tunda ya zauna a 'kasa ya kasa d'agowa, kanshi na sunkuye har yanzu, banda kuka da nadama babu abinda yake.
Abba ne ya taka yaje har inda Dad yake ya tsugunna, sannan ya kalleshi yace "abokina dan Allah ba dan ni ba ina ro'konka ka manta da komai, karka sashi a ranka, ka tashi muje, tashi," Abba ya kama mishi hannu Dad ya mi'ke suka fito daga gidan suka shisshiga motoci suka tayar suka d'auki hanyar gidan.
Kai tsaye gidan Abba suka wuce domin har yanzu basu 'karasa shiryawa su Dad kayansu ba a d'ayan gidan.
Kowa ya samu waje aka zazzauna a kujeru, aka ci aka sha amma banda Dad domin shi har yanzu kuka yake.