Sashe 38
So Mahadin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana fita Amira ta fad'a gado ta fara kuka, tana fad'in "Amir why! meyasa zakai min haka, meyasa zaka tafi ka barni, taya zan iya cigaba da rayuwa ni bayan rabinta ya tafi, sai kuma ta hau girgiza kai, tana fad'in a'a wallahi Amir bai mutu ba, ina ji a jikina Amir d'ina bazai min haka ba, nasan ba zai mutu ya barni ni d'aya cikin wannan duniyar ba," ta dad'e tana kuka babu me rarrashi, a dai-dai wannan lokacin irin halin da take ciki shima Amir yake ciki, so kenan, masoya na ha'ki'ka sukan iya tsintar kansu cikin yanayi iri d'aya, tunani iri d'aya, damuwa ma iri d'aya, ikon Allah kenan.
Bayan ta gama cin kukanta ba mai rarrashi sai ta bawa kanta ha'kuri kamar kullum ta tashi ta shirya.
Ta shirya ba dad'ewa Dad d'inta ya kirata a waya ya sanar da ita cewa ba'konta ya iso yana b'angaren d'akin ba'ki.
Cikin rashin kuzari ta yafa mayafi tare da ficewa daga d'akin ta tunkari b'angaren masaukin ba'ki.
Tana zuwa bakin 'kofa taja ta tsaya tana jiyo wayar da yake yi kuma yana 'kyal'kyalar dariyarsa.
Da farko abinda yasa ta tsaya fad'uwar gaba taji matsananci saboda zuciyarta na ayyana mata kamar in ta kula wani ta ci amanar Amir, sedai fara sauraron abinda saurayin nan ke cewa a kunnuwanta yaja ta 'kara tsayawa tsayuwa me dalili tare da 'kara matsawa tana saurare, abubuwan da taji yasa ta 'kara sarewa da lamarin duniya ta kuma razana abun ya bata mamaki kuma, koda yake ba mamaki in dai wannan zamanin da muke ciki ne.
Cikin sauri ta yaye labulen tare da kutsawa cikin falon, tace "in ka gama wayar sai ka tashi ka tafi, kuma naji duk abinda ka gama fad'i yanzu, inada damar tona maka asiri, amma sedai nasan muddin 'yan gidan nan suka ji sai sun kashe ka, saboda haka fice mana daga gida da kai da dogarawarka kuje ku kwashe motocinku ku bar gidan nan kafin raina ya b'aci in tona maka asiri kowa yaji."
Mahmud ya tashi sum-sum ya fice daga d'akin, cikin 'kan'kanin lokaci suka tattara suka bar gidan.
Nan ma Amira sai da taci kuka sosai sannan ta tashi ta koma cikin gida.
A falo ta tarar da Dad d'inta, har zata wuce ya tsaida ita yace "zo nan 'yata," Amira ta 'karasa kusa dashi ta zauna ya kalleta yace "ba'kon naki har ya tafi?" Amira ta gyad'a kai alamar eh.
Dad yace "to fad'amin ya kukai yadai yi miki ko?"
_Ayi ha'kuri da wannan banjin dad'i wallahi👏_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*MAMIEN BK SANNU BAIWAR ALLAH😰 ALLAH YA 'DORAR MIKI DA DAUWAMAMMIYAR LAFIYA TARE DA DUKKANIN MUSULMI BAKI 'DAYA👏😭😭😭😭😭*
*TAWAN INA RO'KON ALLAH YA BAKI LAFIYA, YA KAWO MIKI SAU'KI DA 'DORARRIYAR LAFIYA, YA YAYE MIKI DUKKANIN DAMUWARKI.*👏😭
*HABIBTY NAH INA RO'KON ALLAH YA BAIWA 'DAN UWANMU LAFIYA 'DORARRA*👏😭
*ALLAH SARKI MASU KU'DI ABUN TAUSAYI,😰 KAFIN SU GANE MASOYI NA GASKIYA SAI SUN SHA MATU'KAR WAHALA, SABODA YAWANCI BA DAN ALLAH AKE 'KAUNARSU BA SAI DON ABUN HANNUNSU, YA ALLAH KA SADA KOWA DA MASOYI NA GASKIYA MAI YIN 'KAUNA DOMIN ALLAH👏*
PAGE 160 to 165
Dad ya sake maimaita tambayarsa ga Amira yace "tambayarki nake Amira kinyi shiru, nace ya kukai dashi ya yi miki?"
