Sashe 29
So Da Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 1 min read
a nutse Dakyar captain ya amince da shawarar Alhaji Dangoje. Don idan akwai gaban matsuwa ma yayi. So yake kawai ya mallaki Dadaa amatsayin matar sa. Shirye shiryen tarewar Dadaa su Haj Amina suka shigaa Yi. Takanas aka dakko mata mai gyaran jiki tashiga gyare ta fatarta tayi santsi da laushi. Hasken fatar ta ya Kara bayyana. Kyawunta na asali ya Kara tsatsowa. Lamarin Sai Wanda yagani kawai. Hakama bangaren na captain. Yadda yake shirya komai Kai kace auren fari zai yi. Gaba daya ya kasa rufe bakin sa saboda murna Don dadi sashen da Dadaan zata zauna sau biyu ana fente shi. An sake kawata shi gwanin sha'awa..