Amira tace "Dad Mahmud ba d'an kowa bane, duk abubuwan da yazo dasu hayarsu suka yi saboda kwad'ayin abun duniya, kuma duk abinda ya fad'a maka game dashi 'karya ne, Dad bansan ya akai ba har kai saurin amincewa dashi ba tare da kayi bincike ba, Dad ashe abinda yasa ka 'ki Amir saboda shi ba d'an kowa bane kenan, da ace yana da kud'i zaka 'kaunace shi koda babu asalinshi kuma kai saurin amincewa dashi kamar yanda kayi wa wannan mutumin?"
Dad ya daka mata tsawa tare da fad'in "wato saboda bakya son auren shiyasa kika zo da wannan 'karyar domin kiy masa sharri koh, to ban yarda da wannan tsarin naki na 'karya ba, saboda haka kije sai nayi bincike na tabbatar, tashi ki bani guri mutuniyar kawai na kawo mutum kin wula'kantashi da wannan banzan halin naki da kika canza."
Amira tace "Dad wallahi tun kafin na shiga d'akin naji yana waya da wasu yana.........." Dad ya sake katseta yace "ba zaki yimin shiru ba, tashi ki bani waje," Amira ta tashi ta haye sama da sauri tana kuka, zuciyarta na zafi saboda 'kin gasgata zancenta da Dad yayi, duk da Dad be gasgata zancenta ba saida yai waya tareda bada umurnin ai mishi binciken wanene Mahmud.
Bayan Dad ya gama wayar sai bambami yake shi kad'ai, yana cikin fad'a wayarsa tai 'kara, wani babban yaron Dad ne kuma aboki na wajen aiki mai suna Haladu wanda ya aminta dashi domin Dad ya maida shi tamkar d'an uwa saboda yardar dake tsakaninsu, abokinshi ne sosai, kuma suna tattauna dukkanin matsalolin su tare, kuma suna baiwa juna shawarwarin da suka dace, bayan haka Haladu yana d'aya daga cikin wad'anda Dad ya yarda dasu kuma yana d'aya daga cikin wad'anda suka san komai na harkar dukiyar Dad, yanzu haka Haladu shine shugaba a cikin d'aya daga cikin kamfanin Dad dake kano, kuma duk wasu harkoki nashi na kano Haladun ne ke kula dasu, a ta'kaice dai sun d'auki juna kamar 'yan uwa ba wai abokai ko bare ba kawai.
Bayan Dad ya d'aga suka gaisa sai Haladu yace "dama zan fad'a maka ne gobe insha Allah muna tafe zuwa gidanka ni da yaronka ze gaisheka, amma ya naji muryarka kamar kana cikin damuwa?"
Dad yace "kai dai bari kawai, tunda mijin Amira ya rasu gaba d'aya komai nata ya shiririce, na kawo mata wani domin su daidaita kansu shima ta koreshi," Haladu yace "ka kwantar da hankalinka, harda wannan maganar ma zai kawoni wajenka gobe insha Allah karka wani damu.
Nan suka yi sallama Dad ya ajiye wayar tare da sauke ajiyar zuciya sakamakon samun 'yar natsuwa da yayi, domin yasan in har Haladu yazo insha Allah zai samar mishi da mafita.
Washe gari ita dai Amira taga ana ta hidimar shirye shirye a cikin gidan, to da yake yanzu bata shiga lamarin kowa yasa bata tambaya ba ta zuba idanu taga wad'anda ake yiwa wannan shirin.
Dad ne ya shigo a bayanshi Haladu ne da d'ansa Nura suka shigo babban falo, kowa sai sannu da zuwa ake yi musu tun daga shigowarsu har suka zauna, nikam a zuciyata nace ga dukkan alamu Haladun nan yana da matsayi a wajen 'yan gidan nan, amma kamar ya dad'e baya zuwa inda suke.
Bayan an gaggaisa aka cika musu gabansu da abinciccika kala-kala, Dad yace a kira Amira itama tazo su gaisa, aka kirata ta gaishe su sannan ta koma cikin d'akinta, tun daga lokacin da Amira ta fito har ta koma Nura kallonta kawai yake yi, ga dukkan alamu ta tafi dashi, mahaifinsa Haladu yana lura dashi, a zuciyarsa yace bazan sha wahala ba wajen cimma manufata kenan.
Dad ne ya katse masa tunanin da yake yi ta hanyar fad'in Nura an girma, yanzu babu abinda ya rage sai ka fito mana da mata musha biki, Nura ya sosa 'keya tare da yin murmushi.
Amira ce ta fito daga cikin d'aki zata fita Dad ya kalleta yace "Doughter ina zakije?" Amira ta bashi amsa a ta'kaice tace "lambu zani shan iska," ta juya tare da ficewa, Haladu yace "Nura kaima kaje can kai hira da 'yar uwarka, muma ka barmu mu zanta nida d'an uwana."
Cikin rawar jiki kuwa ya fice ya nufi inda Amira take zaune yai mata sallama ta amsa sannan ya samu waje ya zauna, yace "'kanwata kwana biyu mun dad'e rabonmu da ganin juna," Amira tai banza dashi, can ya 'kara cewa "koda yake ke nasan baki sanni ba, sedai ni na dad'e sa saninki, domin kuwa kin dad'e da zama a cikin zuciyata da mafarkina sai yau Allah ya bayyanamin ke," nan ma tai shiru bata ce mishi komai ba, ya sake cewa "mutane nawa ne a duniya suka tab'a fad'a miki cewa in kika d'aure bakya yin kyau?" se anan ne tai mishi magana tace "mutum d'aya ne tak sunansa Amir," Nura yace "Allah sarki Amir mutumin kirki ai inada labarinsa nima, gaskiya samun masoyi kamarsa sai an tona," jin anzo inda take so wato maganar masoyinta yasa ta fara d'an amsa mishi jefi-jefi, shima ya dage sai hirar Amir d'in yake mata domin ya riga da ya gano cewa da hirarsa ne kad'ai zai iya samu tai magana dashi.
Dad ya kalli Haladu yace "ya kamfani ina fatan ana samun cigaba sosai?" gaban Haladu ya fad'i, amma sai ya dake yace ana samun cigaba sosai, kwanan nan ma zaka ji alart na biliyoyin kud'i na ribar da muka samu kad'ai," bayan sun gama wannan maganar suka gangaro magana kan Amira, Dad ya fad'awa Haladu abinda ke faruwa, Haladu yace "ikon Allah ashe dai na dad'e rabona da gidan nan ranka ya dad'e shiyasa duk wad'annan abubuwan suka faru ban sani ba.
Amma ga shawara guda biyu, na farko ka d'auketa daga garin nan muddin kana so ta manta da komai kuma walwalarta ta dawo, abu na biyu shine ka had'ata aure da yarona Nura in sun daidaita junan su kaga se ayi tuwona maina kenan."
Dad yai dum yana tunanin maganar da Haladu yazo masa da ita, tabbas yaji dad'in shawarar Haladu ta farko domin shima yana da tunani da kuma 'kudurin canza musu gari ko Allah zaisa ta sanadin haka 'yarsa ta manta da komai har farin cikinta ya dawo, sedai maganar had'a d'ansa aure da Amira gaskiya yana shakku saboda baya 'kaunar wani nashi ya auri talaka balle kuma ace 'yarsa ta cikinsa, amma saboda zuciyarshi na bashi wata 'kila ba mutuwa Amir yayi ba tunda har yanzu ba wanda yace musu yaga gawarsa, shi kuma da Amir ya dawo ya cigaba da zaman aure da Amira gwara ya aurawa Nuran ita, da wannan shawarar da zuciyarsa ta bashi ya yanke hukunci, ya kalli Haladu yace "gaskiya naji dad'in shawararka, Allah ya tabbatar mana da alkhairi, Allah yasa su fahimci junansu."
Bayan ta gama cin kukanta ba mai rarrashi sai ta bawa kanta ha'kuri kamar kullum ta tashi ta shirya.
Ta shirya ba dad'ewa Dad d'inta ya kirata a waya ya sanar da ita cewa ba'konta ya iso yana b'angaren d'akin ba'ki.
Cikin rashin kuzari ta yafa mayafi tare da ficewa daga d'akin ta tunkari b'angaren masaukin ba'ki.
Tana zuwa bakin 'kofa taja ta tsaya tana jiyo wayar da yake yi kuma yana 'kyal'kyalar dariyarsa.
Da farko abinda yasa ta tsaya fad'uwar gaba taji matsananci saboda zuciyarta na ayyana mata kamar in ta kula wani ta ci amanar Amir, sedai fara sauraron abinda saurayin nan ke cewa a kunnuwanta yaja ta 'kara tsayawa tsayuwa me dalili tare da 'kara matsawa tana saurare, abubuwan da taji yasa ta 'kara sarewa da lamarin duniya ta kuma razana abun ya bata mamaki kuma, koda yake ba mamaki in dai wannan zamanin da muke ciki ne.
Cikin sauri ta yaye labulen tare da kutsawa cikin falon, tace "in ka gama wayar sai ka tashi ka tafi, kuma naji duk abinda ka gama fad'i yanzu, inada damar tona maka asiri, amma sedai nasan muddin 'yan gidan nan suka ji sai sun kashe ka, saboda haka fice mana daga gida da kai da dogarawarka kuje ku kwashe motocinku ku bar gidan nan kafin raina ya b'aci in tona maka asiri kowa yaji."
Mahmud ya tashi sum-sum ya fice daga d'akin, cikin 'kan'kanin lokaci suka tattara suka bar gidan.
Nan ma Amira sai da taci kuka sosai sannan ta tashi ta koma cikin gida.
A falo ta tarar da Dad d'inta, har zata wuce ya tsaida ita yace "zo nan 'yata," Amira ta 'karasa kusa dashi ta zauna ya kalleta yace "ba'kon naki har ya tafi?" Amira ta gyad'a kai alamar eh.
Dad yace "to fad'amin ya kukai yadai yi miki ko?"
_Ayi ha'kuri da wannan banjin dad'i wallahi👏_
Muje zuwa
*🅱K CE😘💋*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (🅱K)*
```(Autar marubuta)```
SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```
*🇸🇦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```🤜🤛
*MAMIEN BK SANNU BAIWAR ALLAH😰 ALLAH YA 'DORAR MIKI DA DAUWAMAMMIYAR LAFIYA TARE DA DUKKANIN MUSULMI BAKI 'DAYA👏😭😭😭😭😭*
*TAWAN INA RO'KON ALLAH YA BAKI LAFIYA, YA KAWO MIKI SAU'KI DA 'DORARRIYAR LAFIYA, YA YAYE MIKI DUKKANIN DAMUWARKI.*👏😭
*HABIBTY NAH INA RO'KON ALLAH YA BAIWA 'DAN UWANMU LAFIYA 'DORARRA*👏😭
*ALLAH SARKI MASU KU'DI ABUN TAUSAYI,😰 KAFIN SU GANE MASOYI NA GASKIYA SAI SUN SHA MATU'KAR WAHALA, SABODA YAWANCI BA DAN ALLAH AKE 'KAUNARSU BA SAI DON ABUN HANNUNSU, YA ALLAH KA SADA KOWA DA MASOYI NA GASKIYA MAI YIN 'KAUNA DOMIN ALLAH👏*
PAGE 160 to 165
Dad ya sake maimaita tambayarsa ga Amira yace "tambayarki nake Amira kinyi shiru, nace ya kukai dashi ya yi miki?"
Amira tace "Dad Mahmud ba d'an kowa bane, duk abubuwan da yazo dasu hayarsu suka yi saboda kwad'ayin abun duniya, kuma duk abinda ya fad'a maka game dashi 'karya ne, Dad bansan ya akai ba har kai saurin amincewa dashi ba tare da kayi bincike ba, Dad ashe abinda yasa ka 'ki Amir saboda shi ba d'an kowa bane kenan, da ace yana da kud'i zaka 'kaunace shi koda babu asalinshi kuma kai saurin amincewa dashi kamar yanda kayi wa wannan mutumin?"
Dad ya daka mata tsawa tare da fad'in "wato saboda bakya son auren shiyasa kika zo da wannan 'karyar domin kiy masa sharri koh, to ban yarda da wannan tsarin naki na 'karya ba, saboda haka kije sai nayi bincike na tabbatar, tashi ki bani guri mutuniyar kawai na kawo mutum kin wula'kantashi da wannan banzan halin naki da kika canza."
Amira tace "Dad wallahi tun kafin na shiga d'akin naji yana waya da wasu yana.........." Dad ya sake katseta yace "ba zaki yimin shiru ba, tashi ki bani waje," Amira ta tashi ta haye sama da sauri tana kuka, zuciyarta na zafi saboda 'kin gasgata zancenta da Dad yayi, duk da Dad be gasgata zancenta ba saida yai waya tareda bada umurnin ai mishi binciken wanene Mahmud.
Bayan Dad ya gama wayar sai bambami yake shi kad'ai, yana cikin fad'a wayarsa tai 'kara, wani babban yaron Dad ne kuma aboki na wajen aiki mai suna Haladu wanda ya aminta dashi domin Dad ya maida shi tamkar d'an uwa saboda yardar dake tsakaninsu, abokinshi ne sosai, kuma suna tattauna dukkanin matsalolin su tare, kuma suna baiwa juna shawarwarin da suka dace, bayan haka Haladu yana d'aya daga cikin wad'anda Dad ya yarda dasu kuma yana d'aya daga cikin wad'anda suka san komai na harkar dukiyar Dad, yanzu haka Haladu shine shugaba a cikin d'aya daga cikin kamfanin Dad dake kano, kuma duk wasu harkoki nashi na kano Haladun ne ke kula dasu, a ta'kaice dai sun d'auki juna kamar 'yan uwa ba wai abokai ko bare ba kawai.
Bayan Dad ya d'aga suka gaisa sai Haladu yace "dama zan fad'a maka ne gobe insha Allah muna tafe zuwa gidanka ni da yaronka ze gaisheka, amma ya naji muryarka kamar kana cikin damuwa?"
Dad yace "kai dai bari kawai, tunda mijin Amira ya rasu gaba d'aya komai nata ya shiririce, na kawo mata wani domin su daidaita kansu shima ta koreshi," Haladu yace "ka kwantar da hankalinka, harda wannan maganar ma zai kawoni wajenka gobe insha Allah karka wani damu.
Nan suka yi sallama Dad ya ajiye wayar tare da sauke ajiyar zuciya sakamakon samun 'yar natsuwa da yayi, domin yasan in har Haladu yazo insha Allah zai samar mishi da mafita.
Washe gari ita dai Amira taga ana ta hidimar shirye shirye a cikin gidan, to da yake yanzu bata shiga lamarin kowa yasa bata tambaya ba ta zuba idanu taga wad'anda ake yiwa wannan shirin.
Dad ne ya shigo a bayanshi Haladu ne da d'ansa Nura suka shigo babban falo, kowa sai sannu da zuwa ake yi musu tun daga shigowarsu har suka zauna, nikam a zuciyata nace ga dukkan alamu Haladun nan yana da matsayi a wajen 'yan gidan nan, amma kamar ya dad'e baya zuwa inda suke.
Bayan an gaggaisa aka cika musu gabansu da abinciccika kala-kala, Dad yace a kira Amira itama tazo su gaisa, aka kirata ta gaishe su sannan ta koma cikin d'akinta, tun daga lokacin da Amira ta fito har ta koma Nura kallonta kawai yake yi, ga dukkan alamu ta tafi dashi, mahaifinsa Haladu yana lura dashi, a zuciyarsa yace bazan sha wahala ba wajen cimma manufata kenan.
Dad ne ya katse masa tunanin da yake yi ta hanyar fad'in Nura an girma, yanzu babu abinda ya rage sai ka fito mana da mata musha biki, Nura ya sosa 'keya tare da yin murmushi.
Amira ce ta fito daga cikin d'aki zata fita Dad ya kalleta yace "Doughter ina zakije?" Amira ta bashi amsa a ta'kaice tace "lambu zani shan iska," ta juya tare da ficewa, Haladu yace "Nura kaima kaje can kai hira da 'yar uwarka, muma ka barmu mu zanta nida d'an uwana."
Cikin rawar jiki kuwa ya fice ya nufi inda Amira take zaune yai mata sallama ta amsa sannan ya samu waje ya zauna, yace "'kanwata kwana biyu mun dad'e rabonmu da ganin juna," Amira tai banza dashi, can ya 'kara cewa "koda yake ke nasan baki sanni ba, sedai ni na dad'e sa saninki, domin kuwa kin dad'e da zama a cikin zuciyata da mafarkina sai yau Allah ya bayyanamin ke," nan ma tai shiru bata ce mishi komai ba, ya sake cewa "mutane nawa ne a duniya suka tab'a fad'a miki cewa in kika d'aure bakya yin kyau?" se anan ne tai mishi magana tace "mutum d'aya ne tak sunansa Amir," Nura yace "Allah sarki Amir mutumin kirki ai inada labarinsa nima, gaskiya samun masoyi kamarsa sai an tona," jin anzo inda take so wato maganar masoyinta yasa ta fara d'an amsa mishi jefi-jefi, shima ya dage sai hirar Amir d'in yake mata domin ya riga da ya gano cewa da hirarsa ne kad'ai zai iya samu tai magana dashi.
Dad ya kalli Haladu yace "ya kamfani ina fatan ana samun cigaba sosai?" gaban Haladu ya fad'i, amma sai ya dake yace ana samun cigaba sosai, kwanan nan ma zaka ji alart na biliyoyin kud'i na ribar da muka samu kad'ai," bayan sun gama wannan maganar suka gangaro magana kan Amira, Dad ya fad'awa Haladu abinda ke faruwa, Haladu yace "ikon Allah ashe dai na dad'e rabona da gidan nan ranka ya dad'e shiyasa duk wad'annan abubuwan suka faru ban sani ba.
Amma ga shawara guda biyu, na farko ka d'auketa daga garin nan muddin kana so ta manta da komai kuma walwalarta ta dawo, abu na biyu shine ka had'ata aure da yarona Nura in sun daidaita junan su kaga se ayi tuwona maina kenan."
Dad yai dum yana tunanin maganar da Haladu yazo masa da ita, tabbas yaji dad'in shawarar Haladu ta farko domin shima yana da tunani da kuma 'kudurin canza musu gari ko Allah zaisa ta sanadin haka 'yarsa ta manta da komai har farin cikinta ya dawo, sedai maganar had'a d'ansa aure da Amira gaskiya yana shakku saboda baya 'kaunar wani nashi ya auri talaka balle kuma ace 'yarsa ta cikinsa, amma saboda zuciyarshi na bashi wata 'kila ba mutuwa Amir yayi ba tunda har yanzu ba wanda yace musu yaga gawarsa, shi kuma da Amir ya dawo ya cigaba da zaman aure da Amira gwara ya aurawa Nuran ita, da wannan shawarar da zuciyarsa ta bashi ya yanke hukunci, ya kalli Haladu yace "gaskiya naji dad'in shawararka, Allah ya tabbatar mana da alkhairi, Allah yasa su fahimci junansu."